[4/18, 12:58 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah๐ธ๐ฉ๐ป
A true life *love* story.
By *Aaashmad*
Page 1....
Ban kade kofar da'akayi da karfi ne yasa su saurin juyawa don ganin ko waye hka, *Afeefah* ce ta shigo tana zum6ure zun6ure hawaye cike idonta ba tare da ta bi ta Kansu ba ta nufi hanyar daki da sauri, A fusaace ya daka mata mugun tsawa yace "ke xo nan" a sanyaye ta dawo hawayen da ke cike idonta ya shiga gangarowa fuskarta, *Adnaan* dake xaune gefen babban yayan nasu yyi tsaki yace "kedai gabaki daya rayuwarki ba ki da aikin yi sa na kuka koh? A hka nake ga xa ki qare koda yake ma banga laifin ki ba samun waje kika yi wllh, wawiya kawae" muryar *Ma'mee* su ka ji a falon ashe har ta shigo basu sa ni ba, a fusace take cewa " ke wllh idan baki dinga kama kanki a gidan nn ba sae kin dinga shan mamaki na, hka kawae xa ki sa mutane gaba da kuka a gida, ke yarinya ce ko uwarki ce ta mutu ko uban ki?" Adnaan yace "tambayeta dae Ma'mi, shegantaka kawae don ta ga ba a dukanta, ni da ma xa ki ban izini in saita mata xama a gidan nn" Aliyu kam shiru yyi don kwata kwata bayaso yaji ana wa yar kanwartasa fada shima bada son ranshi yai mata ba, bai ankara ba yaga ma'mee ta daga hannu xata kaiwa Afeefah da ke tsaye gun tana kuka har da shessheka duka, aikam yai xumbur ya miqe yana fadin "ma'mee don Allah kiyi haquri karki daketa kibarni da ita kawai," Adnaan da ransa bae masa ddi ba yace "haba yaya aida ka bari ta kai mata koda daya ne xata maida hankalinta," A tsawa ce Aliyu yace "shut up" ba'shiri kam ya maida sauran maganganunshi ciki yana hararan Afeefah, Aliyu na juyawa yaga babu ma'mee a gurin, janyota yayi ya shiga lallashinta dakyar ya samu ta haqura snn yace ta wuce daki, adnaan kam banda ta6e baki babu abinda yake, miqewa tai tanufi sama tana share hawayenta tashiga dakinta ta kwanta tana maida ajiyar xuciya tana tunanin abinda xata yi ma yayyin nata don rama abinda suka mata taji ddi, bude kofarta da akayi ne yasa ta dago kai don ganin ko waye *jiddah* ce tashigo tana dariya tana fadin "yar lelen yayan mu yau de mun ganku a raana muna labe mun ga duk abinda ya faru, aikam charaf afeefah ta dauka " to sai me? Bai isa yamin fadan bane? kuma ai gwara ni koda munyi fadan a ranar xamu shirya ku fa?, kuma kan ya doke ni ko ya min fada sau daya ku ya maku sau hamsin, xa ki xo kina wani gaya min maganar bnxa sae kace ba ku ku ka ma janyo min ba, kuma wllh sae na rama kmr xata yi kuka ta kare maganar, Daga mata hannu jiddah tai alamar ya isheta "ya isheni haka futsararra dama indai gurin fitsara ne ke gwanace," anyi fitsarar cewar *afeefah* ai ban gayyaceki dakina ba daxa kixo kidinga gaya man magana.A fusace jiddah ta bude qofar tabar dakin, tana fita Afeefah tabi bayanta don ta san inda xa ta, dakin Mami suka nufa gaba daya, Jiddah tace "Mami kina ganin Afeefah daga na mata mgna sae ta kama yi min rashin kunya ko" Mami ta daga kai tana kallon Afeefah, Afeefah ta fashe da kuka tace "Mami wllh su suka fara tsokana na daga mutum yyi min fada a hanya sae su kama min dariya dukansa" Jiddah tace "to Mami tafiya fa take bata kallon hanya saura kadan machine ya bugeta shine wani mutumi ya fara mata fada....." Tsawa Mami ta daka masu tace "duk ku bar min daki na" suka juya suka fita har lkcn Afeefah na hawaye.
Afeefah 'ya mace ce ta biyar ga Hajiya Zuwaira snn kaninta uku su ma duk matan, Alhaji Umar mai gidanta dan kasuwa ne da ke xaune Kano da iyalan nasa, mutum ne shi mai rufin Asiri sosae tunda ya wadata 'ya yansa da komae bbu abinda suka rasa na rayuwa, Hajiya Zuwaira da suke ce ma Mami ita ce matarsa ta biyu, bayan rasuwar Uwargidansa kuma uwar 'ya yansa Maza wato Aliyu da Adnaan, a lkcn Mami na amarya bata fi watanni biyu a gidan ba don da cikin Adnaan ta xo ta sami uwar gidan tasa, Aliyu kuwa na da shekaru biyar a lkcn, tunda ta shigo gidan bata taba samun matsala da matarsa ta farko ba Hajiya fateema har xuwa lkcn da Allah ya karbi ranta bayan ta haifi Faisal da ake ce ma Adnaan da kwana biyu, ssae mutuwar Hajiya fateema ya girgixa Alhaji Umar da amaryarsa Mami, Mami ce ta yi rainon Adnaan da madara har yyi wayo ya fara cin abinci, sae dae har lkcn ko bari bata taba yi ba, dai dai da rana daya bata taba cutan 'ya yan mijin nata ba ta rike su da amana tamkar uwarsu, bata taba barin sun yi rashin uwa ba a duniya don Mami mace ta gari ce, kowa yaba halayenta yake barin mai gidan nata, sae da tayi shekara dai dai har takwas kafin ta samu cikin 'yar ta ta fari wato Nusaiba sae sauran 'ya yan nata shidda duk mata suka biyo baya, Alhaji umar mutum ne me tsattsauran ra'ayi da ya rike policyn cewar sae 'ya yansa sun yi karatu me xurfi kafin su yi aure, don 'yar sa ta fari Nusaiba sae da ta gama karatun ta na Mass com tayi service snn ya aurar da ita ynxu hka tana xaune gidan mijinta a Katsina, hka ma 'yar sa ta biyu Safiya sae da ta kare karatun ta na Microbiology snn ya aurar da ita, ynxu su shidda mata suka rage, Sadiya, Jiddah, Rahma snn Afeefah, sae Fadila da Sumayya. Jiddah na shekara ta biyu a Jami'a ita da Sadiya suna karanta Biology, Afeefah kuma shigarta Jami'a knn tana karanta Bio Chem, Sumayya Fadila da Rahma basu kare secondary ba, Afeefah yarinya ce kyakkyawa don duk tafi 'yan gidan kyau da komae ma ka rantse kace ba gida daya suka fito ba idan suka jera da 'yan uwan nata, ga haskenta me daukan ido ga ta doguwa, komae nata daban ne daga na yan gidan nasu, Duk gidan Abbansu ya fi ji da ita, ka rantse kace ita ce auta, komae take so shi yake mata, ga son Duniya da babban yayansu ya Aliyu ya dauka ya dora mata sae dae hkn bae hanasa bata mata ba idan tayi ba dai dai ba hkn yasa take abun da ta ga dama a gidan, sae dae Mami bata daukan shagwaba da kukan da take addabar mutane da shi a gidan.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 12:58 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya *mace* Kyautar Allah'๐ธ
A true life *love* Story
By Ashmaad
2.... Washegari da safe Afeefah da sauran yayyinta suka gama shirin tafiya makaranta don duk Bayero suke, suka sauko kasa gaba daya don yi breakfast, su Sumayya dama bakwae da rabi suke barin gidan, tea kawae Afeefah ta hada, ita a dole fushi take tun kan abinda ya faru jiya, bbu Wanda ya kalli inda take, Adnaan sae watsa mata harara yake ganin bata gaishesa ba ta kuma ki gaishesan, ya gama shan tean sa ya mike don shima yyi shirin xuwa aiki ne da yake Banker ne shi, Kudi ya ciro a aljihunsa dubu biyu ya mika ma jiddah yace "ga wnn ke da sadiya ku kara a kudin break yau" Afeefah ta shiga mitstsika ido murya can kasa tace "ina kwana yaya" harara ya galla mata yace "wnn kuma da wa take" mikewa tayi da sauri tana kkrin boye dariyarta ta kamo hannunsa tace "wllh ni ma sae ka bani yaya" ya fixge hannunsa yace "da'alla" su Sadiya suka dinga dariya ta fashe da kukan karya ta rungumesa tace "ni wllh yaya kana ganinsu ko" murmushi yyi ya ciro duba daya ya mika mata ta washe hakora tace "ngdd yayana" yace "ayi karatu da kyau snn ya fice rike da briefcase dinsa don ya sallami Mami, Abba bae yrda sun sa gyale su fita ba don hka dukkansu da Hijab suke xuwa sch, Afeefah ta nufi dakin Aliyu ganin bata gansa ba tun da ta sauko ta gansa kwance yana bacci har lkcn, ta isa kusa da gadon ta dan yi kara ya bude ido da sauri tace "yayanmu xa mu tafi" harara ya galla mata yace "nace ki daina tashi na idan ina bacci" ta turo baki ta juya ta fice daga dakin, Driver na ajiyesu makaranta duk suka kama hanyar Faculty dinsu, Afeefah da ko sati biyu bata yi da fara Bayero ba taji duk makarantar ya isheta, lecture Hall dinsu ta nufa tayi mmkin ganin har an soma lecture, ta karasa gun kofar shiga lecture hall din ta tsaya kmr munafuka don bata manta me Aunty Safiya tace mata ba wae idan ka xo ka tarar lecturer ya shiga class to kadda ma ka sa ran shiga lecturen ranan don koro ka xae yi, lecturan da baxae wuce shekaru talatin da biyu ba ya daga kai yana kallon ta, ta dauke kai da sauri ya ci gaba da lecturing dinsa, har aka kai karshen lecture din Afeefah na tsaye inda take, ya bada assignment snn ya kwashi takardunsa ya fito ta basa hanya da sauri, yana kallonta yace "me yasa ba ki shiga lecture ba?" Kmr xata yi kuka tace "idan na shiga xa ka Kore ni" Murmushi yyi kawae ya wuce, ta nufi wani karkashin bishiya a sanyaye tana tunanin shknn bata samu lecturen safe ba, wata yarinya ce ta xauna gefenta tace "Baki shigo lecture ba kika tsaya bakin kofa, ae wnn lecturan baya kora da kin shigo" Afeefah tace "haba" yarinyar tace "wllh kuwa, ga handout din da ya bada sae kiyi photo copy, ya sunan ki" Afeefah tace "sunana Afeefah" yarinyar tace "ni sunana Maryam Sadis" Afeefah tayi murmushi tace "nyc name" Maryam ta mike tace mu je kiyi photocopyn," Afeefah ta mike ta bi bayanta suka nufi shagunan da ake photocopy. Karfe uku da minti sha biyar suka fito daga lecturen su na karshe ranan, Maryam tace "mu je mu dan sha drinks kafin lkcn sllh yyi" wani cafeteria suka nufa suka karbi drinks biyu suka xauna suna sha suna hira kmr da can sun saba, Afeefah tace "to dan koya min lecture din da ku ka yi da safe mana idan kin gane" Maryam ta bude handout din tace "nima fa ba wae na gama ganewa ne ssae ba don ni course din wahala yake min, amma bari in maki bayani iya in da na gane" bayani Maryam ta shiga yi mata da farkon handout din kmr ynda lecturen yyi masu, murya suka ji daga gefensu duk suka juya suka juya gaba daya, lecturan course din suka gani xaune shima da drink a gabansa, yana kallon Maryam yace "idan lecturer yyi maku lecture ba ku gane ba, tun a ajin ya kamata kuyi tambaya ya ganar da ku" Maryam tayi murmushi cike da jin kunya bata ce komae ba, Afeefah ma ta sunkuyar da kai, mikewa yyi ya dawo spare kujerar dake kusa da su ya xauna, ya karbi handout din ya shiga masu bayani gaba daya har sae da ya tabbatar sun gane, godiya ssae suka yi masa barin Maryam, ya sakar masu murmushi yace "yhu re all welcm" yana kallon Maryam yace "ya sunanki?" Tace "sunana Maryam," ya gyada kai yace "nyc name, ke fa me tsoron shiga lecture" ya fadi hka yana kallon Afeefah, ta sunkuyar da kai da sauri cike da jin kunya tace "Afeefah" ya wara nanyany idonsa yace "Afeefah kuma, sunan gskyan ki xa ki fada min" murmushi tayi har lkcn bata dago ba tace "Zainab" yyi murmushi shi ma yace "Nyc name, next tym ki dinga xuwa sch da wuri don kadda ki dinga missin lecture daga farawan ki" ta gyada masa kai tace "nagode" mikewa yyi, yyi excusing kansa ya fita daga cafterian.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 12:58 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya *Mace* Kyautar Allah๐ธ๐ฉ๐ป
A true life *love* story
By *Ashmaad*
3.....
Kallon juna sukai snnan maryam tace "saiki ki kkri nxt class dinshi kixo dawuri sabida course din mutuminnan naada wahala, tana fadin hka ta miqe tashi muje masallaci muyi sallah mutafi gda, masallaci suka shiga sukai sallah suna idar wa ta dauki wayanta sabida tunda take sallah taji yna vibrating, missed call din Sadiya tagani saita dubi maryam tana cewa " kinga drivern mu yaxo saimun hadu gobe, har ta wece sae ta kuma dawowa" what tym Muke da lectures Cox bbu tym table a gurina" 8:30am ki kkri kixo dae da wuri don matar itama da xarar tashiga to bbu wanda xai shiga, godiya tae Mata sukai sallama, tana fita sukaci Karo da jiddah "dallah mallama kixo mutafi tuntuni muke jiranki sallah kamar kina hadawa tun daga subhi, harararta afeefah tayi tai wucewarta ta shige motar,
Basu fita daga motar ba har sae da drivern ya ijye motar a parking space snnan suka fita, afeefah ce karshen fita koda ta fito saita nemi su jiddah tarasa wanda suna fitowa da sauri sukai cikin gida, ta6e baki tae tana tafiyarta a hankali kamar wadda kwae ya fashe mawa, tana stepping qafarta cikin gidan taji an fuxgota da sauri ta juya tana fadin yaya adnaan me kuma nae? "kewae yaushe xaki wayo? Sisters dinki kowacce saida ta gaidaani kafin suka shiga gida, amma kina ganina kika dauke Kai wlh saina saisai ta maki tunani a cikin gidannan, tuni hawayen dake idonta suka soma bin kuncinta daidai lokacin Aliyu yashigo da sauri ya rungumeta "Adnaan! Adnaan!! Adnaan!!! Kaji na kiraka sau uku, wlh idan baka fita harkar afeefah ba ranka xae baaci, Akan wani dalili xaka tasata gaba tuntuni na lura kap cikin yarn gdannan kafi sa mata ido matsawar ka cigaba da takurata wlh ranka baxai kyauba" am telling u this, shikam mamakin duniya duk suka isheshi ya rasa dalilin dayasa Aliyu ke haka bbu dama yaji anamata fada, Amma idan shi yatashi mata bbu mai cewa don me
Tana shiga daki ta nufi bathroom tae wanka, kaya mara nauyi tasaka jikinta ganin yamma tayi dakin ma'mi tashiga ta gaidata "ya makarantar afeefah? Cewar ma'mi,... Hmm!! Ai ma'mi yaukam ban samu lecture din safe ba, ina xuwa na tarar da lecturer a cikin lecture hall din duk a tunanina shima mutumin bai bari a shiga idan ya shiga ashe shi baya Koro, ma'mi tace to baki samu wasu sun nuna miki ba? Nasamu handout din nai photocopy cikin ikon Allah sai muka hadu da lecturen ya koya mana har muka gane "masha Allah" gobe ma kya kara Komawa baccin asbah, don ya koya maku yau bashi xaisa nxt tym ma ya koya makuba, gara kudinga hakura da baccin asbah a'ah tou
Washe gari da wuri suka shirya don basu jira yin breakfst da yan gida ba, har ta nufi kofar Aliyu saita tuna Jan kunnen daya mata akan tashinshi bacci Sai tajuya tama su ma'mi sallama suka fita, duk da irin sammakon da tayi saida ta tararda lecturer din harta shiga, duk da tasan baxata barta ta shiga ba kuma koda tashigan ma sai ta korota hakan baisa taqi shiga ba, bin ta da kallo lecturer tayi har ta xauna snn a nutse tace "Get out" mikewa Afeefah tayi lkci daya hawaye ya cika idonta ta fice da sauri daga class din, karkashin wani bishiya ta samu ta xauna ta dinga hawaye, ta kusa minti goma a gun tana kuka ta ji murya a gefenta ta juya da sauri tana kallonsa, wani matashin saurayi ne da baxae wuce shekaru ashirin da shidda ba, da damuwa yace "me ya faru kike kuka" share hawayenta ta shiga yi da sauri ta mike ta bar wajen kmr munafuka, ta fara tafiya da sauri da sauri don ma kar ya biyota wae, sae da ta dan yi tafiya me nisa snn ta soma waige waige ko xata ga ya biyota, karo ta kusan ci da mutum ta koma baya a tsorace, a dan fusace yace "watch were yhu re goin" shiru tayi tana kallonsa shi ma kallonta ya tsaya yi, "me yasa baki shiga lecture ba?" Tambayar da yyi mata knn, ta sunkuyar da kai ta gaishesa da ladabi ganin lecturansu na jiya ne, bae amsa ba ya kuma jefo mata tambayar da yyi mata, lkci daya hawaye ya soma cika idonta tace "matar ta Kore ni" strictly yace "wat did I tell yhu yesterday?" Kmr xata yi kuka tace "wllh da wuri na xo fa" hawaye ne ya shiga sintiri a fuskarta, yace "mu je," ba musu ta shiga bin sa da alamar yana da lecture da wani class ne, wani lecture hall ya shiga duk 300 level student din dake ciki suka yi tsit, front seat ya nuna mata ta xauna kmr munafuka, class rep din ajin ya mika masa Marker ya soma lecture, ssae take ganewa, awa daya da qtr yyi yana lecture daga bisanni ya ba class rep handout suyi photocopy, yana kallon Afeefah dake bin manyan matan ajin da kallo, ko kadan bata lura ita yake jira ba har sae da yace "Zainab!" Firgit ta mike ya juya ya fita ta bi bayansa da sauri, duk yan ajin suka bi ta da kallo barin matan.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:01 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'ya *Mace* kyautar Allah๐ธ๐ฉ๐ป
A true life *love* story
By Ashmaad
4.....
"Why are yhu late yau ma? ina ne gidan ku?" Tambayoyin da ya jefo mata knn suna cikin tafiya, A hnkli tace "jan bulo" ya juya yana kallonta yace "nan nn jan bulo shine baki xuwa da wuri" shiru tayi bata ce komae ba, ya ci gaba da tafiya yace "me kuke da next ynxu?" Ta ce "ni bani da timetable" ya juya ya kalleta yace "to tafi class ki duba" ta gyada masa kai snn ta nufi lecture Hall dinsu, bakin hall din suka hadu da Maryam, da damuwa Maryam tace "yau ma baki xo da wuri ba" Afeefah kmr xata yi kuka tace "kuma fa wllh da wuri na tashi" Maryam tace "to ki dae dinga daurewa seven xuwa seven thirty ki shigo sch, kinsan wasu lectures basu da mutunci" Afeefah tace "to" Maryam tace "muje kiyi photo copyn handout" bin ta Afeefah tayi suka nufi wani shigo suka gama photo copyn, Maryam ta shiga gwada mata abinda aka koya masu, sha daya saura minti goma Maryam tace "kin ga tashi mu je cafeteria yunwa nake ji, kinsan bana breakfast kafin in fito" Cafeteria suka nufa Maryam tayi masu orderin jollof rice da nama plate biyu sae soft drink, Afeefah tace "ynxu cikin mutanen nn xa mu ci abinci, ni dae kunya nake ji" Maryam tayi dariya tace "lallai, hala baki yi boarding bne" Afeefah tace "kallon mu fa xa ayi" Maryam tace "kin ji ki wa xae kalle ki, kowa na ta cikinsa" Da kyar Afeefah ta ta ci abincin tana duka kai wae ita kunya, Maryam sae dariya take tace "Xa ki daina ne yarinya"
Sae da suka yi sllhn Azahar snn suka shiga next lecture dinsu, ssae ta maida hnkli a lecture din har suka gama wajajen uku da rabi, Maryam tace su jira ayi la'asar snn su tafi, a masallaci suka hadu da su Sadiya da Jiddah, Afeefah tayi introducin yayyin nata wa kawarta Maryam, suka gaisa. Karfe hudu da minti goma drivern gidansu ya xo, Afeefah ta tilasta Maryam su je a rage mata hanya tunda hanyar daya ne, da kyar ta yrda shi ma sae da su jiddah suka sa baki, sun kusa inda motarsu ke Parke driver na jiransu ta hango lecturan su, da alama shi ma gida xae wuce, rasa sunan da xata kirasa da shi tayi don bae ganta ba, can tace "Sir" juyawa yyi suna hada ido ta sakar masa murmushi hade da daga masa hannu tace "sae gobe" murmushi yyi shi ma ya gyada mata kai, snn ya karasa gun motarsa ya shiga, su ma suka shiga ta su motar suka bar makarantar, a hanya Maryam tace gun nn xata sauka, drivern yyi parkin ta fita snn tayi ma yayyin Afeefah sallama, Afeefah ta daga mata hannu snn drivern ya ja motar suka nufi gida.
Da daddare suna xaune falo suna kallo da Mami, Abba ya shigo gidan, duk suka yi masa sannu da xuwa, hnklinsa duk na kan Afeefah da ta hade rae, ya karaso falon yace "ya aka yi dota, me aka maki" cikin shagwaba tace "ba kai ne ba baka tambayeni ya karatu ba" dariya yyi yace "to ae bacci kike kafin in dawo, in xa ki tafi kuma baki shigowa sallamata" Mami ta tabe baki, Adnaan ya mike ya bar falon, su Sumayya kam dariya suka soma yi, Abba yace to tashi mu je ki gaya min ya karatun, ta mike da sauri ta bi bayansa suka nufi sama xuwa falonsa. Karfe goma saura Afeefah ta fito daga falon Abba, dakin Aliyu ta nufa, ta samesa xaune yana danna laptop, ta hade rae tace "yayanmu baka tambayeni ko am enjoying my new sch ba" ba tare da ya kalleta ba yace "OK, Afeefah are yhu enjoying ur new sch" shiru tayi tana kallonsa kmr xata yi kuka, ya dago kai yace "ko ba shknn ba" juyawa tayi xata fita yyi dariya yace "srry little sis, xo ki ban lbrin experience din ki a higher institution" dawowa tayi ta xauna ta shiga basa lbrin abubuwan da suka dinga faruwa tun daga ranan da ta fara Bayero, kwata kwata hnklinsa bae kanta kawae yana amsa mata ne, hkn yasa tace "wayyo yayana ba ji kke ba" ya dago da sauri yace "ohh ina ji mana sis" tace "tohm, a day 15 xa mu tashi ko?" Kai ya gyada mata duk da bae sani ba, nn ta shiga basa lbrin lattin da tayi da tsoron shiga aji da tayi da kuma abinda lecturan yace mata da ya fito, ssae ya mai da hnkli a nn, har ta kai karshen lbrin a day 16 wato yau knn, yyi shiru yana kallonta sae washe hakora take tana jiran jin comment dinsa, ya girgixa mata kai a nutse yana kallonta yace "ki fita hanyar lectures, bbu ruwan ki da su tsakanin ki dasu su maki lecture in sun baki assignment kiyi, ko gaisuwa na hana ki yi ma lecturer," cikin tsawa yace "is dat clear," ssae ta tsorata ta kasa amsa mashi, ya hade rai yace "ba da ke nake ba" muryata na rawa tace "to" ya ce "tashi ki fita" Mikewa tayi da sauri tuni hawaye ya cika idonta ta fita daga dakin.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:01 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ธ๐ฉ๐ป
A true life love story
By Ashmaad
5......
Washegari Karfe bakwae da rabi Afeefah da yayyinta suka gama shirin xuwa sch, suna xaune gaba daya dinnin suna breakfast, bnda Afeefah da ta sa tea a gaba taki sha sae jujjuya bread din hannunta take da yake tasan sae Karfe goma take da lecture, idon nn nata ya kumbura tsabar kukan da tasha jiya da daddare lebbenta yyi ja ssae, Adnaan dake xaune dinnin din shi ma yana breakfast sae saton kallonta yake yana danne dariyarsa, hka ma su jiddah, bbu wanda dae ya tambayeta abinda ya sameta, Mami ce ta fito daga kitchen ta karaso dinnin din ta ajiye masu plate dauke da soyayyen kwai, har xata juya sae ta ga idon Afeefah, da mmki tace "me ya same ki?" Afeefah ta sunkuyar da kanta a hnkli tace "ba komae" sae kuma ta fara hawaye, juyawa Mami tayi ta bar dinnin din don kadda ma xuciya ya kwasheta ta kai mata hannu, ssae halin Afeefah ke bata mata rai, mutum bashi da aiki sae na kukan bnxa, abu kadan kuka, ko kanninta basa abinda take, watsewa duk suka yi suka bar ta a dinnin din, suka sallami Mami snn suka fita xuwa parkin space inda driver ke jiransu, duk da tasan ita ake jira kin tashi tayi daga dinnin din, har driver ya soma horn, amma ko motsi bata yi ba, saukowa falo Mami tayi da wayar chargerta a hannu, Haba Afeefah na ganin hka ta mike ta fice falon da gudu, Momy ta kulle kofar falonta, Su Jiddah suka dinga dariya hka ma Adnaan dake cikin motarsa, Afeefah ta fashe da kuka har da shessheka ta ki shiga motar, jin an bude kofar falon ne yasa ta nufi motar da gudu, Aliyu ne ya fito rike da jakarta ya karasa ya mika mata, cikin kuka tace "yayanmu ka ga su Aunty sadiya dariya suke min koh" ya galla mata harara yace "sun maki din," fixgo hannunta yyi ya nufi motarsa da ita, Su jiddah na ganin hka suka ce "da'alla mu je bala kar muyi latti" sae da suka fita da minti shidda snn Aliyu ya bi bayansu, har lkcn Afeefah hawaye take, har faculty dinsu ya kai ta, ta bude motar xata fita yace "don na gaya maki gskya jiya shine kika kwana kina kuka jiya koh?" Juyawa tayi tana kallonsa ta gyada masa Kai tana hawaye, yyi murmushi ya kamo hannunta yace "to yi hkuri Kanwata, but on a serious note bbu ruwan ki da lecturers kin ji?" Ta gyada masa kai yace "gud gal, ko magana suka maki kar ki tanka su kuma kada ki masu rashin kunya" nan ma ta gyada masa kai, yace "snn bnda kula samari kin dae san halin Abba koh?" Nan ma kai ta gyada masa, ya sakar mata murmushi ita ma tayi murmushin, dubu daya ya ciro ya mika mata, cike da shagwaba tace "yayanmu xa ka xo dauka ta?" Ya girgixa mata Kai yace "xan je Zaria anjima" tace "to bye bye yayanmu, Allah kiyaye hanya," yace "Ameen kanwarmu" dariya tayi ta bude motar ta fice. Lecture hall dinsu ta nufa a xuciyarta tace Allah sa Maryam ta xo, few student ne a hall din sun hada group da alamar karatu suke, don sae lkcn ma takwas da rabi yyi, fitowa tayi ta nufi karkashin bishiyar da ta ke xama, wasu maxa biyu ta gani xaune, hkan yasa ta canxa hanya da sauri ba tare da ta bari sun lura da ita ba, tafiyarta kawae take ba don tasan inda xa ta ba, ido hudu suka yi da lecturan yana tahowa ta inda take, still tayi gabanta yyi mugun faduwa nn da nn warning din ya Aliyu ya fado mata, juya masa baya tayi da sauri, tana jin ya wuceta ta kuma juyowa da sauri ta nufi hanyar da xae sadata da lecture Hall dinsu, "Zainab!" Kasa ci gaba da tafiya tayi jin ya kirata, ta juyo a hnkli tana kallonsa lkci daya ta sunkuyar da kai, da kyar ta iya bude baki tace "ina kwana", "yhu are late again ko?" Girgixa masa kai tayi tace "No" ya juya ya ci gaba da tafiyarsa, ita ma ta nufi lecture hall ta shiga ta xauna.
Goma saura minti goma Maryam ta shigo, Afeefah ta sakar mata murmushi tace "yau na riga ki" Maryam tayi dariya tace "lallai kam, amma yau da alama Karfe hudun asuba kika ta shi" Afeefah tayi dariya tace "A'a ni Karfe shidda na tashi" Maryam ta fito da text book da long note dinta tace "kin yi assignment din jiya kuwa" Afeefah ta wara ido tace "ina ce next class dinta xa ayi submittin," Maryam tace "tabdi, yau fa tace class rep ya kai mata, ki fito da littafin ki muyi kawae" suna cikin yi lecturer ya shigo, hkn yasa suka ajiye kowa ya nutsu.
Sha biyu da rabi suka fito daga lecture'n, Maryam tace "mu je under tree din can mu karasa assignment" ana kiran sllh suka gama assignment din hkan yasa suka nufi masallaci, suna idar da sllh Maryam tace su je cafteria yunwa take ji, Afeefah tace "ni dae ruwa kawae xan siya ba yunwa nake ji ba," drink kawae Afeefah ta karba Maryam ta siya jollof dinta da nama, Karfe uku da rabi suka kare lecture ranan, Maryam ta ce "mu je mosque lkci ya kusa," Afeefah xa tayi magana ta hango lecturansu, suna hada ido ta dauke kai tace "mu je," ganin wani hanya daban ta dauka yasa Maryam tace "ina kuma xa ki" sae a snn Maryam taga lecturan don har ya kusa inda suke, Afeefah kam tuni tayi gaba, kasa wucewa Maryam tayi har sae da ya karaso, ta gaishesa, yyi murmushi yace "thnk yhu" snn ya wuce. A masallaci suka hadu da Afeefah, tace "me yasa kika canxa hanya Afeefah?" Afeefah tace "ba komae."
Washegari Thursday Afeefah da wuri ta isa sch da yayyinta sanin tana da lecture da safe, tana xaune a lecture hall ita kadae don Maryam bata xo va har lkcn, takwas da minti arba'in Lecturer ta shigo, Afeefah bata ji ddi ba don har lkcn kawarta bata xo ba, har aka gama lecture'n bata ga alamar Maryam ba, gashi ita ba xuwa take da waya ba kuma ko da ma ta xo da shi basu yi exchangin nmbr ba bare ta kirata, duk sae taji wani iri, ganin sae bayan sllh suke da lecture kuma yasa ta nufi department din yayyinta, ae ko ta samu basa lecture ta xauna suka dan yi hira da kawayensu suna ta yaba kyanta, abinci suka je ci gaba daya wata kawar jiddah ta biya ma Afeefah, sae da aka yi sllh snn Afeefah ta nufi department ta xauna ita daya a kujerar gaba a hall din, har biyu saura lecturer bae shigo ba sae surutu ake tayi a hall din, wata yarinya ce ta dawo gefen Afeefah ta xauna tace "Yau kawar ki bata xo ba ne?" Afeefah ta juya tana kallonta ta gyada mata kai kawae don ita bata ma taba lura da yarinyar ba, yarinyar tace "Ayya, amma kinyi submittin assignment din ki kuwa" Afeefah tace "wani assignment din," yarinyar tace "ni ya ma course din, Wanda dae muka yi ran Monday, kinsan ni ran mondayn na fara xuwa, Afeefah ta girgixa kai tace "ni ban san ko wannene ba" bude jakarta tayi ta fito da duk assignment din da suka yi da Maryam, yarinyar ta shiga duddubawa, can tace "yauwa wnn ne, ki samu class rep ki rokesa yyi maki submittin don tun daxu aka yi submittin din" Afeefah tace "yana ina" Yarinyar ta nuna mata shi, Afeefah ta mike ta je ta samesa, kmr munafuka tace "wae inji wancan yarinyar in baka kayi min submittin" kallon takardar yyi yace "kai, tun daxu yace ayi submittin ko na je ba kallona xae yi ba wllh," Afeefah ta juya xata koma ta xauna yace "sae dae ki kai masa office ki rokesa don yana recordin assignment, wa enda na kai daga baya da kyar ya karba wllh," Afeefah tayi shiru, a hnkli tace "kora na xae yi kila" class rep din yyi dariya yace "to ae rokonsa xa kiyi," nn yyi mata kwatancan office dinsa yace "xa ki ga, Dr Aliyu Mahmud a jikin kofar, shine office dinsa," tace "to nagode," ganin waya yarinyar take yasa ta fita daga hall din ta nufi kwatancan da class rep din yyi mata, bata sha wahalan gane office din ba, ta dde tsaye bakin kofar office din gabanta na faduwa kar yyi mata masifa ya koreta," da kyar ta kwankwasa office din, taji shiru, sae da ta kwankwasa kusan sau uku snn taji ance "come in" ta tura kofar a hnkli ta shiga, sanyin A.c hade da kamshi mai ddi ya bugi hancinta, rufe kofar tayi a hnkli gabanta na faduwa snn ta juya tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "plss I came to..." Kasa karasawa tayi ta tsaya kallonsa, can ta sunkuyar da kanta tana wasa da fingers dinta, "ya aka yi?" Tambayar da ya jefo mata knn yana kallonta, ta dago tana kallonsa kmr xata yi kuka.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:01 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ธ๐ฉ๐ป
A true life love story
By Ashmaad
6......
Sir, I came 2 submit my assignment nn da nn idanunta ska cka da hawaye, ganin hka ysa ya tmbyta "wani abn aka mki daxaki kka? Kai ta gyada masa, snn yakuma tmbyrt" ina kkaje da hr class rep dnku yai submitting na sauran? Sir, aikam nn da nn hawayen dke idonta suka soma xubowa, ganin hka sae jikinsa yae snyi yace"tou ynxu ina assignment din" tana rawar jiki ta mika masa, bayan ya ansa ya duba sae ya kalleta dauke da murmushi itakam har lkcn ajiyan xuciya tke, ganinta a tsorace dayai yasa yace "tou shknn u can go" mi'kewa tae kamar munafuka bakinta na motsi"sir, " kallonta yae donjin mixata kuma ce masa, sae tace" "dama maryam ma batae submitting nata ba shine nake ro'kon alfarma idan taxo xata iya kawowa? Sae da ya qare mata kallo snn yace "ohh! don kinga na tausaya maki na karbi naki shn kke man xancn na wata? hawayene sukaita bin kuncinta da kyar ta samu ta sai saita kkan snn tace" ba haka bane sir, bata da lfy ne shn tace xatae kkari taxo sbd assignment din " yace" it's okay idan taxo sai ku kawo min" gdy tae ta fice dg office dn
Tana fita taci Karo da maryam da sauri maryam ta karaso tana fdn "nshg uku nasan ko nakai masa baxai kalleni ba", afeefah tace " gsky baxai ansaba don nima saida nae ta hadashi Allah kafin ya amsa yace bbu wnda xae kuma ansar mawa, nn da nn idanuwan maryam suka cka da kwalla sbd tasan assignment dnsa dae dae yke d test ganin maryam nashirin kka ne yace afeefah tae murmushi tace" wasa nke mki kawata nagaya mashi zaki kawo naki amma dakyar ya yrda "murmushi maryam tae ta rungumeta cke da kaunar kawar tata tana mata gdy, sae da sukaxo gab da office din afeefah ta janyo maryam baya tace" ke na manta cemae nayi bki d lfy shysa yyrda " don hka ksan ynda xki mae da fuskarki irin ta marasa lfy, cikin dan kankanin lkc maryam ta sauya fuska xwa ta marasa lfy, knock dya sukae aka amsa masu da" come in" a hnkli suka tura kofar maryam ce a gaba ita kuma afeefah na biye da ita kamar wata munafuka sae ra6e ra6e tke, sanyin A. C na mata ddi uwa bata ta6a shga guri mai A. C ba baccin ko dakinsu a kwae, sallama sukai mashi snn maryam ta gae dashi bae tambayeta komi ba ya nuna mata hannu alamun ta ajiye, idonsa nakan afeefah datae kamar xta shige fens shikam yrnyr dariya tke bashi da irin tsoron da Allah yae mata, gdy maryam ta mashi sosae snn ta juya ta janyo hannnun afeefah sukae waje tana mta gdy tace "yakamata mi exchanging numbers" sae afeefah tace saidae in bki nawa ni bn fitowa da phone, bayan afeefah tasa mta num dnta sae sukae cafteria suna tfy suka ci Karo da class rep dnsu yke tmbyrsu ko lecturan ya amsa a takaice suka bashi ansa suka wuce, 4pm suka koma lecture hall basu suka fitoba sae 6pm wnn karon kudin mota aka bata don su Sadiya tun 4 suka gama lectures, a gajiye ta shiga gida bathroom ta fada tae wanka, kaya mara nauyi ta ska jikinta, dakin Aliyu ta nufa sallama tae tyi bbu ansa sae dg bya ta tuna yace mata xae je xaria tayi mmkn rashin dawowarsa dawuri a saninta idan yae tfy da wuya ya kwana a guri, phone dinta ta dauko tae dialling num dnshi taji switched off, yaukam kasancewar gdan da ba yayanta ysa tana sallar isha'i ta kwanta, karfe 5:30am ta tashi tae sallah, tana idarwa ta koma ta kwnt don basu da lectures ranar kasancewar ran Saturday neh, misalin karfe 11 na safe Aliyu ya dwo tanajin horn tae maxa ta fito a guje tana gnnsa ta rungumesa har dakinsa ta rakashi yae wnka sae da ya shry tsaf snn suka fito dakin Abba ya shiga ya gaidashi snn yje dkn ma'mi su Sadiya ska shg mae sannu da xuwa itakam gogar tna manne da yyn nata, bashi ya fita dga dakin ma'mi ba sae da aka kira axahar, ma'mi na dga daki taji ana oyoyo Su aunty Nusaiba ne, already masu aiki sun gama abinci gabaki dayansu suna xaune a dining suna cin abinci afeefah sae Satan kallon aunty Safiya tke idon adnaan kyar akanta tana dgowa suka hada ido dashi sae ta bone fuska harararta yae gami da tsaki duk abnda suke Aliyu na kallonsu kamar ance adnaan ya dga ido sae sukae ido byu da Aliyu sunkuyar dakae yae miqewa Aliyu yae yace wa afeefah ta tashi suje, parking space suka nufa yaja mota bae tsaya ko inaba sae miss_cute bakery
Meat pie da burger ska saya sae drinks da ice cream inda yae parking suka nufa tana daga ido ta hango lecturan su tsayawa tae kamar xatamae mgn sae ta tuna tare suke da yaya Aliyu nn da nn warning din dayae mata ya fado mta bude motar tae ta shiga
Eeshatullah ๐๐
[4/18, 1:02 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ธ๐ฉ๐ป
A true life love story
By *Ashmaad*
*7*.....
Suna isa gda parking space yae da motar yana kashe motar ta bude ta fita har takusa kofa ya daka Mata tsawa "Kehh, uban wa kka barwa ledojin ya shigar maki dasu? da sauri ta dawo harda gudunta tana bashi hakuri, saeda ta tabbata da ya hakura snn ta dauki ledojin tare suka shiga koda shigarsu su aunty nusaiba sunbar falo hakan yasa sukae dakinsa cire nashi yae ya miqa mata nata yace taje yanason ya kwanta, dakinsu ta nufa don a tinaninta suna dakinne da taga basu saetae dakin ma'mi nan ta tarardasu suna hira, gurin aunty nusaiba ta nufa ta xauna sabida kap cikin yayyinta Mata tafison nusaibah ledar hannunta nusaibah ta ansa ta shiga duba wa "iyyeh yar gatan yayanta" wato ku bakucin tuwo ko? Dariya afeefah tae tace "wane mu muce bamucin tuwo" kemadae kinsan inaci saedae yaya" basu nusaibah suka bar gdanba sae karfe bakwai na dare, da misalin karfe 9pm bayan Abba ya dawo sallah yaci abinci ya kira dansa Aliyu xama yae kusa da ma'mi yana fuskantar Abban, tambynsa Abba yae "wae son har ynxu hutun naku bae qare bane? Ansa ya bashi da" ya kusa karewa Abba nanda 1week nake tunanin komawa dae dae nn afeefah ta shigo tana kallon ma'mi "ma'mi ynxu yaya Aliyu tfy xae ya barni?, ko kallonta ma'mi batae ba Abba ne ya bata ansa da" tou kodae ya hakura da aikin ne ya xauna dake? Sae tace a'ah Abba, da dae xae tafi dani ne tsawa Abba ya daka mata "fice ki bamu guri, wa ma ya kiraki ga yan' uwanki chan a daki baxaki xauna dasu ba duk inda yayanki yke kinanan, idan ya koma baki aikinsa sae muga yadda xaki yrny gaba dayanki ba burki, koda kka ga kina binsa da ae don bakida wayau ne ynxu kam da girmanki gode gode kibishi lagos, tunda Abba ya fara mata fada take hawaye sae jikin yayanta yae sanyi, yace "ki kwantar da hnklinki my little sis indae kuka samu hutu mae tsawo ni na maki alkawarin tfy dake" ya fadi mata hakane don ta kwantar da hnklnta, Abba kam bude baki yae don mamaki , juya wa tae ta wuce daki kan gado ta fada tana kuka, Sadiya ce ke tmbyrta miya sameta tae banxa da ita, sae Jiddah ta dauka "yo sis idan baxatae mgn ba ae ba dole bane sae munji abinda ke damunta sanin kankine batada aekin daya wuce kuka koda ba'ae mata komiba, mi'kewa tae tsam ta xauna tana fuskantar jiddah saeda ta gama sharar hawaye sannan tace" kinga jiddah ki kama kanki tunda na shigo dakinnan ban tankakiba Amma ke kke niman tsokanata bbu ruwanki dani na gayamaki " jiddah tace" yo ae duka na ya kamata ki tashi kiyi mara kunya kedama karya ne a xauna dake bki futsaraba" sae lokacin Sadiya tae mgn "kinga jiddah ki riqa riqe girmanki da baki tanka taba baxa tae maki raini ba, da'ma ai sa'ko da sa'ko sae haka, kamar Kuna gamin hanjin cikin junanku, tou wlh ko ku maeda hnklinku ko kuma naje na sanar da Abba in yaso ya hadaku ya hukunta hakuri afeefah ta bata, Sadiya har ga Allah tanason kanwar tata gashi dae batada kunya Amma duk yanda ka nuna bacin ranka akan abu takanyi kokari ta daena snn tabaka hakuri shiyasa take sonta, kukan datae ne yasa ta bacci ranar da wuri
Karfe 5:30am ta tashi tae sallah snn tashiga wanka 7:00am ta gama shirinta xuwa skul su Sadiya kawae take jira, suma basu bata lokaciba suka gama shirayawa, dakin yayanta ta nufa harta murda kofar dakin ta tuna warning din da yae mata akan tashinsa bacci da takeyi, ba yabo ba fallasa ta juyo ta dawo falo sallama tae wa ma'mi suka fita da'ma drivern su yakejira , suna shiga sch ya sauke su Sadiya gaban department dinsu snn ya wuce da ita nasu department din, a entrance suka hadu da lecturer din tae maxa ta shige gabansa sbd karya mata mgn sunanta taji ya kira saeta tsaya chak "baki iya gaisuwa ba ko?, sae ta sunkuyar dakae maganan Aliyu ne ke mata yawo da yace ko gaisuwa karya hadata da lecturers, dakewa tae ta gaishe sa bae ko ansa ba yae wuce warsa hall din, sunanta taji ankira ta baya ta waega maryam ce keta faman sauri tace mata "ke ya naganki tsaye anan bbu lectures ne? Afeefah tace akwae Yama shiga, bude baki maryam tae tana kallonta" ohhh yama shiga shine kkae tsaye anan sabida kinsan bae kora ko? dama muna shiga ya koroki, Murmushi kawae tae mata suka shiga hall din, suna shiga ya wurga mata wani irin kallo na ta'rae namae hankali, miqewa tae xata fita maryam ta janyota ta xaunar da ita "wae ke zainab meke damunki saeki dinga abu kamar Wata mae iskokae" afeefah bata ce mata komi ba gaba daya lectures din da yae masu ranar hankalinta bae kansa, saeda ya gama xae fita ya miqawa class rep dinsu handout suyi photocopy yae ficewarsa, kudin photocopyn suka bawa rep dinsu suka ce masa idan sun dawo class din 4:00pm xasu ansa, Mosq suka nufa suka kwanta baccine ya daukesu, basu suka tashi ba sae karfe 3 , basuje cafeteria ba kasancewar duk ranar Monday and Thursday suna axumi, al'amarin makaranta sae ka hada da axumin nafila, Ana Kiran la'asar saega su Sadiya sun shigo Mosq din danyin sallah, suma sae 6:00pm din xasu tashi
[4/18, 1:02 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ธ๐ฉ๐ป
A true life love story
By *Ashmaad*
8.....
Bayan sun gaesa da maryam Jiddah ke cewa "ynxu dae kun xama kamar yan biyu duk inda kaga daya tou ka tabbata dayar na gurin" murmushi maryam ta sakar mata, bayan sunyi sallah sun koma lecture hall din lfy kalau akae masu yanda ko wanne xae fahimta kuma alhamdulillah duk sun fahimta 6pm bae cikaba lecturer ta fita suma suka bi bayanta, ynxu dae ko da yaushe sae sun ragewa maryam hanya sumtyms kuma har gda suke kaeta, a galabaece ta shiga gda wani jiri jiri take gani sabida yunwa aekam ana Kiran sallah ta Maxa ta bude fridge ta dauko ruwan Sanyi tasha, sallah tae daman ma'mi ta hada masu komi na bude baki, a dinning suka hadu harda Abba dasu yaya Aliyu,suna cikin bude baki ne Jiddah ta kalli afeefah suka hada ido afeefah ta jefa Mata harara, dama Jiddah Jira take aekam ta dubi Abba tace " Abba ka jaawa afeefah kunne ynxu ban tankataba Amma take hararata", adnaan ma yae charaf ya ansa "wlh Abba haka take bbu wanda take raga mawa a cikin gdnn sae yaya Aliyu ka jaa Mata kunne wataqila taji maganarka" Sadiya ce ta kalli Jiddah tace "ke Jiddah kiji tsoron Allah, duk wani Abu da afeefah xatae Maki ke kkeja sabida ynxu dinma ina kece kika fara tsokanarta, Abba yace "ke afeefah da'ma inason inja maki kunne, na lura baki ganin kowa da gashi a cikin gdnn tou wlh ki kiyayeni, sannan ke Jiddah ki rinqa riqe girmanki nagaji da irin ja'iranci irin naku na gaya maku, sarkin hawayen nn da nn ta soma idon Abba akanta ya daka Mata tsawa "kehhhh! Uban wa xakiwa shaqiyanci? Tashi kibar nan ko jikinki yae tsami, don wlh idan na miqe sae kin gayamin dalikin kukan, a guje tashiga daki ta fada gado tana shashshekan kuka, Aliyu ne ya miqe ya dauki abin buda bakinta da bata ciba, xae bar gurin Abba yace "duk wani iskanci da shagwaba da takeyi ae kae ka daure Mata gindinyi" bae ce wa Abba komi ba ya wuce, bude kofar dakin yae tana ganinsa ta mi'ke ta xauna, fada ya shiga Mata sosae "keh afeefah wlh! Wlh!! Wlh!!! Kinji sau uku ko idan baki daena wannan dan iskan kukan tou wlh xan fita harkarki gaba daya, Jiddah xan janyo a jiki sae muga karshen kukan naki, ga abin bude bakinkinan idan kinga da'ma kici idan kinga da'ma ki barshi a nan bbu abnda ya shafeni na gaya maki, yana kae wnn yae ficewarsa daga dakin
Eeshatullah Goni ๐๐
๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
9......
Xama tae ta tsirawa kayan bude bakin ido mi'kewa tae ta nufa dakin yayanta a hankali take tfy saeda takae kofar dakin ta fara kwalla, sallama tae aka amsa da ta shigo, tana shiga ta xube gabansa tana hawaye "yaya don Allah kae hakuri na dae na kaaji ta kae maganar tana hawaye" kallonta yae yace "na saba jin cewa kin dae na, Don haka ba sabuwar kalma bace a guna" tashi ki tafi sosae take kuka tana basa hakuri sabida yana nuna Mata so irin wacce akeso yayyi sudinga wa yan'uwansu, shikadae yake nuna mata gata, shi kadae yake daukan duk wani ta 6ara da xatae, bata tashi a inda takeba sae da ta tabbata da ya hakura, tace tou yaya indae ka hakura kae min murmushi " Ya'qe yae mata yace ta tashi taje taci abinci ta kwanta nan tae masa sallama, dakin Abba ta wuce, sallama tae ya bata ixinin shigowa, anan ta taradda ma'mi kusa da Abba ta xauna tana hawaye" Abba don Allah mae hakuri baxan kuma ba, janyota yae yana fadin "karki damu yar lelen yayanta ae da'ma ba fushi nae ba" Amma Inaso ki chanxa halayyarki kinji" gyada masa kae tayi ta juya gun ma'mi "ma'mi nasan kema kinyi fushi dani ko? Tou don Allah kiyi hakuri ma'mi kinji", nan ma'mi ta nuna mata batae fushi da itaba godiya tae masu ta fice daga falon,tana koma dakin ta taradda su Sadiya a dakin, jikin jiddah ta fada ta rungume ta ran Sadiya yae matukar dadi ganin kannin nata sun shirya kamar ba suba kae ka rantse bbu abnda ke shiga tsakaninsu, har warewa Sadiya kae sukae duk inda xasuje tare suke xuwa, ran Abba da ma'mi yae matukar fari sabida kan yayan nasu ya hadu, Inda suke San afeefah knn Sam batason taga ran iyayen nata ya baci nan da nan xata fita hayyacinta hankalinta bae kwanciya har sae ta tabbatar da ta basu hakuri kuma sun hakura, matsalarta kenan raini da kukan da ba gaira bbu dalili ita ba karamar yarinya ba
Yaude kam sae karfe 9pm suka bar gida don dukkansu sae 10 sukeda lectures
Yau madae ta riga maryam xuwa sch koda ta shiga lecture hall din basu da yawa a ciki, tana xaune taji kamar ana kiran sunanta aekam tana daga kae taga jiddah da mamaki tace "sister lfy naganki anan, baku da class ne?? A jere tae mata tambayoyin sae jiddah tace" muna xuwa class rep dnmu yace wae lecturan yace ae masa uxuri baxae sami xuwa ba an masu rasuwa, kuma gashi sae 4pm muka ce Bala yaxo ya daukemu sae afeefah tace, tou nima bansan stand dinmu ba class rep dinma ban ganshiba bare muji xaexo ko baxae xoba, sae jiddah tace ni Bama wannan ya kawoniba "ina guy dinnan dana baki lbrnsa", gyada mata kae tayi, sae ta cigaba da cewa "chayae xaexo yau" xaro ido๐ณafeefah tae tace "xaexo ina? Badae gida ba, jiddah tace dalla dadina dake bakicin ribar xance, nan sch din yace xaexo nace masa inada class har six (6)amma yace wlh saedae idan yaxo duk abinda xan mae na mae tunda na hanashi xuwa gida, ke karshema daya gaji da jin karyaxo kashe wayar sa yae, gashi yasan duk inda xaeje ya sameni, afeefah tace "tou nidae ina jiye maki kada wataran tsau tsayi ya kawoshi gda ko kuma yaya Aliyu ya ganku tare" sae jiddah tace "kema kinsan baxan bari inxama ta farkon data karyawa Abba dokar gdannan ba ynxu baefi 1yr da few months suka rage mana a sch dinnanba kinga ko gara ka kama dahir idan na gama makarantar kinga inada miji a hannu, Amma idan nace saena gama karatu xan fara tanka maxa ashe ba aure xanba, kuma Abba bae bari fita balle ka samo wani a hanya, murmushi afeefah tae tace "tou nidae kinga jiddah bbu ruwana, abinda xan ce maki shine" u should be very careful" a gaida min dashi idan yaxo, tana kae wanna saega maryam taxo suka gaesa da jiddah, maryam tayi matukar mamaki ganin jiddah a department dinsu gurin afeefah,, itadae tasan ba shiri sukeyiba "sallama jiddah tae masu ta wace, sae maryam ta kalli afeefah sannan tace" afeefah how comes "sae afeefah tae dariya tabawa aminiyar tata labarin komi daya faru ranar, murmushi maryam tae tace Allah ya kara hada kawunanku, maryam na matukar son kawar tata, ta yaba da halinta da kuma tar biyarta, tana respecting elders dinta, amma idan ka shiga gonarta nanne xaku sami matsala, a bangaren afeefah ma hakane tana kaunar kawar tata hade da yabawa da halinta na gari, ta yarda da ita shiyasa Sam bata boye mata komi daya shafeta, itama maryam din ta yarda da afeefah 100% kamar yadda afeefah ta yarda da ita, duk abinda ya sami maryam Saeta gayawa afeefah, suna tsaye sir, kabeer yaxo wucewa ta gabansu that lecturer dinsu da suka fara sani
Eeshatullah Goni ๐๐
๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
10......
Maryam ce ta soma gaishesa cikin fara'a ya amsa, ganin afeefah batada niyyar gaishesa yasa maryam ta xungureta, a sanyaye take gaeshesa kanta a kasa, itama ansa mata yae kamar yadda ya ansawa maryam yae wucewarsa, yana tfy saega class rep dinsu maryam ce ta tambayesa "wae class rep lecturan nan baxa taxo bane?, sae yace, abinda ya kawoni knn sabida ta kirani wae baxa ta sami xuwaba kuma gashi banida number din kowa a class if not da akira tuntuni anyi informing dinku, sae lokacin afeefah tae mgn tace masa" tou ka shiga ka gaya masu sabida xaman jiranta akeyi ", saeta juyo kan maryam tace" Kawata ynxu ina muka nufa?, maryam tace wlh afeefah bansaniba inaga kawae sulaiman xan kira yaxo musha hira sabida bashida aeki Sae nason mu hadu kinga ynxu wannan itace Karo na farko da xamu xauna dashi, afeefah tace "kardae wanda kike bani labarinshine" maryam tace "dalla ba Ahmad ba" ae Ahmad har a gda an sanshi, my husband to be insha Allah", haka kam akayi kiransa tae babu bata lokaci nan da nan yaxo da'ma burinsa kenan ta bashi damar da xaexo su xauna, bayan yaxo suka gaesa da afeefah cikin mutunci, suna xaune kamar ance ta daga ido lecturan su ta hango yana tahowa, cafeteria din ya nufo saeda yaxo gabda gurin ya lura dasu, bae shiga ciki ba yace "Zainab to!" xonan, tashi tae ta nufi gurinsa Kae a kasa tana matukar jin nauyinsa, " me kkeyi anan baku shiga class ba? Wato ynxu so kuke ku fara gudun lectures ko? Tambayar daya jefeta dasu knn, Xaro ido tae tace" A'ah sir, ba haka bane "class daya mukedashi yau kuma wae baxata sami xuwaba shine mukayo nan," ohhh! Kukayo nan kuke tadi ko? Instead of ku shiga library kuyi karatu yayi maku kyau, adaebi a hankali a nutsu ae karatu, kada kuyarda wani daa namiji ha hure maku kunne, ni namijine ninasan halinmu, maxan ynxu wlh ba ko wanne ake yarda dasuba, so u should be very very careful, ta yarda da maganarsa 100% godiya tae masa ta koma ta xauna nesa dasu maryam, shikam lecturan juyawa yae ya fasa shiga gurin don baeson raini, yau da gobe idan suna yawan haduwa raeni ne xae shiga tsakaninsu shiyasa ya chanxa shawarar daena xuwa gurin, yanxu duk sanda ykeson cin abinci restaurant din outside sch din yake xuwa
Basu sukabar gurinba saeda aka kira la'asar sukae sallama da sulaiman akan idan maryam ta'idar xae ajeta a gida, Mosq suka nufa direct don yin sallah, suna idarwa maryam ta nufi inda sulaiman yae parking,, ita ma afeefah gurin da nasu drivern yae parking ta nufa bayan sunyi sallama da maryam, a ciki ta tarardasu jiddah suna shiga Bala ya tada motar suka bar sch din, suna shiga gda suka nufi gurin ma'mi, Aliyu, adnaan suka gaedasu sannan suka wuce dakinsu
Eeshatullah ๐๐
[4/18, 1:03 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
*11*.....
Daren ranar da ya Aliyu xaeyi tafiya dukkansu suna xaune a falon Abba, Aliyu, adnaan, Sadiya, jiddah, dukkansu suna xaune Amma bbu afeefah, Abba ne yace "ma'mi wae ina afeefah ne? naga duk yarannan suna xaune amma bbu afeefah", ma'mi tace "halan ka manta da gobe ne tafiyan Aliyu", tanachan tana aekin kuka "jiddah najin haka ta mi'ke ta nufi dakin kwance ta sameta tanata aekin kuka, dagota tae tana share mata hawaye" sister don Allah kiyi hakuri tafiyarsa ae ba yana nufin rabuwarku bane, karki manta mumafa yayanmu ne, kuma kamar yanda kike nuna masa kauna muma muna masa duk da dae nasan shakuwarku dashi tafi wanda mukae dashi, wae baga shi xakudinga waya ba, saekace babankine xaeyi tafiya, ni wlh harkin batamin rae haba, shigowar dataji anyine yasa ta kallon kofa, gyara xama tae ganin yaya Aliyu ne ya shigo, kallon jiddah yae yace "lallashinta kike ko kuma masifa kike Mata?, tace" yaya masifa kuma? Lallashinta nake, tana kaewa ta mi'ke ta fita daga dakin
Zama yae kusa da ita yace "kewae zainab karamar yarinyace ke? Kamata yae ki farincikin Tafiyata sabida halas dina xanje nema, don Allah ki cire komi a ranki kinajina? Gyada masa kae tayi, yace" to ki murmushi" hkan tae, yace Mata ta taso suje falo, suna shiga ta xauna kusa da Abba hira sukae tayi 9:pm ko wa yae dakinsa, saeda kowa yae daki Abba ya kira Aliyu, ba bata lokaci ya fito, kusa da kafan Abba ya xauna, Abba yace son tambayace xan maka, kallon sa yae don jin tambayar daxae masa "Aliyu banason banbancin da kake nunawa yarannan, narasa dalilin dayasa kake nuna hakan" kallonsa Aliyu yae yace "Abba bawae ina nuna banbanci bane, Abba sanin kankane tun tasowar afeefah tafi sabawa dani har girmanta, sannan tana matukar bani respect yanda yakamata, tanajin maganata, Sam bbu raini tsaka nina da ita, tana matukar shakkata, Amma kaga su jiddah sa'banin hakane, shiyasa hausawa suka ce xuciya nason abinda ke kyautata mata, Abba yace "shknn Amma dae ka rage nuna banbanci haka" ya gyada masa kae, Abba ya kuma cewa "ya kadae gama shiryawan ko? Yace" tun jiya na kammala Abba, yanxu tafiya kawae ya rage, Abba yace masha Allah, kaje ka kwanta sabida flyt din 7am xakabi, sallama yawa Abba ya wuce dakinsa
Bayan dawowarsu sallah asubah ne yae break fast, bangaren afeefah kuma cikin ikon Allah harda murmushinta ta rakoshi har inda Bala ke jiransa, su ma'mi dasu Sadiya duk sunfito mashi sallama
Suna koma cikin gda suma sukae break fast dinsu suka nufa makaranta
Tana isa hall din taga ko wane student ya duqufah akan abinda ke gabansa, gaba daya ta manta Sunada test din kabeer, maryam ta hango itama maryam din idonta na kan afeefah, maryam ji take kamar xatae kuka sabida ko afeefah ta shigo baxata rubuta abin arxikiba xae karba, jitae yana 5 minutes left, nn da nn idanuwant suka cika da kwalla, ji tae an dafata tana Juyawa taga maryam, da sauri ta kalleta tana kwalla "maryam ynxu ya xanyi? Nayi missing din test din kenan? Tambyr data wurgawa maryam kenan lokaci guda, maryam tace" kibari idan ya fita sae mubishi mu rokeshi, ynxu xae mana lecture ne, jiki bbu kwari suka shiga, ido biyu sukae dashi cikin mamaki yake kallonta Sam bae lura da bata hall dinba, cikin harshen turanci yake tambayarta "are u just coming?, gyada masa kae kawae tayi, ganin bata da niyyar bashi gamsashshiyar amsar abinda ya hanata xuwa da wuri yasa ya shareta bae kuma tambayantaba,lecture yakeyi amma tunaninta na tayanda xata soma bashi hakuri har ya amince yae mata nata, maryam data lura da ita tace "kinga karki biyu babu, ki natsu ki saurari abinda yake mana kuma ki fahimta, lecture din 2hrs gareshi yae using half hour na test sae saura 1and half hour yae masu lectures
Yana fita maryam ta riqota tace tashi muje zainab, afeefah tace, a hanya xamu masa mgn? Sae maryam tace, a'ah har office dinsa xamu bishi Muda muke niman alfarma ae baxamu soma tareshi mu rokeshi a hanyaba, sae da suka bari ya shiga da yan mintuna Sannnan sukae knocking, sun dade suna knocking kafin yae masu ixinin shigowa, maryam a xuciyarta tace, "lallae bawan Allah nan saeda ya cika ya batse yabarmu tsaye kafin ya amsa", sallama sukae masa yaudae kam babu annuri a fuskarsa sabida yanda sukaga ya amsa masu ba yanda suka saba gani bane, afeefah na ganin haka jikinta yae matukar sanyi don ta ma rasa ta inda xata soma
*Eeshatullah Goni*๐๐
Hope Kuna enjoying din Novel din, bana typing dayawa sabida 2days banjin dadi..... Luv u all๐๐๐
[4/18, 1:03 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By *Ashmaad*
12....
Duk da shakkar da takeyi amma ta dake, Sir,... Sae kuma ta kasa ce masa komae, Jin shirun yae yawa yasa yace "Zainab idan bakida abin cewa tou dan Allah ku tafi kuban guri"
Sae tae saurin fadin "sir, da'ma alfarma naxo nima" duk da yasan me bakinta ke shirin furtawa bae hana shi tmbyrtaba, "alfarmar me knn Zainab?
Sae tace," inaso ne ka taimakeni kamin nawa test din don Allah karka cemin a'ah plss sir"
Kauda kae yayi daga kallon dayake mata yace "Zainab am sorry" baxan iya makiba sabida ba ke kadai bace baki rubutaba, kuma idan na maki ke kadae na yaudari kaena, this is not the first time dana fara advising dinki da kidaina xuwa late Amma kinkiji ynxu wa gari ya wa'ya, hawaye ne keta bin kuncinta ya tausaya mata kasancewar sa mutum ne wanda yakeda tauheed Amma baeda daman mata, aikinsa yake kan gsky,so indae yae mata baewa sauranba baeyi adalciba, ynxu kinga ranar xuwa sch da wuri, jiki ba kwari suka fita daga office din
Suna fita maryam tace "afeefah anya yau lecturan nan lfyarsa lau kuwa?, afeefah da bakin ciki ya gama rufeta tace" kalau yake, maybe yau mulkinsa ta lecturorine ya tashi sae wani babbatsewa yake", maryam tace " a'ah afeefah inaganin dae an bata masa raene don wlh bawan Allah nan yanada mutunci, ki tunafa idan bakixo da wuriba saeya rambayeki dalilin rashin xuwanki da wuri, afeefah ta yamutsa fuska tace" yo ai bani kadai yake tambaya ba duk wanda yaxo late saeya mashi tambayar ", Oho dai koma miye yanadai tambaya" cewar maryam , kawai dae inaga sun sami matsala ne da matarsa
Da sauri afeefah ta juyo
Mata? Ke ynxu wannan yai maki kama da mai aure, maryam tace dalla matsa mi kika sani game dashi bare kisan yanada aure ko baida
Afeefah tace ke inafa jin yanda yammatan sch dinnan ke bibiyarsa, suna cewa gashi gaye har gaye Amma bayyida mata, Sam mata basu gabanshi a halin yanxu, don haryau baisami macen da tadaace da rayuwarsaba, afeefah tace maryam mubar gurinnan, masallaci suka nufa sunyi kusan minti talatin sannan maryam tace ke nifa ko ruwa bansha ba nafito don haka tashi xakiyi muje kirakani, cafeteria suka wuce don ya xama joint dinsu, lipton tace a dafa mata sae indomie da kwai plate daya, bae bata lokaci ba wurin kammala mata ya kawo mata, tana kurba so daya call din *Ahmad*ya shigo, da sauri ta ajiye cup din ta dauki wayar, cikin yar siririyar murya tae sallama, soyayya suke ynda kasan suna kusa da juna, bangaren afeefah kam mamakin maryam kawae takeyi ynda taga cikin dan kankanin lokaci ta sauya murya sae rangwada takeyi tana kashe murya uwa tana gabanshi, saeda ta kammala wayanta tsaf sannan ta dubi afeefah wacce har lokacin kallonta takeyi
Maryam tace "ke lfy irin wannan kallon hka, yau aka fara soyayya a gabanki
Afeefah tae murmushi tace" ai dole inkalleki irin wannan karairaya kamar kina kusa dashi, kuma batun soyayya a gabana ban taba ganin anyi ba saeyau, sanin kankine Abba bae barinmu kula samari ballantana har mukaega hira dasu
Taaap! Ki tsaya kallon ruwa kwado ya maki k'afa, sae kin gama sch ki rasa mijin aure, ba gara ka kama dahir ba ana kammala sch din sae aure, amma saekin gama sch ne xaki fara kula samari, kinada aiki babba a gabanki
Ummm! Nidae mubar wannan maganar, kici abincinki mu kara Wuta, tana kammala wa suka koma masallaci don yin sallah, karfe biyu xasu koma class
Tou haka dae suka gama da lectures din ranar
Misalin karfe 9 na dare ta kira yayanta, saeda ya katse baidaukaba sannan ya kirata back
Eeshatullah Goni ๐๐
๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ธ๐ฉ๐ป
A true life love story
By Ashmaad
13.....
Sallama tae cikin muryar shagwaba, shima cikin tattausan lafaxi ya amsa
Yaya nayi fashi dakae tunda baka nimeniba throughout,
Murmushi yae kamar yana gabanta
Haba my little sister, kina raina, bandae sami tym din kiranki bane coz aiki yamin yawa,
Tou shikenn yaya, ya aiki?
Lfy lau afeefah, hope kina kulamin da kanki
Sae ta tabe baki "hmm! Ai dole yaya na"
Yaya kasan me?, yace Mata saekin fada
Yaya lecturan nan.... Bae bari ta karasaba ya katseta da tsawa saeda ta kauda wayar daga kunnanta sabida kara
Zainab! Zainab!! Zainab!!! Kinji na kiraki sau uku, wlh idan baki fita hanyar lecturoriba sae ranki yae mugun baaci, uban me ya kuma hadaki dashi
Gabaki daya jikinta yai sanyi, yaya Aliyu sanda naje sch ne na tarar da yabada test harnae missing banyi ba shine na Bishi in bashi hakuri yamin
A fusace yace "meya hanaki binshi gida ki bashi hakurin" Mahaukaciya wlh idan baki fita harkarshiba saena hadaaki da Abba, ince masa kin fara tara samari sai muga karyar iskanci
Haba yaya wlh bbu abinda ke tsakaninmu, hasalima koda nabishi ceman yai baxaiminba tunda ba nikadai bace banyi ba
"oho dae na fadamaki wlh ki kiyaye tunda test din ba na barin duniya bane" kinajina?? A tsawace ya fadi, hawaye kawai takeyi tace "naji yaya na daina"
Yace "good girl", so gayamin mai kikaci a sch yau, tace yaya ba abinda naci sabida banji yunwa ba, ya kuma tambayrta taci abinci dare? Sae tace masa "a'ah banjin yunwa"
So kike muyi fada ko? Matukar bakiso muyi fada to kije kici in yaso na kiraki anjima, tou kawae tace masa ya katse wayar
Kitchen ta shiga ta hada tea mae kauri sannan ta koma daki, wayar jiddah ce ta soma ringing bugu biyu tae ta dauka ganin wacce ta kira, sunan aunty nusaibah ne yae appearing
Auntyna ta kaina ina yini ina gajiya??, bayan sun gaisa take tambayrta Sadiya da afeefah,tace gasu kusa dani, sai tace a sata a hands free, hakan tae kamar yadda ta umur ceta, my one and only sister cewar aunty nusaibah, afeefah najin haka tasan da ita take, haba aunty ai fushi nake dake, yaushe rabanki da kirana kiji yadda nake
Lallaima afeefah ae gabaki dayanku kallonku nake, bbu wacce tace bari taxo tamin kwana biyu ko xuwa ma ynxu kundainayi
Sadiya ce tae mgn "kema aunty kinsan baccin skul bbu abinda xai hanamu xuwa gidanku"
Jiddah tace "insha Allah muna samun hutu xaki ganmu duka kafinnan kinga su *Rahma* sun dawo hutu saimu barsu da ma'mi mu kuma muxo gurinku keda aunty safiya
Aunty nusaibah tace tou Allah ya kaimu..... Ina labarin samarinku? Gabaki dayansu suka xaro ido," samari kuma aunty? "dukkansu suka hada baki, rufamana asiri karkisa Abba yaji yae tunanin munada su
Dariya tai sosae tana fadin" Munafikai nasan is hardly kuce baku da samari saedae kuce bakuda daman tsayuwa dasu
Afeefah tace "sister wlh nidaikam bandashi Amma su ki tuntu6esu baxasu rasaba, Sadiya tace" halan ke kika mana samarin ", jiddah kam sai kifta Mata ido take
Aunty nusaibah tace" Saekunyi hakuri Abba nada matukar tsauri inba haka ba aeda tuni Kuna taad'ih, baccin adnaan wlh da kunyi abunku a boye ina dalili
Afeefah tace "kedai aunty hakanan xamu ququta mugama mubishi a yanda yakeso", tou shikenan Allah ya xaba mafi alkhairi cedar nusaibah, duk suka ansa da "Ameen" nan tae masu sallama ta katse wayar
Da misalin karfe goma na daren Kiran yaya Aliyu ya shigo, yaeta ringing ba'a daukaba don lokacin tae nisa a bacci
Eeshatullah Goni ๐๐
[4/18, 1:04 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By *Ashmaad*
14......
A hankali Afeefah ke tafiya kmr me tausayin kasa sanin bata da lecture sae 10:30, class rep dinsu ta hadu da, da yake sun dan saba ta tsaya suka gaisa snn suka nufi faculty dinsu, suna tafiya tace "Wae in tambaye ka Abdul, test din Dr Aliyu Shariff da kuka yi jiya yana recording ne?" Abdul yace "kai, ae tests dinsa ke taimaka ma mutane da yawa a exams dinsa," Afeefah ta dan tabe baki bata kuma cewa komae ba, wani haushinsa taji ya dirar mata, ido hudu suka yi da shi ya fito daga hall din da 200lvl students ke daukan lecture da alamar lecture ya gama masu, hka kawae taji faduwar gaba ta dauke kanta da sauri, Abdul ya tsaya gaishesa tayi gaba da sauri, bin ta yyi da kallo ta gefen ido snn yyi wucewarsa. Har suka fito daga lecture Maryam bata xo ba, hkan yasa ta ciro wayar ta a jaka ta kirata tunda sun yi exchanging nmbr ynxu, muryar wata ta ji, suka gaisa snn yarinyar tace mata Maryam na bacci bata da lfya, da damuwa Afeefah tace "me ya sameta?" Yarinyar tace "ciwon cikinta ne ya tashi Cikin dare," Afeefah tace "Ayya, to Allah ya sauwake xan kira xuwa anjima idan ta tashi" yarinyar tace to snn suka yi sallama, shiru Afeefah tayi da damuwa tana tausaya ma kawartata sanin cewa ba wani abu bne bnda Appendix din da ya sata gaba. Karfe sha biyu da rabi Afeefah suka fito daga lecture ta nufi masallaci, ana idar da sllh suka fito da rukayya yarinyar da ke son mata mgna don sun dan fara shiri da ita, ji tayi tana gaida mutum ta juya da sauri suka hada ido shima ya fito daga mosque, dauke kai Afeefah tayi ta kara gaba abunta, shi kam murmushi yyi ya amsa gaisuwar Rukayya ya nufi office dinsa, sae da suka isa faculty dinsu snn Rukayya tace "ba ki gaida Dr Sharif ba" Tsaki Afeefah tayi tace "bn lura da shi ba," Karfe uku saura Class rep Abdul ya shigo class da yake lecturan su bae shigo ba ranan, announcement ya bada na cewa Dr Sharif yace wa enda basu yi lst test dinsa ba su xo gobe as early as eight o clock yyi masu test din, ba karamin farin ciki students din suka yi ba, Afeefah dae sae danna wayarta take bata ce komae ba, da xolaya Abdul yace "Hajiya Zainab kin dae ji koh?" Murmushi Afeefah tayi tace "na ji" Afeefah na xaune karkashin bishiya dae dae inda drivernsu ke tsayawa idan ya xo tana jiran fitowar yayyinta daga lecture, duk yau sae taji ta gaji da jiransu da take yi kullum kawae Abba xata gaya ma ana tashi ita a dinga xuwa ana daukanta don wani lkcn sae ta fi awa biyu tana jiransu a xaune, kamr ance ta daga kai ta hango Dr Aliyu Sharif da alamar ya gama lecturing dinsa xae tafi gida, dauke kai tayi da sauri duk da sun hada ido, wnn karan ta so gaishesa amma kunya ya sa ta kasa, shi ma bae ce mata komae ba ya bude motarsa ya shiga yyi reverse ya bar wajen, bin lafiyayyen motar tasa tayi da kallo snn ta dauke kanta.
Washegari Karfe bakwae da rabi Afeefah ta farka daga bacci, a tsorace ta mike xaune ganin Karfe nawa, tana kallon yayyinta da ke ta baccinsu hnkli kwance, duka ta kai masu gaba daya, suka mike xaune suna kallonta kamr xata yi kuka tace "mun yi latti fa" tsaki Jiddah tayi tace "ba mu da lecture da safe yau Malama" da sauri Afeefah ta mike hawaye har ya cika idonta ta nufi bayi tana cewa "wayyo na shiga uku ina da test yau" wanke baki tayi tayi wanka ta fito da sauri, takwas saura kwata ta gani, tana hawayenta na gado tayi sauri ta shirya snn ta figi jakarta bayan ta sa hijab ta fice daga dakin, bbu abinda Jiddah da Sadiya suke bnda dariya, Mami da fitowarta daga kitchen knn tace "ke ina xa ki kinyi break ne?" Kuka ta fashe da tace "Kinga Mami yau ina sa test Karfe takwas shine bbu wanda ya tasheni gashi na makara ynxu" Mami ta watsa mata harara tace "Akwae wnda kika ajiye sa xae dinga tashin ki ne, da'alla wuce kiyi breakfast" Afeefah ta kuma fashewa da kuka tace "ni baxan yi ba nayi latti" Adnaan dake xaune falo yana sa safar kafa yace "Ke da'alla wuce ki ci abinci," tana hawaye tace "ni baxan ci ba Dubi fa Karfe nawa" mikewa yyi, yyi kanta da gudu ta nufi dinnin tana rusa kuka, sae a snn Mami ta haura sama, hka Adnaan ya tsare ta har sae da ta hada tea ta sha da bread, wajajen Karfe takwas da minti sha biyar ta fita daga gidan tana kuka. Ba ita isa faculty dinsu ba sae kusan takwas da rabi, tsaye tayi bakin lecture Hall din tana hawaye ganin har an fara test din ga student dayawa sun xo, kallonta kawae yake, taki dago kai, karasa wa yyi bakin kofa ya tsaya yana ci gaba da kallonta yace "Gud mrnin Ma'am Can we help yhu" juyawa tayi da sauri ta bar wajen tana ci gaba da kukanta. Ana idar da sllh Afeefah ta dawo class duk da basu da lecture da gninta ranan kasan ba karamin kuka ta ci ba, ko kadan bata damu da dariyar da yan ajin ke mata ba don ixuwa ynxu tasan kukanta ke basu dariya, wani handout take dubawa ita kaddae a xaune don yau din ma Maryam bata xo ba, Class rep ne ya shigo class din ya nufi seat din da take yace "Malama Zainab, Dr Aliyu yace ki je office dinsa," xaro ido tayi lkci daya gabanta ya fadi tace "Ni?" Yace "ehh mana" kai kawae ta iya gyada masa ya wuce, ta fi minti goma a xaune snn ta Mike kmr mara laka ta fita daga class din, office dinsa ta nufa, a hnkli ta kwankwasa masa kofa, ya amsa da "come in" tura kofar tayi shima a hnkli ta shiga office din da sallama can ciki, suna hada ido ta sunkuyar da kai da sauri tace "Ga ni Sir" jin bae ce komae ba yasa ta dago kai a hnkli tana kallonsa, kallonta taga yana yi lkci daya ya sauke idonsa kasa yace "sit" ba musu ta karaso ta xauna kan kujerar dake facing din nasa, ya ajiye pen din hannunsa yace "y were yhu late today" hawaye ne ya cika idonta muryarta na rawa tace "bbu Wanda ya tashe ni yau har sae da nayi latti, kuma Mami tace sae nayi breakfast bayan nayi latti" cikin muryan kuka ta kare maganan, jin be ce komai ba yasa ta dago kai tana hawaye tana kallonsa, murmushi ta ga yana yi, ta yi saurin sunkuyar da kanta tana share hawayen, "Are yhu now ready for d test?" Gyada masa kai tayi da sauri ba tare da ta kallesa ba, fullscap ya 6alla ya mika mata da pen ta karba, yace "am dictating d questions for yhu" ta gyada masa kai snn ya shiga dictating mata questions din, yana gamawa yace "answer 3 out of d five, am giving yhu 20 min" a hnkli tace "OK sir" wani kujera daban ya nuna mata ta koma ta xauna tana kallon questions din hannunta kmr me shirin kuka ganin ko question daya bata gane ba, dago kai tayi a hnkli don kallonsa, suka hada ido tayi saurin sunkuyar da kanta, ta fi minti goma ta kasa amsa ko daya, sae take ga kmr bae taba koya masu topics din da take gani yyi question a kai ba, mikewa taga yyi ya dauki books ya fita daga office din, hawayen dake makale idonta ya gangaro mata, bayan fitansa da minti biyar Abdul ya shigo yana ganinta yace "lah ashe baki samu test daxu da safe ba" kai kawae ta gyada masa ya ajiye abinda xae ajiye xae fita tace "don Allah Abdul mun yi topics din nn" dawowa yyi yana kallon questions din yace "kai ai shine farko ma a semestern nn, amma ni kaina na manta, komawa yyi kan table din office din yace " lah ga text book xo ki bude ki duba da sauri kafin ya shigo" xaro ido tayi a tsorace tace "Textbook?? Ni tsoro nake ji kar ya shigo" Abdul yace "tab ae kuwa xa ki fadi, can cafeteria fa naga ya nufa ba ynxu xae dawo ba" kmr xata yi kuka tace "to ae ban san page din ba" Abdul ya shiga nema mata page din da sauri, yana gani yace "xo kiyi sauri ki kwafa ga shi nn" da sauri Afeefah ta karasa kusa da table din hannunta na rawa ta soma copy din answer din, Abdul yace "kiyi sauri kafin ya shigo kuma ba dukka xa ki kwafa ba" juyawa yyi xae fita Afeefah ta xaro ido a tsorace tace "tafiya xa kayi" yace "Kinga sauri nake, ke dae kiyi maxa kafin ya shigo," yana kai wa nn ya fice daga office din, har wani xufan tsoro Afeefah ta shiga yi ga wani rawa da jikinta yake, ji tayi an bude kofar office din, suka yi ido hudu da shi, mikewa tsaye tayi a rikice ta saki pen din hannunta lkci daya ta fashe da kuka tana kallonsa, karaso wa table din yyi yana kallon textbuk din gabanta, durkushewa kasa tayi cikin kuka tana yarfe hannu tace "Don Allah don Annabi, kayi hkuri sir, ban iya bne" daukan papern test din nata yyi yana kallon abinda ta rubuta, wani mugun kallo da ya kada mata hanjin cikinta ya daka mata yace "Stand up" jikinta na rawa ta mike, yace "come here" karasawa tayi kusa da shi tana hawaye har lkcn jikinta na bari.
Kuyi hkr kamar yadda na fadi maku banjin dadi neh, yau kun samu... Godiya dubu๐๐
Eeshatullah ๐๐
[4/18, 1:05 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By *Ashmaad*
15......
Kallonta ya tsaya yi fuskarsa daure bayan ta karaso gabansa yace "Leave My office!" Kin fita Afeefah tayi tana kuka ssae ta koma baya tace "Sir wllh am nt the one dat opened the textbook, don Allah kayi...." Wani tsawan ya kuma daka mata yace "Get out," Afeefah ta bar wajen da sauri ta koma can jikin bangon office din ta dinga rusa kuka har da buga kafa a kasa tana cewa "Don Allah sir kayi hkuri wllh I'm nt d one dat open d textbook bani bace ba wllh" Ajiye textbuk din hannunsa yyi yace "fita nace" nn ma taki fita sae rusa kuka take, xagawa yyi ya xauna kan kujerarsa ya ci gaba da aikinsa, har aka kira la'asar Afeefah bata fita daga office din ba kuma bata bar kukan da take ba, Mikewa yyi ba tare da ya bi da kanta ba ya fita daga office din don xuwa masallaci, har ya dawo bayan minti kusan ashirin Afeefah na durkushe inda ya bar ta, sae a snn ta mike ta dauki jakarta ta nufi kofa a sanyaye ta fita, bin ta yyi da kallo har ta rufo masa kofar. Main Gate Afeefah ta nufa don bata jin xata iya jiran yayyinta, ta tsaida adai daita ta gaya masa inda xata. Tana isa gida ta ba sa kudinsa ta nufi cikin gidan, Zaune ta samu Mami da su Sumayya a falo, ta xube kasa ta fashe masu da kuka, Mami ta Mike a rude hka ma su sumayya duk aka shiga tambayarta me ya faru ina su Sadiya, cikin kuka tace "Suna sch" Mami tace "to me ya dawo da ke ynxu, me faru" cikin kuka tace "ni kaina ke man ciwo" tsayawa kallonta Mami tayi, can ta haureta tana huci ta wanka mata mari tace "wllh baxa ki fasa min xuciya ko ki daura min hawan jini ba Zainab, don uwar ki don kan ki na ciwo sae ki shigo ki ruda mutane??" Da gudu Afeefah ta mike tun kan ta kuma kai mata wani marin ta nufi sama tana ci gaba da rusa kuka. Har su Jiddah suka dawo bbu wnda ya bi ta kan Afeefah da ke daki har lkcn, sadiya tace "Afeefah ta dawo" Su Sumayya suka ce eh, Jidda tayi tsaki tace "Gskya Mami ki gaya ma Afeefah ta daina daga ma mutane hnkli, idan xata tafi gida ba sae ta xo ta ce mana ta wuce ba hka kawae xata ba mutane wahala ayi ta neman ta" Mami tace "duk ran da baku ganta ba kuyi tahowar ku kawae,"
Da daddare duk yan gidan na xaune falo suna kallo Adnaan dake danna laptop yace "wae ina Afeefah ne?" Rahma tace "tana daki tun daxu" Mami tace "Kai ma ka kula bata falon, ae na kusa fara dukan Afeefah a gidan nn, ko kanninta basa min iskan cin da take min," sae da Abba ya shigo shi ma ya tambayi Afeefah snn Adnaan ya mike ya nufi sama ya bude dakin da yasan xae sameta ya shiga, kwance ya ganta cikin bargo ya karaso kan gadon ya yaye bargon yana kallonta, mikewa tayi xaune tana mitsika ido, ya galla mata harara yace "me aka maki?" Kanta ta nuna masa a hnkli tace "kai na ke man ciwo" dafa goshinta yyi ya ji xafi, yace "tun yaushe?" Kmr xata yi kuka tace "tun da rana" juyawa yyi ya fita daga dakin ba a jima ba Jiddah ta shigo dakin da abinci ta ajiye mata tace "ya Adnaan yace ki tashi ki ci" bnxa Afeefah tayi mata Jiddah ta juya ta fice, bayan kusan minti ashirin Adnaan ya dawo dakin rike da ledan magani, ya wani hade rae yana kallonta yace "baki tashi kin ci abincin ba yar rainin wayo" Afeefah ta sakko daga kan gadon hawaye cike idonta, hka ya tsareta har ta ci abincin snn ya bata magani ta amsa ta sha ya juya ya fice. Hka Afeefah ta kwana da xaxxabi daren ranan, bbu Wanda ya lura da hkn har suka sauka kasa yin break, ganin irin hararan da Mami ke watso mata yasa Afeefah ta shiga hada tea kmr ynda yayyinta suka yi, kmr kar ta kai cup din tean baki ta mike da gudu jin amai ya taso mata ta bar dinnin din kan ta karasa bayi hat ta soma kwarara amai, Jiddah ta mike tabi bayanta da sauri hka ma Mami, Amae ta dinga yi kmr xata amaye hanjin cikinta, Adnaan ya sakko hka ma Abba duk suna tambayar me ya sameta, Mami dae na tsaye bata ce komae ba, Jiddah ta taimaka mata ta shiga bayi don gyara jikinta, Abba na kallon Mami yace "me ya sameta?" Mami tace "Nima bn sani ba wllh" Abba ya dubi Adnaan yace "Dauko makulli a tafi asibiti" bbu bata lkci Adnaan ya dauko makullin motarsa ya nufi asibiti da Afeefah, kuka ta dinga rusa masa a mota wae kanta na ciwo har suka isa bbu bata lkci suka ga likita da yake da safe ne, bayan ya gama mata tambayoyi da rubuce rubucensa yace "kina sa damuwa ne a ran ki da yawa, kuma naga alamomin malaria a tare da ke xa mu yi maki karin ruwa"
Yau kwanan Afeefah uku rabonta da sch kuma ko kadan bata damu ba ita a dole ba lfya, hka kawae taji bata ma son xuwa sch din kwata kwata, da an mata maganar makaranta sae ta kuma langwabewa tace kai ko ciki, bata da aiki sae na danne dannen waya da kallo, yau kam tun safe take fara'a tunda ya Aliyu na hanya, Mami ta shigo dakin ta sameta kwance sae game take, tana ganinta tayi lamo kan pillow, Mami ta tabe baki tace "in Kinga kin xauna min gida gobe to shure shuren mutuwa kike," Afeefah ta turo baki kmr xata yi kuka Mami ta ajiye abinda xata ajiye ta fice daga dakin, Karfe sha daya da kusan rabi ta ji mai gadi ya bude gate, ta mike har tana tuntube ta nufi window din ganin Wanda ya shigo, Motar ya Aliyu ta gani, ta yi karan murna ta nufi kofa da gudu ta sauka downstairs bata bi ta kan Mami dake cewa ina xata da dangalallen rigan jikinta ba ta fice abunta, ya bude mota knn ya fito ta nufesa a guje ta rungumesa tace "oyoyo yayanmu" Murmushi ya sakar mata yana shafa kanta yace "baki je sch bane" ta turo baki tace "ba bani da lfya ba ka manta ne" ya xaro ido yace "har ynxu?" Langwabar da kanta tayi murya can ciki tace "ehh mana" ya kulle motarsa yace "Amma Adnaan yace min kin warke ae" bata fuska tayi tace "ko daxu fa sae da nayi amai, kuma har ynxu bna cin abinci, shi bae san komae ba" kama hannunta yyi ya nufi cikin gida da ita yace "idan na huta sae mu koma asibiti" kan rug Aliyu ya xauna ya gaida Mami dake falon a xaune, ta amsa tana murmushi tace "ya hanya Aliyu amma gudu kayi koh" ya shafa kai yace "A'a Mami ni bnyi gudu ba" tace "toh sannu, kaje ka huta bari in hado maka break" mikewa yyi Afeefah ma ta mike ta kama hannunsa suka nufi sama, ita ta hada masa ruwan wanka a bathroom dinsa ta fito ta samesa har ya soma bacci, ta hade rae ta shiga tashin sa tace "yayanmu na fa hada maka ruwan wanka" mikewa yyi ya xauna yace "na gaji da yawa ne" tace "to kayi wanka sae ka kwanta" ya gyada mata kai snn ya mike tsaye ya nufi bathroom.
Maryam ce xaune karkashin bishiya da wata kawarta sun fito daga lecture Karfe sha biyu, kawar me suna Fatima tace "wae har ynxu Afeefah bata ji sauki bne?" Maryam tace "ko daxu na kirata wllh, wae har ynxu jikin ne, tun da gobe da wuri xamu gama lecture xan kokarta in je in dubota" Fatima tace "Allah sarki Allah ya sauwake mata," Maryam tace "Ameen, ko xa ki rakani" Fatima tace "wllh Kinga akwae inda xa ni gobe da Mama da na raka ki wllh" Taku suka ji duk suka juyawa a tunaninsu wata course mate dinsu da suke jira ce, Fatima tace "Dr Shariff, ni dae mutumin nn na burge ni bbu ruwansa wllh" Maryam tace "ae kam bbu ruwansa duk cikin lecturers dinmu ya fi burgeni" shiru suka yi ganin ya karaso, duk suka gaishesa da ladabi ya amsa da dan murmushi a fuskarsa, har ya wuce ya dawo yana kallon Maryam yace "Maryam ryt?" Ta gyada masa kai tana murmushi, yace "ina kawarki Zainab?" Maryam tace "Wllh bata da lfya yau kwana uku," shiru ya danyi sae kuma yace "Me ya sameta?" Maryam tace "nima dae bn sani ba amma har anyi admitting dinta a asibiti, gobe ma xan je dubata" ya kusa second ashirin bae ce komae ba sae kuma ya juya ya bar wajen kawae.
Eeshatullah Goni ๐๐
[4/18, 1:05 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By *Ashmaad*
16......
Washegari kowa na ta shirin sch bnda Afeefah da tayi lamo kan gado, Jiddah dake xaune gaban madubi tana shafa mai tace "Wae Afeefah baki kallon agogo ne?" Afeefah ta galla mata harara tace "Bni da lfyan xan je sch?" Dariya Jiddah da Sadiya suka fashe da basu dae ce komae ba kowa ya ci gaba da harkan gabansa, Mami ce ta shigo dakin don ganin me suke har lkcn ba su sakko yin break ba, baki bude take kallon Afeefah tace "me kike har ynxu a kwance?" Afeefah ta mike xaune kmr xata yi kuka tace "Mami ni kmr amai nake ji" Karasowa Mami tayi cikin dakin ta nufi gun wayar rechargeable din dake gaban madubi, Afeefah na ganin hka ta mike da gudu ta fice daga dakin a tsorace, dakin Aliyu ta shige yana kwance yana bacci ta fasa masa kuka ya farka a rikice yana kallonta yace "Me ya faru," bae rufe baki ba Mami ta shigo dakin, Afeefah ta kuma fashewa da kuka ta nufi bayansa ta rikesa cikin kuka tana cewa "Don Allah yayanmu ka taimake ni Mami xata dokeni" Da sauri Aliyu ya rike wayar hannun Mami ganin tana neman shauda mata yace "don Allah Mami kiyi hkuri me tayi" tsawa ta masa tace "ka fita idona Aliyu, ka matsa ka ban waje" kin sake wayar Aliyu yyi yace "A'a don Allah kar ki doketa Mami, ki gaya min ne tayi" Afeefah ta kankamesa tana rusa kuka tana cewa "Wayyo yayanmu ka taimake ni" Fixgota Mami ta shiga yi Aliyu ya mike da sauri ya tare ta har lkcn yana rike da wayar hannunta yace "don Allah fa nace Mami" Afeefah na ganin hka ta nufi bathroom da gudu ta sa key, Mami ta fara ma Aliyu masifa kmr xata maresa shi dae bae ce komae ba ta juya ta fice daga dakin. Kulle kofar dakin yyi ya dawo ya nufi kofar bathroom yace "ae sae ki bude kofar" bude kofar tayi ta fito tana kuka har lkcn, ya galla mata harara yace "me kika yi" cikin kuka tace "yayanmu ban fa gama samun sauki har ynxu ba, wani lkcn sae in dinga jin amai, shine wae sae na je sch" wani mugun kallo yake mata lkci daya ya daka mata tsawa yace "a hkn ne baki samu sauki ba" wani sabon kukan ta fashe da ta durkushe nn tsakiyar dakin, yyi tsaki ya nufi bathroom. Har goma na safe Afeefah bata fito daga dakin Aliyu ba, wanka ma a bayinsa tayi, ya faki idon Mami ya tafi can dakinsu ya dauko mata kayanta, break ma a boye ya kai mata, ta ci ta sha hnklinta kwance tana kallo, yana danna laptop tana xaune gefensa tana kallo yace "gobe fa ko suma kike kisan sae kinje sch, gashi ynxu Kinsa Mami na jin haushi na" turo baki tayi tace "ae na sani"
Karfe hudu da minti goma Maryam ta fito daga faculty dinsu tafiya take tana kkrin kiran Afeefah da wayar hannunta don tayi mata kwatancen gidansu, shawara ta yanke kawae ta je ta samu su Jiddah su mata kwatancen gida, cikin rashin sa'a ta samu suna lecture, juyawa tayi kawae ta kama hanyar gate, Dr Aliyu ta gani ya fito daga office dinsa ya kulle ganin sun hada ido yasa ta tsaya don gaishesa, ya amsa da murmushi yace "ya lecture?" Tace "Alhmdllh" tafiya suka shiga yi don hanyar daya ne, ba tare da ya kalleta ba yace "ba tutorial ake maku a class ba Mae yasa baki tsaya ba" tace "Gidansu Afeefah nake son xuwa ne idan banje yau ba bani da tym kuma" yace "OK" parkin space suka isa ya nufi gun motarsa hkn yasa tace "Sae gobe sir" kai ya gyada mata yace "Allah ya kai mu" tada motarsa yyi, yyi reverse sae da ya iso inda take ya dan tsaya yace "idan ba damuwa shigo in rage maki hanya, if its OK by yhu" kasa cewa komae tayi gashi bata iya kallon fuskarsa tsabar kwarjinin da yake mata, xagayowa tayi kmr me tausayin kasa ta bude front seat din ta shiga da sallama wani dad'da'dan kamshi ya bugi hancinta , ba tare da ta kallesa ba kanta a kasa tayi murmuring din "Thnk yhu sir" "Welcm" kadae yace mata ya ja motar suka nufi gate. Sae da suka hau kan titi snn yace "jan bulo koh?" Da mmki ta daga kai tana kallonsa, to wa ya gaya masa, juyawa yyi ya kalleta lkci daya ya maida dubansa kan titi, Maryam tace "ehh can gidansu yake, amma ban san anguwar ba sae na kirata" bae ce mata komae ba ta shiga kiran Afeefah, Afeefah dake dakin ya Aliyu har lkcn ta dauki wayarta dake gefensa don ganin me kiranta, wara ido tayi tace "kawata ke kirana yayanmu, yarinyar tana da kirki ina sonta" bata jira cewarsa ba ta daga wayar, Maryam tace "Afeefah ki ban Address din gidanku ina hanya" Afeefah ta mike xaune da sauri tace "da gske?" Maryam tace "da gske mana," karan jin ddi ta saki tace "bari in maki text din sa ynxu" Maryam tace "kai Afeefah a hkn ne baki da lfya" tuni Afeefah ta kashe wayar ta shiga tura mata text din Address cike da jin ddi, Mika ma Dr Shariff tayi ya karba yana duba address din da suka xo traffic, yace "OK," snn ya mika mata wayarta, tace "ka gane wajen sir?" Yace "yea, ina da frnd a layin" Maryam bata kuma cewa komae ba har suka shigo layin, yyi parkin dae dae nmbr din Address din da ya gani, ya juya yana kallon Maryam yace "I think nn ne, ki kirata" Maryam ta shiga kiranta tace "ki fito ga ni a kofar gida" Afeefah ta doka tsalle tana kallon ya Aliyu da ke ta bin ta da kallo tace "ta xo yayana" hijab dinta ta figa ta daura kan 3 qtr gown din dake jikinta ba tare da ta bi ta kansa ba ta fice da gudu, kitchen ta nufa da sauri ta samu Mami tana girki ta marairaice tace "Mami kawata a sch ta xo gaishe ni bani da lfya tana gate wae" harara Mami ta watsa mata ta ci gaba da abinda take, kmr xata yi kuka ta fita tana isa balcony ba tare da ta bi ta kan takalmi ba ta nufi gate da gudu, leka waje tayi ta ga mota a Parke dae dae nn Maryam ta fito daga motar tana murmushi, Afeefah ta doka tsalle ta nufi gun motar ta rungumeta cike da jin ddin ganinta, Maryam tace "kai Afeefah Ca nake xan xo in ga baki da lfya ssae" Afeefah ta bata fuska ta taba wuyarta tace "taba wuya na ki ji toh" dariya kawae Maryam ke yi tana kallonta, duk wnn abinda suke Dr Aliyu Sharif na kallonsu, Maryam tace "xo ku gaisa da Wanda ya kawo ni" Afeefah tace "yayanki ne? Nima yayanmu jiya ya dawo" motar Afeefah ta nufa ganinsa a bude ta isa maxaunin Driver tace "ina yini ya....." Makalewa sauran gaisuwar suka yi a throat dinta, Maryam ta kauda kai tana yar dariya, kallonta kawae yake daga sama xuwa kasa barin foots dinta da ba takalmi, ta sunkuyar da kai kmr munafuka tana wasa da hijab.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:06 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By *Ashmaad*
17....
Dauke kai daga kallonta yyi yace "Allah ya sauwake Miss Zainab" ta sunkuyar da kai murya can ciki tace "Ameen ngd" tada motarsa yyi yana kallon Maryam yace "I will b on my way" Maryam tace "OK am grateful Sir, Allah kiyaye hanya" yace "Ameen" snn yyi reverse ya bar anguwar, sae a snn Afeefah ta galla ma Maryam harara tace "Wa yace ki xo da wnn mutumin Maryam" Maryam tayi dariya ssae tace "Ke rage min hanya yyi ba cewa nayi ya xo ba" Afeefah ta tabe baki don bata ma son tuna abinda ya faru ranan, ta kama hannun kawartata suka nufi cikin gida, Har kasa Maryam ta duka ta gaida mami da fitowarta daga kitchen knn, Mami ta amsa da fara'arta tana mata sannu da xuwa, Afeefah ta kuma janta suka nufi sama ta kai ta bedroom dinsu, dakin ya Aliyu ta koma da sauri baki har kunne tace "Yayanmu xo ka ga kawar tawa Maryam, tana dakinmu xo ka ganta" Aliyu da hnklinsa na kan laptop yace "kai Haba har kawar ta mu ta iso, to sannun ta da xuwa, maxa je ki gani nn xuwa" ta bata rae sanin idan ta tafi ba fitowa xae yi ba tace "ni yayanmu ka taso mu je mana" mikewa yyi sanin idan yana son kwanciyar hnkli to ya bi ta kawae, da fara'a ya gaisa da Maryam yana tambayarta ya karatu ya dan yi minti biyar a dakin snn ya koma dakinsa. Mami da kanta ta kawo wa Maryam drinks da snack ganin Afeefah bata da niyar kai mata, Maryam tayi mata godiya snn ta fita, hira ssae suka yi daga bisanni Maryam tace xata wuce ganin har biyar ya gota, Afeefah ta hade rae tace "to yaushe kika xo" dariya Maryam tayi tace "kar ki damu next tym xan kuma xuwa in dade amma sae kin xo namu gidan ke ma" Afeefah tayi murmushi tace "to ina nn xuwa idan Allah ya yarda" Dubu biyu Aliyu ya bata kudin mota, Mami kuma ta bata turare tayi masu gdya ssae snn Afeefah ta rakata har inda xata shiga mota, Maryam tace "amma de xa ki xo sch gobe ko Afeefah" Afeefah ta marairaice tace "Ehh kila in xo"
Washegari da safe ya Aliyu ya sa Afeefah gaba ta fara shirin sch, ko damuwa da kumbure kumburen da take bae yi ba, Karfe bakwae da rabi driver ya tafi da su da ita da su Jiddah, kmr munafuka ta nufi faculty dinsu ta samu karkashin wata bishiya ta xauna, takwas da minti sha biyar ta mike sanin suna da lecture Karfe takwas ta nufi lecture hall dinsu, gabanta yyi mugun ganin shima ga nufo hall din tasan lecture dinsa garesu ranan, har ya wuce ta bata ce komae ba tana shiga hall din ta nufi can back seat ta xauna, duk student suka soma nutsuwa ganinsa, sae da class rep ya mika masa marker snn ya daga kai yana kallon Afeefah yace "leave dat seat" kallonta duk yan aji suka fara yi ta ji kmr ta nutse kanta a kasa ta Mike tsaye, seat din dake gabansa ya nuna mata, a dan tsawace yace "come bck here" seat din ta nufa hawaye cike idonta ta xauna kmr munafuka gefen matan dake xaune gun tana goge hawayen da hijab dinta, bae damu da hka ba ya soma lecturing dinsa, kwata kwata hnklinta bae kan abinda yake koyarwa duk ta kagu ya gama ya tafi don duk a takure take, ita dae tasan ya fi awa daya yana lecturing ta ji yana buga desk da marker da sauri ta dawo daga duniyar da ta tafi ta ga kallonta yake "can yhu explain it to us plss" kwalalo ido tayi tace "explain wat?" Dariya duka class din suka kwashe da ta juya da sauri tana kallon kowa, sae hawaye, yarinyar gefenta ne tace "ga question din a board," Afeefah ta kalli board din da sauri, rungume hannayensa yyi yana kallonta, ta soma share hawayen da ya ki tsaya mata tace "Sir I didn't understand!" Wani kallo ya watsa mata yace "keep quiet nd stop lying, yhu weren't listen, leave my class!" Dago kai tayi tana kallonsa tana hawaye yace "i said leave my class" mikewa tayi ta fice daga class din da sauri tana kuka," karkashin bishiya ta samu ta dinga rusa kuka uwa an aikota, ta kusa minti sha biyar xaune gun taji an kirata, ta daga kai da sauri ta gansa tsaye bayanta, yace "am waitin for yhu at my office" bae jira cewarta ba ya bar wajen. Mikewa tayi bayan minti kusan biyar ta bi bayansa kmr munafuka, xaune ta samesa yana danna waya, ta sunkuyar da kanta a hnkli tace "am here sir" dago idanuwansa yyi yana kallonta ya nuna mata kujera yace "sit" ba musu ta xauna, ya ajiye wayar hannunsa yace "y were yhu absentminded in class today?" Sunkuyar da kanta tayi bata ce komae bae, kwankwasa kofa aka yi lkci daya aka bude aka shigo, ya daga kai yana kallon kofar, "ba ki iya sallama bne" tambayar da taji yyi ma wnda ya shigo knn, yarinyar ta karaso tace "srry nayi a xuciyata amma" kallonta kawae yake har yarinyar ta iso kusa da shi ta ajiye basket din hannunta da leda tace "yaya, Ummi tace kadda ka manta ka taho mata da drugs dinta later fah" yace "OK," yarinyar ta dafa goshinsa tace "kan ya daina maka ciwo yaya" yace "ya daina," tace "to ga abinci ka ci, ur favourite Ummi tayi maka," "ohh naji Teema, ba driver na jiran ki ba ne wae" ta juya da sauri tace "Bye yaya, sae ka dawo" tana kai wa nn ta fice daga office din. "Am tokin Zainab" Afeefah ta dago da sauri a hnkli tace "sbda bni da lfya" dan murmushi kawae yyi ya bude kulan abincin gabansa, shinkafa ce da lafiyayyen stew da nama, ya rufe ya dauki flask ya xuba ruwan xafi a mug snn ya shiga hada coffee, wani mug din ya kuma dauka ya xuba ruwan xafi snn ya hada wani coffeen ya xuba madara da sugar ya mika mata, dago kai Afeefah tayi tana kallonsa, yace "take" girgixa masa kai tayi da sauri tace "No thnk yhu" wani kallo ya watsa mata yace "ki karba my frnd" ba karamin tsoro ta ji ba ta karba hannunta na rawa yace "ke kar fa ki xubar min coffee kan table" sunkuyar da Kai tayi tana kallon coffeen hannunta gabanta na faduwa, ya dauki nasa ya soma sha.
Eeshatullah Goni ๐๐09077036932
[4/18, 1:06 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By *Ashmaad*
19.....
Shiru Dr Sharif ya dan yi kmr me naxari snn daga kai yana kallonta yace "ina xa ki ynxu" A hnkli tace "gida" ya ce "yayyinki fa?" ta make kafada tace "ni baxan jira su ba" yace "OK cry no more, I will fish out those galz, su nawa ne?" Tana kallonsa tace "su biyu ne" yace "gud!" Yana kai wa nn ya xaga ya shiga motarsa ita kuma ta nufi main gate. Da daddare Afeefah na xaune falo da yayyinta da su Sumayya suna kallo Abba ya shigo Aliyu na biye da shi a baya, duk suka yi masa sannu da xuwa ya nufi sama, Aliyu ya dawo kusa da Afeefah bayan ya amsa gaisuwar kannin nasa yana kallon idonta yace "Me aka maki" bata fuska tayi tace "a sch ne mana" yace "hado min coffee ki kawo min" yana kai wa nn ya nufi stairs, ta Mike ta je tayi abinda ya sa ta snn ta haura sama don kai masa coffee din, yana xaune yana waya ta karaso ta ajiye masa ta xauna tana kallonsa, yana gamawa ya ajiye wayar yace "Mami ce ko" girgixa masa kai tayi tace "a sch ne mana, wasu mata...." Shiru tayi da sauri ya daga kai yana kallonta yace "wasu Mata me?" Kmr xata yi kuka tace "su ke son min dariya a sch" harara ya watsa mata yace "shine kike masu kuka wawiya kawae, ke baki da bakin masu dariyar ne" hawaye cike idonta tace "ina masu ni ma ae" tsaki yyi ya dauki coffee dinsa ya soma sha, ta wara manyan idonta da ke kyalli da hawayen ciki tace "yayanmu ashe dama coffee na da ddi?" Ba tare da ya kalleta ba yace "da baki sani ba" tace "wllh ban sani ba sae da na 'dan dana daxu kuma har da madara ya sa min, yyi ddi ssae" cire cup din yyi daga bakinsa lkci daya yana kallonta yace "wa ya bakii?" Xaro ido tayi kmr warce ta tuna abu tana kallonsa a dan tsorace ta fara inda inda, ya ajiye cup din hannunsa ya murtuke fuskarsa yace "nace wa ya baki coffee," kuka ta fara yi tace "yayanmu siya fa muka yi ni da Maryam" tsawa ya daka mata yace "yaushe kika fara karya Afeefah? OK gobe xa ki kai ni inda ku ka siya coffee din" ta xaro ido a tsorace tace "wayyo yayanmu kayi hkuri, wani lecturan mu ne ya bani..." Tsit tayi ganin irin kallon da yake mata, ya mike ya xabga mata mari mai lfya yace "ki ka ce wa ya baki" kuka ta fashe da ya daura hannu lebbansa alamar tayi shiru, lkci daya ta hadiye kukan, fuskarsa a daure yace "wani lecturer ne wnn?" Ta hadiye sauran kukanta tace "A makaranta" ya kai mata wani marin a fusace yace "fita ki ban waje, doluwa kawae, " mikewa tayi da sauri ta toshe bakinta da hannunta ta fice daga dakin da gudu ta afka dakinsu ta xube gabansu Jiddah ta dinga rusa masu kuka, harkan gabansu duk suka ci gaba da yyi bbu Wanda ya kalleta bare ya ji me ya sa ta kuka sanin irin halinta. Ta gaji da kukanta ta Mike ta nufi gado ta kwanta lkci daya bacci ya dauketa.
Washegari da safe Afeefah ta je gaida Abba bayan tayi shirin sch kmr ynda suke yi duk safiya, xaune ta tadda duk yan gidan a falon Abba bnda Mami da ya Aliyu, ta xauna gefen su bayan ta gaishesa ya amsa fuskarsa a daure, Mami ce ta shigo snn ya Aliyu, Afeefah ta ki bari su hada ido da ya Aliyu, sae wasa da fingers dinta take, sunanta taji Abba ya kira, ta dago kai da sauri yace "Wani lecturer ne a sch kike xuwa office dinsa yake baki abu ki ci?" Xaro ido tayi a tsorace tana kallonsa, Abba ya daka mata tsawa "ba magana nake maki ba kike kallona hka, meye tsakanin ku, kuma a ina kika san shi? Kin mance doka na ne" Kuka ta fashe da tana kallon Aliyu da ya wani hade rae, Abba ya mike a fusace yace "au kuka xa ki yi min don kaniyar ki don ban sa an xane min ke ba?" Sunkuyar da kai tayi ta hadiye kukan da sauri, Abba yace "today shud b d first nd last day da za ki sake kula lecturer a sch, na hane ki da sake kula ko wani namiji a makaranta, hka kika ga yayyinki suna yi, to na sake jin hka sae nayi mugun Saba maki wllh, tashi ki ban waje sha shasha kawae" mikewa Afeefah tayi da sauri ta fice daga falon da gudu. Abba ya juya kansu Jiddah yace "ku kuma ban ga amfanin ku ba a tare, ku tashi ku ban waje" sum sum suka fice daga falon su ma.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:07 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By *Ashmaad*
Dedicated to my kawalliya romon jaa6a(khaleesat haiydar) ๐๐
20....
Afeefah bata yi wani break din kirki ba tsabar kukan dake cin ta ga shi bbu daman yi, Mami da ya Aliyu na falo, bbu abinda take sae jujjuya Fork din hannunta, Da kyar ta iya yi ma Mami sallama don har wani rawa muryarta yake, ya Aliyu kam ko kallonsa bata yi ba, driver na barin gidan ta rushe masu da wani matsanancin kuka cikin mota, Driver yyi parkin da sauri yana kallonta da mmki yace "kai! me ya faru" tsaki su Jiddah suka yi suka ce "Da' alla baba mu je iskanci ne kawae" har suka isa makaranta bbu Wanda ya kalli inda take, Duk suka nufi faculty dinsu, ita ma ta nufi faculty dinta, Bakin lecture Hall ta ga Maryam tsaye suna magana da wasu yan ajinsu, Maryam ta saki baki tana kallonta har ta karaso snn tace "Ni kam kina bn mmki Afeefah, bbu ranan da xae wuce baxa ki yi kuka ba, kukan ma mara reason? Haba ki dinga maintain mana, ke fa ba yarinya bace don Allah ki bari, ni baxan boye maki ba gskya haushi kike ban, abu kadan kuka kmr wata yar shekara uku" tabe baki tayi ta ci gaba da xancenta da yan matan ajin, Afeefah tayi tsaki ta bar wajen ta koma karkashin bishiya tayi xamanta. Har lecturer su ta iso Afeefah bata shiga aji ba, yan ajinsu da dama sun yi mata mgna lecturer fa na class sae dae ta ce ta sani, Tun daga nesa ta hangosa yana tahowa, gabanta yyi mugun faduwa taji kmr ta tashi ta falla a guje amma ta kasa, wasa da hijab dinta ta shiga yi gabanta na faduwa, dago ido tayi suka yi ido hudu da shi, ta sunkuyar da kai da sauri, har ya wuceta bae ce komae ba ita ma bata gaishesa ba, mikewa tayi da sauri ta bar wajen kmr munafuka. Da yamma tana xaune cafeteria ita kadae amma ba wnda suka saba xuwa ba, kwata kwata ranan bata shiga lecture ba a cafeterian ta yini, ko Maryam bata san inda take ba, juyawa tayi jin student din cikin cafeterian na gaisuwa don ganin Wanda suke gaisar wa gabanta ne yyi mugun faduwa ganin sa da tayi ya shigo cafeteria, tayi saurin sunkuyar da kai ta jawo hijab dinta ta dan rufe fuskarta, kujerar dake kallon nata ta ga ya ja ya xauna, mikewa tayi da sauri xata bar wajen yace "if I shud slap yhu! Koma ki xauna" kallonsa ta tsaya yi ya watsa mata harara yace "sit" komawa tayi ta xauna ta sunkuyar da kanta, fuskarsa a daure yace "me ya hana ki shiga lectures yau?" Kin dago kai tayi bare ta basa amsa, waiter din dake cafeterian ne ya ajiye ma Dr Aliyu soft drink a table da pack din straw, ya xare straw daya snn ya bude chill coke din gabansa ya saka straw din yyi sip din kadan snn ya dago kai yana kallonta yace "Answer my question B4 i slap yhu" kin dago kanta tayi, a dan tsawace yace "Zainab!" Dago kanta tayi lkci daya hawayen da ke makale idonta ya gangaro, yyi mata mugun kallo yace "oh kuka kike min?" girgixa masa kai tayi ta share hawayen da sauri, ya hade rae yace "me ya hanaki shiga lecture yau" a hnkli kanta a kasa tace "an min fada a gida ne" jin yyi shiru bae ce komae ba yasa ta dago kai tana kallonsa, ta ga wani mugun kallo yake mata, ta dauke kai, a nutse yace "fadan me aka maki?" Shiru tayi bata ce komae ba, ta ji yace "Zainab!" Kallonsa tayi snn tace "Ni ma bn san me nayi ba" Maryam ce ta shigo cafeterian da alamar Afeefah take nema, hango hijab dinta tayi ta karasa table din da sauri tace "kin kyauta Afeefah daga na fadi maki gskya shine har da wani kin shiga lecture...." Harara Afeefah ta watsa mata tace "ehh ban shiga ba" tana kai wa nn ta mike ta fice daga cafeterian sae a snn Maryam ta lura da Dr Sharif da ya bi Afeefah da kallo, ta dan kirkiri murmushi tace "sir ashe kana nn, ina yini" yace "lfya lau" ta juya kmr munafuka ta fice daga cafeterian. Mikewa Dr Sharif yyi ya ciro kudi ya mika ma waiter din snn ya fita, parking space ya nufa ya shiga motarsa yyi reverse ya nufi main gate, tafiya kawae take tana share hawayen idonta taga mota ya tsaya daga kusa da ita, ya bude motar ya fito yana mata mugun kallo yace "yhu walked out of me ina maki magana koh?" Xaro ido tayi tace "Sir Maryam ce..." Dakatar da ita yyi yace "meet me at my office yanxun nn" yana kai wa nn ya bude motarsa ya shiga ya bar wajen.
Eeshatullah Goni ๐๐
[4/18, 1:07 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
21....
A hnkli Afeefah ta tura kofa ta shigo bayan tayi sallama ta karasa kusa da table dinsa kanta a kasa tace "am here sir" jin bae ce komae ba yasa ta dago kai tana kallonsa, hararanta taga yana yi, yace "Sit" ba musu ta xauna tana kallonsa, yace "Me aka maki a gida?" A hnkli tace "yayanmu ne ya gaya ni da Abbanmu" kallonta yake yace "Me kika masa?" Girgixa masa kai tayi kmr xata yi kuka murya can kasa tace "wae don nace ka bani coffee" shiru yyi yana kallonta gnin hka yasa ta soma wasa da fingers dinta, "me yasa kika gaya masa na baki coffee?" Dago kai tayi ganin hawaye idonta yace "kar ki min kuka" gyada masa kai tayi ta mayar da hawayen snn tace "Dama yace in hado masa coffee ne da daddare shine da na kai masa daki nace masa ashe coffee yana da ddi ban sani ba sae yace eh mana, sae nace masa har da madara ka sa min....." Murmushin da taga yana yi yasa tayi shiru tana kallonsa, ya ce "ina jin ki" shiru tayi har lkcn, yace "go on!" Sunkuyar da kanta tayi tace "shine sae ya mareni, kuma ya gaya ni da Abbanmu ana ta min fada" muryarta na rawa ta kare maganan tana kallonsa, a hnkli ya daura fingers biyu kan lips dinsa yace "kar ki min kuka" ta gyada masa kai tare da hadiye kukan, murmushi ya kuma yi yace "meyasa kika gaya masa na baki coffee?" Girgixa masa kai tayi tace "ni ma ban sani ba" yace "beside gani nayi kina kallona ranan shi yasa na baki Zainab" xaro ido tayi tace "sir ni ban kalle ka ba wllh" murmushi kawae yake ya jawo foil papern dake desk a gabansa ya warware ya dauki table knife yyi slicin cake din ciki ya soma ci a hnkli yace "ya sunan yayan naki?" Sauke idonta tayi daga kallonsa tace "Ya Aliyu!" Ya dan wara ido yace "uhhn Namesake dina ne knn" Bata ce komae ba, bayan kusan minti uku ta dago kai tana kallonsa jin bae ce komae ba, suka hada ido don kallonta yake tayi saurin sunkuyar da kanta, cake din gabansa ya dauka ya mika mata yace "Take" ta girgixa kai da sauri tace "Thnk yhu sir" hararanta yyi yace "Shine kuma kike kallona?" Kmr xata yi kuka tace "ni ban kalle ka ba wllh" a dan tsawace yace "C'mom take this" har wani rawa hannunta yake ta karbi cake din da yake mika mata, yace "Eat" tace "Sir...." Kallon da ta ga yana mata yasa ta kai cake din bakin ta shiga ci a hnkli yana kallonta, rabi ta ci tace "Sir na koshi wllh" ba tare da ya kalleta ba yace "In xubar kike nufi, yhu had beta finish it right away," kmr xata yi kuka ta karasa cin cake din ya mika mata table watern da ya fara sha, ta karba a hnkli ta bude ta sha snn ta ajiye sauran, wayar ta dake jaka ne ya soma vibrate ta bude jakar yana kallonta ta fiddo wayar, xaro ido tayi sae kuma ta mayar da wayar da sauri yace "feel free, pick yhur cal" girgixa masa kai tayi da ganinta kasa a tsorace take, a nutse yace "wa ke kira?" Da kyar ta iya cewa "Yayanmu" yace "To dauka mana" bude jakar ta ta dauko wayar da ya katse a lkcn, kuma kira aka yi, ta daga kai tana kallon Dr Aliyu kmr xata yi kuka, yyi murmushi yace "pick" daga kiran tayi ta kara a kunne tayi shiru, ya Aliyu yace "Baki gama fushin ba Afeefah" turo baki tayi tace "Eh" yar dariya yyi yace "Srry Angel, nayi laifi baxan sake ba...." Make kafada tayi ta fashe da kukan karya tace "bana so, kuma ni bbu ruwana da kai kar ka sake min magana bbu ruwana da kai" Kallonta kawae Dr Shariff yake, ya Aliyu yace "ohh Haba yar Kanwata, I said am srry, yhu caused everything" ta kuma saka kukan karya tace "ni ka kyaleni joor" lallashinta kawae ya Aliyu ke yi yana mata promises kala kala, lkci daya ta fashe da dariya tace "yhu Promised fa yayanmu" yace "Allah Kanwata I mean it" dariya take sosae tace "ohk byee na hkura" katse wayar tayi ta mayar cikin jakarta ta dago kai tana kallon Dr Aliyu da ya kafa mata ido, wani kunya ya rufeta ta rufe fuskarta da tafin hannunta da sauri tana yar dariya tace "Sirrr" murmushi yyi yana kallonta har lkcn, hkn yasa ta cusa kanta cikin Hijab dinta tana dariyar jin kunya.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:07 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป'Ya Mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
Dedicated to all my fans.... Luv u all❤❤
22......
Gajiya tayi da boye fuskarta ganin bae ce mata komae ba ta bude fuskar a hnkli ta mike ba tare da ta kallesa ba tace "Sir am goin home" Yace "ashe bayan kuka ma har da dariya kika iya hka?" Boye fuskarta ta kuma yi da sauri ta fara wani sabon dariyar kmr an aikota, murmushi yyi yana kallonta, can ya mike ya dauki makullansa ya fice daga office din ta bi bayansa. Ba tare da ta kallesa ba yana kulle office dinsa tace "Sae gobe sir" yace "OK Allah ya kai mu" Main gate ta nufa ta samu adai daita da xae kai ta har gida. A falo ta samu ya Aliyu da Mami ta gaida Mami shi kuma ta 6alla masa harara xata haura sama Mami tace "ina su Jiddah" Tace "Mami sae shidda fa xa su gama lecture ni kuma tun uku na gama" Mami bata ce komae ba Afeefah ta haura sama, Aliyu ya dan saci kallon Mami snn ya Mike ya bi ta. Bedroom dinsu ya sameta ta bata fuska tace "ni ka tafi" Dariya yyi yace "ba kin ce kin hkura ba Kanwata" juya masa baya tayi yace "To ki shiriya mu fita yawo da daddare," tsalle ta doka ta rungumesa tace "Yeehhh thanks yayanmu, wllh na hkura" dariya yyi yace "toh ina jiran ki downstairs ki xo mu yi kallo," juyawa yyi ya fice daga dakin, ta shiga cire kayan jikinta snn ta fada bathroom don yin wanka. Da daddare Ya Aliyu ya fita da ita kmr ynda yyi mata alkawari, yawo suka yi ssae snn ya biya da ita shoprite don siya mata ice-cream da kuma shopping da ta ce xata yi, Shopping ta fara yi duk abinda tasan tana bukata ta dinga diba yana tura mata trolleyn, bangaren Ice-cream suka nufa daga karshe bayan ta gama siyayyanta tace "yayanmu mu dan siya ma su Anty Jiddah da Sumayya kar su ji haushi na koh? Ka ga suna ta fushi da xa mu fita" Yace "to xa mu siya masu" ice-cream robobi Shiddah suka siya snn ta kuma sa shi ya siya mata Wanda xata sha a hanya aka sa mata scoop biyu na vanilla da chocolate, juyawa tayi da sauri ba tare da thinking twice ko akwae mutum a bayanta ba taji ta fada jikin mutum kusan rabin ice-cream din hannunta ya xube jikinsa, da sauri ta koma baya, ta xaro ido ganin duk ta juye masa ice-cream din ta daga kai tana kallonsa feelin guilty, sae kuma hkurin da take shirin fara basa ya makale ta kafa masa ido, murya can kasa tace "Sir!" Kallonta shi ma yake, ta cire dankwalin kanta da sauri ta shiga goge masa ice-cream din chest dinsa bayan ta dafa shoulder dinsa duk da ynda ya fi ta tsayi tana cewa "Am srry sir bn san.... Kayi hkuri plss sir" kallonta kawae Dr Shariff yake, kanwarsa ce ta bullo da trolley tana ganin abinda ke faruwa ta karaso da sauri tace "ya aka yi yaya, bata gani ne," Afeefah dake goge masa jikinsa har lkcn da dankwalinta tace "Mistake ne bn sani ba" kmr xata yi kuka ta kare maganar tana kallon yarinyar, Dai dai nn ya Aliyu ya karaso gun da trolley ya tsaya kallon Afeefah da mamaki yace "meye hka wat happened?" Kmr xata yi kuka tace "ban sani ba na buge sa yayanmu shine sae ice-cream ya xube jikinsa" Karasowa Aliyu yyi ya fixge dankwalin hannunta yana mata mugun kallo, snn ya karasa goge ma Dr Sharif jikinsa ya danka masa dankwalin ba tare da ya lura da na Afeefah bne fuskarsa a daure yace "srry" snn ya ja ta suka bar wajen, waigawa take tayi tana kallon Dr Sharif da ya bi su da kallo kafin su sha kwana ta daga masa hannu alamar _bye bye_ tare da yi masa murmushi, shi ma ya mayar mata, biyan kudin kayansu yyi yana janta har lkcn fuskarsa a daure suka fita ya tura ta cikin mota cikin tsawa yace "don kin xuba masa ice-cream shine xa ki kama gardi kina goge masa jiki? Kina da hnkli kuwa?" Girgixa masa kai kawae tayi, yyi tsaki ya xaga driver seat ya ja motar a fusace ya bar wajen. Sae da suka isa gida yyi parkin snn ya kamo hannunta a hnkli yace "am srry sweet sis, me yasa kike taba namiji" sunkuyar da kanta tayi bata ce komae ba, hkuri ya shiga bata don yyi mamakin rashin kukan da bata yi ba, daga karshe ta dan yi murmushi alamar ta hkura, shima murmushin ya sakar mata ya ja kumatunta yace "ko kefa yar Kanwata," a hnkli tace "dankwali na yayanmu" yace "yana ina?" Ta dan yi shiru snn tace "ka bar masa" wara manyan idonsa yyi yace "meyasa baki ce min naki bane? Ohh yi hkuri xan siya maki wani atamfar me kyau kin ji" murmushi tayi da ya bayyana beauty point dinta da ke gefen kumatunta na dama tace "thnk yayanmu" ya bude motar ya fita ya fiffito mata da kayanta ya kira su Jiddah su xo su kwashe.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:08 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'ya mace kyautar Allah๐ธ๐ฉ๐ป
A true life love story
By Ashmaad
23....
Washegari Afeefah na xaune da Maryam da wasu matan ajinsu bayan sun fito daga lecturen safe suna hira tana basu lbrin lagos da irin mutanen dake can da irin rayuwar can, Salma tace "dama karatu ya kawo ki kano knn?" Girgixa kai Afeefah tayi tace "Nan ne fa garinmu, hutu kawae nake xuwa gun yayanmu a lagos lkcn ina sec sch" Rukayya tace "Shi da matarsa suke xaune a can knn" Afeefah ta wara ido tace "ke bae da aure fa, kawae aiki yake yi a can, toh idan ya dawo gida muna hutu sae ya tafi dani, wae nn ba a hutu ne ni?" Dariya duk suka yi suka ce "ana yi mana, ae mun kusa tafiya mid semester break kila next wk, idan an dawo sae a fara shirin exams" Afeefah xata yi magana suka ji muryar wani lecturansu yace "ku baku da aikin yi sae hada joint kuna hira yan matan nn, ba dae a ga littafi a hannun ku kuna karatu ba" daga kai duk suka yi suna kallonsa suka ga tare suke tafiya da Dr Sharif, Afeefah ta dan turo baki snn ta kalli Dr Sharif, ya watsa mata wani mugun kallo ya ci gaba da tafiyarsa, yan matan duk suka tabe baki, Rukayya ta ci gaba da xancen ta, Afeefah ta kuma kallon direction din lecturers din dae dae lkcn da Dr Sharif ya kuma juyowa suka hada ido ya kuma hararanta ya dauke kai, mikewa Afeefah tayi da kyar tace "uhnn ni xan tafi mosque" bata jira cewarsu ba ta bar gun da sauri. Da yamma sun fito daga mosque ta hadu da Dr Sharif da alamar shi ma daga mosque din yake, sau uku tana kallonsa tana kauda kai kuma a tare suke tafiyar sae da ita tana gaba shi yana baya, ana hudun ne ta gaishesa cike da jin kunya, bae amsa ba ya dan tabe baki yace "go to my office ki dauki adikon ki" Kai ta gyada masa snn ta canxa hanya. Bayan kusan minti sha biyar ta samu Maryam da yake basu da lecture tace "Maryam xo ki rakani office din Dr Aliyu Sharif in karbi dankwalina" Maryam ta kalleta da mamaki tace "me ya kai dankwalin ki kuma office din shi" Afeefah tayi dariya ta bata lbrin jiya a shop rite da daddare, Maryam ta fara dariya tace "Da yyi knock din kan ki ae" tare suka nufi office dinsa, Afeefah tayi knocking snn ta tura kofar, yana xaune yana duba wani textbuk, ba tare da ya kallesu ba ya amsa gaisuwar su, Afeefah ta karasa table dinsa murya can kasa tace "am here sir" daga kai yyi yana kallonta snn yace "I've seen yhu" murmushi tayi ta sunkuyar da kai, kallon dankwalinta da ke kan table dinsa a linke tayi tace "Sir in dauka" yace "dauka" dauka tayi tace "nagode sir" snn ta ajiye jakarta kan kujera ta xuge xip ta saka dankwalin ta rufe, Dr Sharif dake kallonta yace "Gashi ku karbo min chill coke a waje" dari biyar ya ciro ya mika mata, ta karasa ta dan risina ta karba snn ta nufi jakarta xata dauka su fita yace "sae kin tafi da jaka knn, ko dan kar in maki sata" xaro ido tayi tace "Aa fa sir" sae kuma ta juya ta bar jakar suka fita da Maryam dake dariya suka rufo masa office. Mikewa Dr Aliyu yyi ya nufi jakar tata ya bude ya ciro wayarta, murda office din ya ji anyi ya mayar da wayar da sauri yana kkrin xuge jakar Afeefah ta shigo office din tana cewa "Sir only coke kace ae....." Shiru tayi tana kallonsa, ya dan wara ido yace "Ehm ur pen plss I...I...I mean i can't find mine" Karasowa tayi tana kallon jakar ta dan duka ta bude xip din ta ciro masa pen din ta ta mika masa, karba yyi ba tare da ya kalleta ba yace "Thank yhu" ta gyada masa kai snn tace "Sir coke kadae....." "Yes" yyi saurin bata amsa ta juya ta fita daga office din. Kasa barin gun yyi ya kuma kallon jakarta ya duka da sauri ya xuge ya fiddo wayar yyi danne dannensa snn ya mayar jakan ya koma table dinsa da sauri ya xauna.
Ur comments do alwayz encourage me, get this fans
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:08 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace Kyautar Allah ๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
24/25.....
Da sallama Afeefah ta shigo office din ita kadae rike da coke din da straw ta karasa table dinsa ta ajiye tace "Sir ga shi" ba tare da ya kalleta ba yana ci gaba da danna wayarsa yace "Thnk yhu" ajiye masa change dinsa tayi ta nufi jakarta ta dauka xata fita ya dago da sauri yace "Ina maryam din?" Juyawa tayi tana kallonsa tace "tana waje tana jira na" yace "OK, ku baxa ku sha coke din ba" ta girgixa masa kai tace "Aa mun sha daxu" yace "OK" har ta isa kofa yace "Zainab!" Juyawa tayi tana kallonsa yace "Waye ku ka je shop rite da shi jiya?" Ta wara ido tace "Shine yayanmu ae" gyada mata kai yyi yana kallonta yace "Cousin brother koh" ta girgixa kai da sauri tana dariya tace "lah Abbanmu daya wllh fa Sir" shiru yyi yana kallonta snn ya gyada mata kai, ta juya ta fice daga office din.
Ana gobe xa su tafi mid semester break Afeefah ce xaune da su Maryam da Rukayya inda suka saba xama bayan sun fito daga lecture tana masu explaining wani topic a course dinsu BiOC 312 da suka ce ba su gane ba, Maryam sae kallonta take don bata taba tunanin Afeefah na da maida hnkli hka ba ka rantse kace lecturer ce ynda ta xage take fahimtar da su da turanci, duk ajin anyi xaton kuka ne kadae abinda ta fi iyawa, Muryar lecturen Course din suka ji a bayansu da alamar ya gama lecture da yan 200lvl yace "Ashe bayan kuka ma kina da kkri wajen karatu Zainabu" Afeefah ta rufe fuskarta da sauri da littafin hannunta tana dariya da yake sun dan saba da lecturan tana yawan ganinsa office din Dr Sharif ko a department wani lkcn, su Maryam suka fara dariya suna kallonta, shima yyi dariyan ya wuce. Da yamma suna dawowa daga mosque Afeefah ta nufi cafeteria da Maryam suna tafe suna hira Maryam tace "kin ga yan matan nn basu sake xuwa gun mu ba" Afeefah tace "Allah ya taimake mu don ni tsoronsu ma nake, kila sun...." Maryam ta xabga mata harara tace "Da'alla, matsoraciya kawae to me suka isa su mana, ae Dr Sharif ya kirani a ranan ban san wnda ya gaya masa ba, muka je har department dinsu da shi na nuna su" Afeefah ta xaro ido tace "ba ki ji tsoro ba Maryam? To me ya ce masu" Maryam ta tabe baki tace "oho, kawae yace in tafi, nayi wucewa ta" drinks Maryam tayi masu orderin bayan sun xauna. Biyar saura suka fito daga cafeterian Afeefah tace "ni gida xan tafi Maryam, sae mun hadu next wkk, xan sha bacci wnn break din da muka samu" Maryam tace "wae meyasa kika daina jiransu Anty jidda, kuma fa Abdul na tutorial a class tun daxu kuma course din Dr sharif" Afeefah tace "sbda wani lkcin ina riga su gama lecture sae in ta jiransu har in gaji" Maryam tace "to mu shiga tutorial din" Afeefah tace "A'a ni baxan shiga ba xan yi karatuna a gida, byee" tana kai wa nn bata jira cewar Maryam ba ta kama hanyar main gate, Maryam ta tabe baki ta nufi Department don shiga tutorial, tafiya kawae Afeefah take ko rabin main gate din bata yi ba ta hango yan matan da suka samesu da Maryam a cafeteria ranan da kawayensu su kusan uku suna tafe suna hira da shewa. ta xaro ido a tsorace ganin tahowa suke ta inda take tafiya, rawa jikinta ya dau yi ta fara kalle kallen inda xata buya kan su iso inda take, wani cafe dake wajajen ta shige da gudu ta labe kmr munafuka xuciyarta na bugawa, bayan kusan minti Uku taji muryar matan a cafe din sun shigo da alamar xa suyi photocopy, saura kiris ta fashe da kukan tsoro ganin basu lura da ita ba yasa ta fice da gudu ta kama hanyar gate, mota taga ya ja burki gefenta, har xata falla a guje ta ga Dr Sharif ne, tsayawa tayi tana share hawayen fuskarta da sauri tana kalle kalle kmr munafuka don bata yi wani nisa da cafen ba, yana fitowa daga motar ya hade rae yana kallonta yace "Meyasa baki shiga tutorial ba?" Girgixa masa kai tayi muryarta na rawa tace "gida xan tafi" ya galla mata harara yace "kukan me kike?" Ganin xata fashe masa da kuka yasa ya daka mata tsawa ba shiri ta hadiye kukan har lkcn bata bar waige waigen da take ba ta ga ko yan matan sun fito, ya juya yana kallon inda take kallo, dae dae lkcn da yan matan suka fito daga cafen, bayansa ta nufa da sauri muryarta na rawa tace "Sirrr," kallon yan matan kawae yake su ma kallonsa suke lkci daya kuma duk suka dauke kai suka fara tafiya suna isa dai dai inda yake tsaye Afeefah na bayansa kmr munafuka suka gaishesa, bbu yabo bbu fallasa ya amsa suka ci gaba da tafiyarsu kmr sun hada baki suka juyo gaba daya suna kallon Afeefah sae kuma suka kwashe da dariya suka yi gaba da sauri, Afeefah ta fito daga bayansa tana share hawaye ya daka mata wani mugun tsawar da ya raxanata yace "kuka kike min?" ba shiri ta hadiye kukan tana girgixa masa Kai, ya bude mata front seat bata jira yace ta shiga ba ta shige da sauri, ya rufe motar ya xaga ya shiga maxaunin driver snn ya tada motar ya nufi main gate, hanyar jan bulo taga ya nufa da ita, ita dae sae wasa da fingers dinta take, "kina jina?" Dago kai tayi tana kallonsa ta mayar da kanta kasa da sauri ganin ynda ya hade rae, "Seriously daga yau, i mean daga yau na kuma ganin kina kuka a sch xaki sha mamaki na, yhu re not a kid I c no reason xa ki dinga yi ma mutane kuka unnecessarily, kar in kuma ganin hawayen ki a sch" a dan tsawace ya kare maganan, ta gyada masa kai a hnkli, yace "kin ji ni da kyau kuwa?" Kai ta gyada masa nn ma, yace "to me nace?" a hnkli tace "kace kar in kuma kuka a sch" yace "good! Repeat after me" dago kai tayi tana kallonsa yace "ki ce, ke Zainab," murya can kasa tace "Ni Zainab," yace "kinyi alkawarin" nn ma a hnkli tace "nayi alkawarin," yace "baxa ki sake kuka a sch ba da ma ko ina!" Sunkuyar da kanta tayi ta maimaita abinda yace a hnkli, yace "yhu promised fa kika ce?" Kai ta gyada masa tace "yes sir" ya galla mata harara yace "da wani katon idonta a gurin" boye fuskarta tayi da tafin hannunta ta fara dariya a hnkli, dan murmushi yyi ya mayar da hnklinsa gaba daya kan tukin da yake, a hnkli dan kanta ta xame hannunta daga fuskarta. Nesa da gidansu ssae yyi parkin ya juya yana kallonta, ta dan wara ido tace "Sir dama kasan gidanmu?" Da sauri ta ba kanta answer tace "ohh Maryam ta taba xuwa da kai na manta" murmushi kawae yyi, tace "na gode sir" snn ta bude motar ta fice, "Zainab!" Taji ya kirata a nutse, ta juya da sauri tana kallonsa, a hnkli yace "Read ur books, dnt sleep too much during d break, ur exam is around the corner, nd I will b conducting my last test on Tuesday" Kai ta gyada masa tace "OK sir xan yi karatu," kai ya gyada mata ta kulle masa motarsa ta nufi gate dinsu shi kuma yyi reverse ya bar anguwar, tsaye ta ga Ya Aliyu a gate da alamar shigowarta yake jira, xuciyarta ya kusa shigewa cikinta, cikin rawar Murya tace "yayanmu"
[4/18, 1:08 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace Kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
26.....
"Zainab wa ya ajiye ki a mota?" Afeefah da jikinta ke bari ganin yanayin yayan nata, cikin rawan murya tace "Wayyo yayanmu ni ban shiga mota....." Mari ya kai mata yana huci yace "Ni xa ki ma karya? I will so beat the hell out of yhu ynxun nn idan baki gaya min gskya ba, wa ya ajiye ki a mota nace?" A tsawace ya kare mgnr, Afeefah da har hawaye ya soma taruwa idonta ta tuno promise din da tayi ma Dr Sharif da sauri ta hadiye kukan, tana girgixa masa kai a hnkli tace "yayan Maryam ne ya xo daukar ta shine suka rage min hanya" bata san lkcn da karyar nn yyi formulatin kansa a bakinta ba, Aliyu da idonsa suka sauya launi ya fixgo hannunta ya nufi cikin gida da ita yana huci, dakin Mami ya nufa da ita, lkci daya duk ya xayyane ma Mami abinda ya gani da kuma abinda ta ce masa, Mami ta saki baki tana kallonta tace "wato ke kin xama me kunnan Kashi ko Zainab, bbu Wanda ya isa da ke knn a gidan nn, to wae ni hka kika ga yayyin ki na yi ne, wllh ka tafi da ita ka xaneta Aliyu, gobe idan ance ta shiga motar mutane gudu xata yi ta bar wajen" Afeefah dae kanta na kasa, Mami tayi mmki wae yau Afeefah aka sa gaba ana yi ma fada bbu ko digon hawaye abinda bata taba gani ba tunda ta haifeta, shi kansa Ya Aliyu ba karamin mmki yyi ba har ya mareta bata yi kuka ba, kofa ya nuna mata alamar ta fita, ta nufi kofan a sanyaye ta fita ta jira sa a corridor, dakinsa ya nufa da ita ya xaunar da ita gefen gadon yana kallonta fuskarsa a daure yace "me yasa baki jin magana Afeefah, baki da kudin mota ne xa ki shiga motar mutane?" Girgixa masa kai kawae tayi, ya ji tausayin ta ya dawo gefenta ya xauna yace "Haba yar Kanwata, ynxu kin daina jin maganata ko?" A hnkli tace "ina ji yayanmu" yace "to meyasa kike disobeying dina idan na hanaki abu" kanta a kasa tace "na daina" ya dan yi murmushinsa me kyau ya dago kanta yana kallon cikin idonta yace "yauwa princess dina" dan murmushi ita ma tayi tana kallonsa, ssae ya Aliyu yyi mmkin kukan da Afeefah bata yi ba yana mata fada, ya mike yace "go nd bath ki sauko ki ci abinci kinji" mikewa tayi ta gyada masa kai ta fita daga dakin ta tafi nasu. Da misalin karfe goma na dare Afeefah ta fito daga wanka knn tana shirin kwanciya, su Jiddah gaba daya suna falo suna kallo, wayarta dake ajiye gefen gado yyi haske alamar ana kiranta don alwayz a cylnt wayar yake, karasawa tayi ta dauki wayar ta kafa ma new numbern dake kira ido tana tunanin waye, har sae da ya kusa katsewa snn ta daga a hnkli ta kara kunnenta, shiru taji na kusan second sha biyar har tana shirin katsewa taji anyi sallama, mamaki ne dauke fuskarta jin muryar namiji, da kyar ta iya gather din courage tace "Waye?" Yace "Baki amsa sallama ne?" Ta dan yi jim snn tayi saurin cewa "Srry, wrong number malam" tana kai wa nn ta fara kkrin katse wayar, "Wait Zainab!" still tayi jin ya kira sunanta, da kyar ta ce "A ina kasan ni?" A hnkli taji yace "Allah ne ya hada ni da ke" kuma kallon nmbr tayi da sauri snn ta mayar kunnenta tace "don Allah kayi hkuri wrong number ne ka kira" murmushi taji yyi yace "Wrong number kuma? Ba da Zainab Mahmoud Umar nake magana ba?" Xaro ido tayi jin ya kira full name dinta tace "Dan Allah ka rufa min asiri a ina ka samu nmbr na?" Yace "Allah ne ya bani" a tsorace tace "toh ni ba ni bace" bata jira cewarsa ba ta katse wayar snn ta kashe wayar gaba daya, jikinta na rawa ta kwanta ta shige bargo don ita dae tasan bata taba ba namiji lambarta. Da Asuba ringing din wayarta ne ya tasheta daga bacci ta mike a firgice tana kallon wayar, wani kara ta saki da ya farkar da su Jiddah gaba daya snn ta fice daga dakin da gudu ta afka dakin ya Aliyu tana ihun sunansa, shi ma a firgice ya farka yana kallonta yace "me ya faru?" Bayansa ta labe tana kuka tace "yayanmu na kashe wayata kafin in kwanta wani aljani ya kunna min wlh" sake baki yyi yana kallonta aka bude kofar dakin ta fasa ihu, shi kansa sae da ya ji tsoron bude kofar, Mami ce ta shigo dakin a tsorace ita ma, sae ga Adnaan ma ya shigo da sauri, su Jiddah ma a rude suka shigo dakin, duk suka tsaya kallonta, Abba dake tsaye bakin kofar duk suka ba hanya ya shigo dakin yana Kallon Afeefah da mamaki yace "me ya faru Zainab?" Kuka ta fashe da ta fito daga bayan ya Aliyu da sauri ta nufi gun Abba tace "Abba ka ga na kashe wayata jiya da daddare kafin in kwanta kawae ina jin aljani ne ya kunna min ya fara ringing ina bacci, wllh Na kashe kafin in kwanta" cikin matsanancin kuka ta kare maganan, su Jiddah suka kwashe da dariya har da kyakyatawa, Abba ya daka masu tsawa, Sadiya tace "Abba ni ce fa na kunna xanyi browsing jiya da daddare bn da data" dariya ssae su Jiddah suke suna kallon Afeefah, Ya Aliyu ya daka masu tsawa yace "don me xa ku kunna mata waya, wawayen yara kawae" juyawa Abba yyi tsaki Adnaan yyi yana hararan Afeefah ya fice daga dakin ransa a bace, Mami ta yi kwafa ita ma ranta a bace tace "nasan maganin ki, ba dae ke yarinya bace xa ki tada mutanen gida da ihu, xa ki sha mamaki na" tana kai wa nn ta juya ta fice daga dakin ita ma, su Jiddah suka kuma kwashe wa da dariya, ya Aliyu ya dauki filo ya jefa masu a fusace snn ya Mike da sauri, da gudu suka fice daga dakin, ya juya yana kallon Afeefah ya galla mata harara yace "fita ki ban waje da'alla" mikewa tayi ta fice daga dakin a sanyaye.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:09 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ธ๐ฉ๐ป
A true life love story
By Ashmaad
27__28
Afeefah ne xaune daki ita da Sadiya, ita tana karanta handouts dinta sadiya kuma na kwance tana danna wayarta, Mami ta shigo dakin tace "wae me ku ke yi ne? Ina Jiddah? Ku fito ku daura girkin rana don bbu yar da xan ma girki yau ta ci ku fito ku shiga kitchen" tana kai wa nn ta juya ta fita daga dakin, Afeefah ta ajiye handout din hannunta da sauri ta kwanta tare da lumshe ido kmr me bacci, Sadiya tace "ehh kya ma bude idon ne yarinya, sannun ki da wayo" tana kai wa nn ta fice, Afeefah ta kuma gyara kwanciya kmr me bacci, Jiddah ce ta shigo dakin bayan kusan minti biyar tace "ke Afeefah baxa ki fito mu shiga kitchen bne" Shiru Afeefah tayi kmr me baccin gske, Jiddah ta juya ta fice, Mami ce ta shigo dakin a tsawace tace "Zainab!" Mikewa xaune tayi da sauri tana murxa ido kmr xata yi kuka tace "Mami ni bacci..." Bayi ta shige da gudu ta kulle tun kan Mami ta karaso ganin ta yo kanta, Muryar Adnaan taji a dakin alamar Mami taje ta kirasa yana cewa "baxa ki fito ba sae na bude kofar nn, wa kika ajiye xae maki girki a gidan nn, ke baki da aiki sae dae a baki ki ci ki addabi mutane da kukan bnxa koh" murguda baki tayi kmr yana ganinta taki bude kofar, gate taji an bude downstairs ta washe hakora sanin ya Aliyu ne ya shigo, lkci daya ta saki kukan karya, Adnaan ya bude baki yana kallon kofar hka ma su Jiddah dake bakin kofar dakin a tsaye suna jiran fitowarta, muryar Aliyu su ka ji a corridor din rooms din yace "me ya faru?" Jiddah ta tabe baki tace "kaga yayanmu Mami ce fa tace mu je muyi girki shine ta shige bayi ta kulle" daga cikin bayin Afeefah tace "yayanmu ka ga fa karatu nake xa muyi test Monday" kmr xata yi kuka ta kare maganar, Aliyu ya watsa masu harara yace "mutane nawa xa suyi girkin? Ina su Sumayya?" Sadiya ta bata fuska tace "ba suna sch ba su" ya kuma watsa masu harara yace "ku biyu baxa ku iya girkin ba sae kace masu girkin gidan bikin, common get lost my frnd" Muryar Mami suka ji tana cewa "ka ga Aliyu ka fita idona bana son kana min hka a gidan nn ita wacece da baxata shiga kitchen ayi girki da ita ba, ta fi wani ne a gidan nn, ko idan ta tafi gidan mijinta ni xan bi ta ina mata girki?" Murmushi Aliyu yyi yace "sae mijin ya yafe mata girkin Mami," wani harara ta balla masa tace "Ka fita harkana fa, kuma ta fito idan ba hka ba in sa Adnaan ya daure min ita yyi mata shegen bugu" Juyawa Aliyu yyi yana hararan Adnaan, Adnaan ya fice daga dakin kmr xae tashi sama, Aliyu ya juya yana kallonsu Jiddah yace "ku bar dakin nn kar in taka ku" ficewa suka yi da sauri, Mami tayi kwafa ita ma ta fice tana cewa ta fito ta samesu kitchen idan ba hka ba sae dae ta ci bbu yau a gidan nn. Suna fita Afeefah ta bude kofar bayin, ta fito tana turo baki, ya Aliyu yyi murmushi ya kama hannunta ya nufi dakinsa da ita, har aka gama girkin rana Afeefah bata fita ba, Mami ta kwashe rabonta ta kara ma mai gadi Jiddah ta kai mashi, sadiya na kai ma ya Aliyu nasa a daki yace "Na Afeefah fa?" Tace "ina jin yana kitchen" yace "to dauko Mata," kai ta gyada masa ta fice duk da tasan bata da rabo, sae da ta isa falo ta fara dariya, ganin sadiya bata dawo ba yasa yace taje ta dauko abincin ta a kitchen da kyar ta yarda ta fita wae Mami xata doketa, tana shiga kitchen taga bbu komae an ma wanke tukunyar, ta koma sama kmr munafuka tace "sun cinye yayanmu" murmushi yyi yace "je dauko spoon ki xo mu ci nawa," kitchen ta koma ta dauko spoon suka ci a tare. Da yamma tana kwance dakin ya Aliyu tana kallo shi kuma yana dakin Mami wayarta ya soma ring mikewa tayi xaune ta dauki wayar gabanta na faduwa, wnn nmbr jiyan nn ne dae, sau uku yana kiranta yau bata dauka ba, mikewa tsaye tayi ta nufi dakinsu da gudu ta mika ma Jiddah wayar tace "Aunty Jiddah ki daga ki tambayi waye don Allah" karban wayar tayi tana kallon nmbr snn ta daga tayi shiru, jin anyi sallama yasa tace "wa ke magana wae," "ba da ke nake son magana ba, mika ma Zainab wayar" kmr munafuka ta mika ma Afeefah wayar. Afeefah tace "wae waye yace maki" Jiddah tace "oho" kara wayar a kunnenta tayi ta hade rae yace "Hello" tace "ina jin ka?" Murmushi yyi jin ynda ta amsa mashi yace "Me yasa kika ba yayarki wayar, kina tsorona ne?" Girgixa kai tayi tace "sbda me xan ji tsoron ka, ae Allah shine abun tsoro?" Yace "yea gskya ne," ta hade rae tace "kar ka kuma kiran layina ni ban san ka ba" yace "amma ni na sanki" a fusace tace "a ina ka san ni?" Cikin sanyin murya yace "nasan ki a bayero da kuma jan bulo" xaro ido tayi da mmki amma ta kasa cewa komae, yace "are yhu there?" Tsaki tayi tace "toh ni ban san ka ba kada ka kuma kiran layi na" katse wayar tayi ta jefar kan gado, Jiddah tace "wllh ki daina irin hka, baki san ko wani irin mutum bne kawae yaje ya cuce ki a bnxa, gwara ki bi sa a hnkli ku rabu lfya" Afeefah kmr xata yi kuka tace "to ni ya xan yi, bace kada ya kuma kirana ya ki ji" Jiddah tace "a hnkli xaki bi sa har ya rabu da ke, amma kar ki masa wlknci ko ki gaya masa bakar magana baki san wani irin mutum bne shi, baki kuma san meye a xuciyarsa ba, Afeefah ta bata fuska tace "wayyo na shiga uku to ina ya samu nmbrna Anty Jiddah?" Jiddah tace "oho ta ya xan sani nima" Afeefah tace "to in gaya ma yayanmu?" Da sauri Jiddah tace "ke! Gaya masa to tunda baki sa hnkli, so kike ya kirasa kawae ya xaxxagesa ki ja ma kanki" Afeefah tace "to to baxan gaya masa ba ba ruwana" fice wa Jiddah tayi daga dakin da sauri jin Mami na kiranta Afeefah ta xauna kan gado a sanyaye gabanta na faduwa, to waye wnn mutumin kuma, da daddare tana dan dube dubenta a wtspp Msge ya shigo da wani sabon nmbr, kura ma nmbr ido tayi lkci daya ta gane na me kiranta ne, gabanta na faduwa ta bude Msge din tana kallon sallamar da yyi mata, dakewa tayi ta amsa ko Allah xae taimaketa ya gaya mata inda ya Santa, bude Dp dinsa tayi da sauri tayi don ganin meye a kai, taga wata kyakkyawar yarinya rike da cake me kyau alamar birthday tayi, kallon yarinyar kawae take don gani take kmr ta taba ganinta amma ta rasa a ina, can ta fita taga bae mata reply ba still, kin sauka tayi tana jiran reply din, har bayan kusan minti takwas snn reply ya shigo, "ba ki yi bacci ba? Yhu re suppose to b readin ur book fa, who are yhu chattin with this late?" turo baki tayi ta mayar masa da cewa "Don Allah where did yhu get my contact frm, don Allah na ce" sae bayan kusan minti biyar reply ya shigo, "Go offline now!" Tsaki ta dan yi tana mmkin irin command din kmr ta san shi, reply ta mayar masa tace "ba ka ma Allah knn?" Lkci daya ya mata reply da cewa "to wa ke xan ma idan ban ma Allah ba, common go offline my frnd, idan baxa kiyi karatu ba ki kwanta kiyi bacci nd stop wasting ur tym here" ji tayi kmr ta saka kuka don takaici, gashi tana tsoron masa musu da ta tuno maganganun Jiddah, "OK" kadae ta mayar masa snn ta sauka ta kashe data ta jefar da wayar gefenta tayi kwanciyarta. Washegari kmr jiya vibration din wayar ta ne ya tasheta, ta jawo wayar da kyar tana kallon screen, din ta wara ido da sauri ganin lambar, samun kanta tayi da dagawa daga daya bangaren taji yace "almost tym for sallat baccin ya isa hka Madam" takaici ne ya isheta cikin bacin rae tace "to Ca nayi maka bbu masu tashi na ne a gidan mu" a nutse yace "ban ji ba, me kika ce" tsoro ne ya kamata tace "Ca nayi nagode, ynxu xan tashi" yace "OK" snn ya katse wayar. Da safe suna xaune dinnin suna breakfast, da ke ranan Saturday ne har da Adnaan da ya Aliyu Mami ce kadae bata dinnin din, Sumayya tace "ya Aliyu wnn hutun ka dde sosae" Afeefah ta galla mata harara tace "just two wk shine xa ki ce ya dde...." Wayarta da ke vibrate ne yasa tayi shiru tana kallon screen din wayar, ta dago kai tana kallon Jiddah da ta tabe baki ta ci gaba da shan tean ta, mikewa tayi ta nufi stairs da sauri, ya Aliyu ya bi ta da kallo, dakinsu ta shiga ta daga kiran kan ya katse ta kara a kunne, "Ae nayi xaton baxa ki daga ba" murguda baki tayi kmr yana ganinta ta ki cewa komae, "Zainab!" Ta amsa da "Na'am," yace "Gud mrnin" da kyar ta iya mayar masa da gaisuwar, yace "kinyi breakfast," girgixa masa kai tayi tace "shi nake yi" yace "okk srry, sae anjima" ji tayi an bude kofar dakin ta katse wayar da sauri ta juya tana kallon ya Aliyu, yace "wa ya kira ki?" Kame kame ta soma yi tace "yayanmu, kaga dama yayanmu Maryam kawata ce ta kirani," a nutse yace "karya kike, tell me the truth wa ya kira ki" muryarta na rawa tace "Ita ce yayanmu" ya fi minti biyar yana tsaye yana kallonta snn ya fice daga dakin, ta sulale kan gado ta xauna tare da sauke ajiyar xuciya, hka ta karashi mid break a gida a kullum xa a kirata sau hudu sau biyar kuma bata kin dagawa sbda abinda Jiddah ta gaya mata sae dae har lkcn ya ki gaya mata waye shi, kiri kiri ta daina hawa wtspp sbda shi don da ta hau xae ce ta sauka barin da nyt, gashi bata iya masa musu. Ran Monday da yamma ya Aliyu ya kare hutunsa ya kama hanyar lagos, Washegari Tuesday kusan a tare suka shigo sch da Dr Sharif, Afeefah ta sunkuyar da kai bayan su Jiddah sun nufi department dinsu, har sae da ya karaso inda take snn ta gaishesa, ya amsa va tare da ya kalleta ba ya nufi office dinsa. Har ya dan yi nisa ya juya yana kallonta yace "come, xo ki gyara min office" kmr munafuka ta bi bayansa ya bude office din suka shiga, yace "Just 10 mins ki gama gyara min office kafin in dawo" yana kai wa nn ya fita ta fara abinda ya sa, har ta gama bae dawo ba, ta gyara masa kan table dinsa ta jera masa duka buks dinsa gu daya, snn ta nemi guri ta xauna, har kusan takwas da rabi bata gan shi ba gashi suna sa lecture, taji kmr tayi kuka, sae kusan Karfe tara da rabi ya shigo yana kallonta yace "srry na je clinic ne, you've missed ur lecture koh?" Hade rae tayi bata ce komae ba ya karaso ya xauna yace "Wani lecture ku ke da shi" kanta a kasa ta gaya masa yace "to fiddo littafin kiyi karatu" mikewa tayi yace "ina xa ki?" Tace "xan fita in je inyi" yace "sit, kiyi a nn wajen" komawa tayi ta xauna kmr xata yi kuka snn ta fiddo littafin, shi dae sae kallonta yake ta farin glass din idonsa, can bayan minti kusan bakwae ta saci kallonsa taga idonsa na kan wani littafi, ta sunkuyar da kanta, bude kofar aka yi aka shigo da sallama Afeefah ta kafa ma yarinyar ido, yarinyar ta karasa kan table din tana cewa "yaya don Allah ka xo kayi ma baba sanusi magana, ka ji wae baxae kai ni ba yawo nake son xuwa" kallonta kawae yake ta ajiye basket din hannunta ta marairaice, Ya ajiye pen din hannunsa yace "Ummi ta sa ni ne" tace "ta sani mana, kawae shi sae ya dinga min abinda ya ga dama," mikewa Dr Shariff yyi yace "mu je" yarinyar tayi gaba yana biye da ita a baya, Afeefah ta bi su da kallo snn ta fiddo wayarta da sauri ta duba Dp din mutumi me kiranta taga hoton yarinyar ce a kai, duk sae tayi confuse tana tunanin to ko Dr Sharif ne ke kiranta, amma ae bae da nmbr ta, dubara ce ta xo mata tayi dailin nmbr dake kiranta, cikin second biyar wayar Dr Sharif da ke kan table ya soma ring, still tayi tana kallon table din, jiki ba kwari xata karasa table din ya shigo office din, juyowa tayi da sauri, yana kallonta yace "kina neman abu ne" girgixa masa kai tayi a daburce tayi saurin katse kiran da take masa, ya karasa table din yana kallon wayarsa murmusi dauke fuskarsa yace "lfya kike kirana" sunkuyar da kai tayi a hnkli tace "Sirr," Karasowa gabanta yyi yana kallon fuskarta yace "ya aka yi" kin bari su hada ido tayi murya can kasa tace "kayi hkuri ban san kai bne ba" murmushi yyi yace "to ynxu kin sani koh?" Juya masa baya tayi da sauri ta rufe fuskarta, ya nufi kujera ya xauna ya jawo basket din da Kanwarsa ta kawo masa ya shiga hada coffee, Ita dae har lkcn bata juyo ba, can ta nufi kofa tace "Na tafi Sir" a nutse yace "Zainab!" Juyowa tayi tana kallonsa snn ta karasa table din tace "gani sir" kujera ya nuna mata ta xauna snn ya mika mata mug din coffee. Girgixa masa kai tayi kanta a kasa tace "Ngd sir" jin bae ce komae ba yasa ta dago kanta a hnkli ta ga kallonta yake, sauke idonsa yyi daga kallon nata ya ajiye mata gabanta yace "je ki xubar a waje to" murmushi tayi ta dauki mug din a hnkli ta kai bakinta, rabi ta sha ta ajiye ba tare da ta kallesa ba tace "na koshi Sir" bae ce mata komae ba ta mike kanta a kasa tace "Sir I want to go nd read for test" yace "OK" snn ta fice daga office din. Ana gama sllhn Azahar Afeefah ta nufi lecture hall dinsu da Maryam, Maryam ta xauna kujerar gaba Afeefah tace "ke test fa xa muyi, mu koma baya" Maryam ta xaro ido tace "wani test?" Afeefah tace "na Dr Sharif mana" harara Maryam tayi Mata tace "ke wa ya gaya maki" Afeefah tayi shiru da dan mmki tana kallonta, sae a snn ta tuna ashe fa ita kadae ya gaya ma, "wllh nayi xaton kin sani, kuma bamu hadu yau bne da na gaya maki" Maryam tace "kin kyauta ae, da ni ce da na kira ki" bata jira cewar Afeefah ba ta nufi seat a baya, Afeefah ta bi bayanta sanin bata kyauta mata ba, gefenta ta xauna ta marairaice tana bata hkuri, Dr Sharif ya shigo hall din, tsit kke jin hall din bayan minti daya kowa yyi settle down, Dr Sharif yace "I will b conducting my last test today, hope yhu all are ready" kallonsa students suke da mamaki, bae damu da hka ba ya bukaci duk su fito da jakansu da any material da suka san is nt proper to b with dem while writtin his test, mikewa Afeefah tayi ta karbi jakar maryam da nata bayan sun dauki pen da takardar sa za suyi test din ta nufi front din hall din ta ajiye, hada ido suka yi ta dauke kai da sauri ta bar wajen ya bi ta da kallo, dictating questions din yyi masu snn ya basu time yace "this my last test, any one dat misbehaves I will cancel all the test he has done so far, I strictly warn yhu once more to respect ur selves" tsayuwarsa yyi bakin kofa yana danna wayarsa, bayan minti goma Afeefah ta juya tana kallon Maryam ta ga guda biyu kadae tayi ta ajiye pen, kallon Dr Sharif Afeefah tayi taga wayarsa yake danna wa, murya can kasa tace "kawo in rubuta maki 2 nd 4 a bayan paper da pencil sae ki goge da eraser" Ganin maryam bata tanka ta ba yasa ta mika mata papern nata gaba daya tace to gashi ki kwafa, nn ma bata ce komae ba, hkn yasa ta daga kai tana kallonsa ta ga kallonta yake, ajiye takardarta tayi da sauri, Dr Sharif yace "stand up" a hnkli kmr me shirin kuka tace "am srry sir" wani kallo ya watsa mata ba shiri ta mike ya nuna mata kofa alamar ta xo ta fita, kmr xata yi kuka ta nufi gaban class din tace "sir plss am srry i...." Tsawa ya daka mata yace "out!" Jakarta ta dauka ta fice daga class din ta nufi main gate, ta rasa dalilin da yasa bata yi kuka ba, cukuikuye takardar test din nata tayi ta jefar snn ta tsaida adai daita sahu ta hau ta tafi gida abunta.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:09 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
29.....
Mami na kitchen Afeefah ta shigo gida, Mami tace "Har kun tashi?" Afeefah tace "ehh," snn ta gaisheta ta nufi sama, kwanciyarta tayi bayan ta jefa jakarta kan gado, nan da nan bacci ya dauketa, vibration din wayarta da ke jakarta ne ya farkar da ita ta mike xaune tana mitsika ido ta jawo jakarta ta bude ta ciro wayar, tana kallon me kiran nata, Nmbr Dr Sharif ne, ta yi tsaki ta ajiye wayar ta koma ta kwanta. Da daddare tana gugan Hijabbanta wayar ta ya fara vibrate ta dauka tana kallon me kiran taga Nmbr Dr Sharif ne still, sae da ya kusa katsewa snn ta daga, ta kara a kunne tayi shiru, "kin ga dama knn" nn ma shiru tayi masa, yace "Zainab!" Kin amsawa tayi se da ya kuma kiranta tace "Na'am" hade da murguda baki, "me yasa na kira ki daxu ba ki daga ba" a takaice tace "bacci nake" yace "koh" shiru tayi masa, ya dan yi murmushi yace "yhu will explain dat tomorrow," katse kiran yyi, ta ja dogon tsaki ta ajiye wayarta ta ci gaba da abinda take. Tun daga ranan Afeefah ta soma wasan yar buya da Dr Sharif da ta gansa xata gudu ta canxa hanya idan ya kira ta ki dagawa, duk inda tasan xae ganta daina xama tayi a gun, in suna da lecture dinsa to ranan da wuri xata wuce gida, masallaci ma Dena xuwa Wanda xa su hadu tayi, sbda shi ta goge wtspp a wayarta, sae dae fa ynxu kukan ta ya ragu ssae har aka dinga Mamakin hka a gida, sau da yawa Maryam kan tambayeta wae me ya hadata da Dr Sharif take gudu idan ta gansa, sae dae tace bbu komae, ana hka suka fara Shirye shiryen exams, ana saura sati daya exams dinsu Afeefah na xaune gaban department dinsu da su Maryam an gama tsula ruwa knn, duk ta sakankance ranan dr Sharif bae xo ba don bata ga motarsa a parkin space ba kawae ta hangosa yana tahowa da wani student da alamar lecture ya fito, mikewa tayi da sauri ba tare da ta lura da wani katon dutse dake gefenta ba xata falla a guje ta buge kafa da dutsen sae ga ta kasa cikin ruwa, lkci daya ta fasa ihu uwa wata jaririya tana cewa wayyo kafarta, su maryam tuni suka mike a rude, Maryam ta fara kkrin dagota amma ta kasa don kin tashi tayi, Dr Sharif ya karaso gun da sauri shi ya dagota ta fashe da wani matsanancin kuka tana cewa wayyo kafarta, office dinsa ya nufa da ita ya sa ta xauna kan kujera har lkcn tana kuka, yana mata mugun kallo yace "ni dodonki ne da xaki dinga gudu idan kin gan ni Zainab? An ce maki ina da lkcn ki, listen daga yau kika kuma gudu idan ki ka gan ni, I will make yhu spell doom" kuka kawae take tana yarfe hannunta, a dan tsawace yace "pull off dat hijab my frnd" tana kuka ta fara kkrin cire hijab din don duk ruwa ne da datti, yyi tsaki ya mike ya nufi first aid box dinsa ya dauko ya dawo gabanta ya durkusa yana kallon kafarta da ke jini amma ya kasa taba kafan, yace "ina ke maki ciwo?" Ankle dinta da toes ta nuna masa da kneel, ya rasa ynda xae ce ta daga skirt din ma, kawae ya Mike ya nufi table ya dauki wayarsa, wata nurse ya kira tana dagawa yace "kina duty ne pls farida" ta amsa masa da tana gida, yace "OK plss ki xo Buk ynxu, over to my office wata student dina ce taji ciwo xa kiyi mata dressing" tace ga ta nn xuwa, yace "olryt tnxx" snn ya katse wayar, kanwarsa teemah ya kira yace "Fatima plss ki taho sch ynxu da spare hijab din ki" bae amsa tambayoyin da take jefa masa va yace "just come over" snn ya katse kiran ya dawo kusa da Afeefah dake hawaye har lkcn, ya daure fuska yace "srry" kae kawae ta gyada masa a hnkli ba tare da ta kallesa ba, yana tsaye kanta har Nurse Farida ta shigo office dinsa da sallama yyi welcoming dinta, Nurse Farida ta duka tana kallon kafar Afeefah yace "garin ya hka" Dr Shariff yace "she's runnin ne" yar dariya Farida tayi snn ta shiga fiddo kayan da xata gyara mata kafar a first aid box, yace "ki duba mata ankle dinta ma its hurting her" kuka Afeefah ta fara ganin matar ta tsoma cotton wool tace "na shiga uku sir kace ta min a hnkli xae min xafi" harara ya balla mata yace "Naki" da kyar ta bari nurse Farida ta wanke mata kafar tana kuka, ya fita don bata waje ta duba mata knee dinta, nurse Farida ta ga gurjewa kawae tayi shima ta wanke mata snn tace "to sannu an gama yan mata" Afeefah ta share hawayenta ta mike xata sa hijab dinta ta ji ta kasa tsayuwa da toes dinta ta koma ta xauna da sauri tace "xafi" matar ta kuma duba kafar tace "kin yi targade knn" kuka ssae Afeefah ta dinga yi tana yarfe hannu, nurse din ta fita ta kira Dr Sharif tace "Doctor tayi targade ne fa" kallon kafar kawae yake snn ya karasa ya duka kusa da ita yace "Sae an kai ki asibiti knn" Afeefah ta fashe da kuka tace "Sir ni ba sosae fa yake min ciwo ba" nurse Farida tace "Haba Dr ka gyara mata mana ba sae anje asibiti ba" girgixa kai yyi yace "su tafi asibiti dai" Dubu daya ya ba ma nurse din tayi transport bayan yyi mata godiya ta wuce, tana fita Fateema ta shigo, ledan hannunta ya karba ya ciro hijab din ciki ya mika ma Afeefah, ta karba kanta a kasa, Fatima tace "Yaya me ya sameta" yace "gudu take ta fada cikin ruwa" Fatima tace "eyya sannu" kasa dago kai Afeefah tayi, Dr Sharif yace "yhu can go, ko ba tare da driver kike ba," sallama tayi masa ta fita daga office din, ya kalli Afeefah yace "tashi in yi dropping din ki a gida, sae ki fadi kinyi targade a kai ki clinic" mikewa tayi ta dauki hijab dinta ta linke snn ya fita daga office din bayan ya dauki car key dinsa ta bi bayansa tana dingishi, har kofar gidansu ya ajiyeta, kanta a kasa tace "ngd sir" snn ta bude motar ta fita ta nufi gate da kyar sae kuma ta tsaya tana yarfe hannu, Dr Sharif ya fito yana kallonta yace "ya aka yi?" Durkushewa wajen tayi Cikin kuka tace "ni baxan iya tafiya ba kuma ciwo kafata ke min" xae yi magana aka bude gate dinsu, Mami ta fito da Rahamah, Afeefah ta mike da sauri, Mami da bata ma kula da Dr Sharif ba ta bude baki tace "meye hka Zainab" kuka ta saka tace "Mami faduwa nayi a cikin ruwa a makaranta ynxu gashi bn iya tafiya sosae ba, shine ya dawo dani gida, ina jin kafar ya karye ne" Rahmah ta juya ta fashe da dariya, Mami ta hade rae tace "ke mahaukaciya ce da xa ki fada cikin ruwa Zainab," ta girgixa ma Mami kai tana hawaye, sae a snn Mami ta kalli Dr Sharif, kansa a kasa ya gaisheta ta amsa tare da cewa "mun gode bawan Allah" Afeefah ta karbe da sauri tace "kuma makarantar mu daya fa, shine ya kira aka sa min spirit da magani" tana kai wa nn ta nufi cikin gida da kyar tana dingishi, godiya Mami ta kara masa tace baxa ka shiga daga ciki ba, dan murmushi yyi yace "A'a mama, ngd" tace "To Allah saka da alkhairi" sallama yyi mata ya shiga motarsa ita kuma suka koma cikin gida da Rahmah don dama kasuwa xata rakata ynxu kuma bbu maganar xuwa kasuwan. Da daddare Afeefah na kwance daki bayan Mami tasa Adnaan ya siyo mata mugunguna a pharmacy ta sha kiran Dr Shariff ya shigo wayarta, jawo wayar tayi ta daga a dan kunyace tayi shiru, cikin sanyin murya yace "ya kafar Zainab?" A hnkli tace "da sauki," yace "kun je asibiti?" Tace "um um ni nace bna so," yace "to ae sae an ja maki kafar xae daina," tace "ni bana so ya dan daina" shiru ya dan yi snn yace "in kawo maki fruits xa ki sha," shiru tayi bata ce komae ba, yace "Zainab!" Tace "umm xan sha" yace "mama xata bari ki fito?" Nn ma ta dan yi shiru snn a hnkli tace "kila."
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:10 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
30......
Bayan minti sha biyar Jiddah ta shigo dakin tana kallon Afeefah tace "ke ana neman ki downstairs," Afeefah ta mike xaune tace "ni?" Tsaki Jiddah tayi tace "A'a ni" snn ta fice daga dakin, Afeefah ta mike tana kallon kafarta da ke mata ciwo har lkcn, kasa taka kafar tayi don wani shegen ciwon da taji yana mata, da kyar tana dingisawa ta fita daga dakin ta sauka kasa, xaune ta ga yarinyar a falo Mami ma na xaune falon da Adnaan, Da kyar ta karaso cikin falon tana dingishi Mami tace "wae kafar har ynxu?" Kmr xata yi kuka tace "ciwo yake min sosae Mami" Mami tace "to sae a tafi asibiti gobe" Afeefah ta dan yi Mamakin ganin kanwar Dr Sharif, ta kirkiri murmushi tace "sannu da xuwa' yarinyar ta mayar mata da murmushin tace " ya jikin" Afeefah tace "da sauki" Ledan hannunta ta ajiye tace "Yayana yace in kawo maki" Afeefah ta kalli ledan a dan kunyace tace "ngdd" mikewa yarinyar tayi tace "ni xan koma Mumy ana jirana waje" Afeefah tace "tare ku ka xo?" Kai fateema ta gyada mata, Mami tace "ae da ya shigo," murmushi Fateema tayi ta kuma yi masu sae da safe, Mami ta kalli Afeefah da bata da niyar tashi tace "baxa ki rakata bane Afeefah" mikewa Afeefah tayi ta karbi hijab din jiddah tana dingishi ta bi bayan fateema da har ta kai kofa, har suka fita daga compound din bbu Wanda yace komae cikinsu, sauke glass din motar Dr Sharif yyi Afeefah ta karasa jikin motar kanta a kasa tace "ina yini sir" kallon kafarta kawae yake ta daga kai tana kallonsa jin bae amsa ba yace "har ynxu kafar bae daina ba" gyada masa kai tayi, yace "meyasa baki son a je asibiti a duba maki" tace "kila xa su ce xa su min allura kuma ni bna so" murmushi kawae yyi, a hnkli tace "sir ngdd" yyi noddin kansa yace "welcm, ki gaida mama" tace "xata ji," sae da safe ta kuma yi ma fateema snn ta nufi cikin gida ya bi ta da kallo, dariyar fateema ya sa ya dauke kai da sauri ya juya yana kallonta yace "meye hka" dariya take sosae ta kashe masa ido tace "waow at long last yaya!" Murmushi kawae yyi ya tada motar yyi reverse, tace "yaya amma student din ka kuma?" Harara ya galla mata ya maida hnklinsa kan tukin da yake. Afeefah na shiga gida Mami tace "har sun tafi" gyada mata kai kawae tayi ta kwanta kan kujera, Adnaan yace "kawar ki ce" mikewa xaune tayi da sauri tace "ehh ya aka yi?" ya daga kafada yace "na ga yarinyar na da hnkli da natsuwa ne" dariya Afeefah ta fashe da tace "ahaf ta dai fi karfin ka wllh gwara ma ka daina gnin hnklinta da natsuwa, class din yayanmu ce wnn" da gudu da yar kafarta me ciwo ta nufi sama tana kyalkyala dariya su Jiddah da Mami na taya ta.
Washegari da kyar Afeefah ta yarda aka tafi da ita asibiti a duba mata kafa, ba karamin wahala ta ba likitan da xae gyara mata targaden ba don sae da aka riketa ta dinga rusa masu ihu har sae da Adnaan ya mareta snn suka dan samu lfya, da yamma tana kwance ta fara bacci Dr Sharif ya kira wayarta, da kyar ta iya dagawa don har xaxxabi sae da targaden ya sa mata, murya can kasa ta gaishesa, yace "ya kafar kun je clinic" kuka ta sakar masa tace "bayan mun je an ja min, gashi wani sabon ciwo yake min" yace "wa ya ja maki?" Tace "wani likita ne mugu mana," yace "kiyi hkuri xae daina" da kyar tace "to" snn yyi mata sallama ta ajiye wayar, har kusan magrib Afeefah kasa tashi tayi daga kwancen da take tsabar ciwon da kafar ke mata, Mami ta shigo tace "wae har ynxu kafar ciwon yake maki?" Kmr xata yi kuka tace "Kinga Mami kumbura fa kila xae yi" Mami ta kalli kafar tace "gskya bae gyaru ba knn sae an koma" Afeefah ta fashe da kuka a tsorace tace "don Allah Mami kar mu koma wllh xae kuma mun tsami ne, kila sae xuwa gobe xae daina" Mami ta galla mata harara tace "a hkn kafa ya fara kumbura xa ki ce gobe xae warke? Bari dae Adnaan ya shigo" kuka ssae Afeefah take don bata mance axabar da ta sha daxu ba, Mami bata bi ta kanta ba ta fice, ana idar da magrib Adnaan ya shigo ya kalli kafar yace "ki tashi ki shirya mu koma" kuka ta kuma fashewa da bae bi ta kanta ba ya fice, tana cikin kukan wayarta ya soma ring ta dauka tana kallon Mae kiran, da kmr baxata daga ba da taga Dr Sharif sae kuma ta daga, ta sakar masa kuka tace "Sir kaga wae mai dani asibitin xa ayi a kuma jagwalgwala min kafar koh" shiru yyi bae ce komae ba ya barta ta ci gaba da kukanta, can yace "Zainab, where is d promise yhu made for me?" Hadiye kukan tayi lkci daya tace "ni?" Jin bae amsa ta ba yasa a hnkli tace "Kaga fa sir abun da xafi shi yasa nake kuka, wllh akwae xafi" yace "to ya isa, kina son ni in ja maki kafar?" A hnkli tace "ka iya ne?" Dan murmushi yyi yace "na iya" tace "to xan gaya ma Mami sae kae ka min," yace "OK," snn ya katse wayar, Afeefah ta shiga kwala ma Anty Jiddah kira, Jiddah ta shigo tana hararanta tace "lfya?" Afeefah tace "dan Allah kira min Mami baxan iya tashi ba" tsaki Jiddah tayi ta fice, ba a dau lkci ba sae ga Mami da Adnaan sun shigo dakin Adnaan na rike da makullin mota, Mami tace "ki tashi ki sa hijab" da sauri tace "Mami tsaya ki ji, wnn mutumin da ya kawo ni jiya yace xae gyara min kafar wllh, Dr ne shi ma, sunansa Dr Sharif Mami" Adnaan yace "to kawae Mami ya xo ya gyara mata don ni har tunanin tafiya asibiti nake da ita wllh" Afeefah ta marairaice tace "Ehh Mami, nima har tunanin binsa nake wllh" Mami tace "munafuka, ae sae ki kirasa ya xo ya gyara maki tun da hka kika fi so" dan murmushi tayi tace "to Mami" Mami ta fita Adnaan ya bi bayanta, suna fita wayarta ya soma ring ta jawo da sauri a tunaninta Dr Sharif ne sae ta ga ya Aliyu, a hnkli ta daga ta kara a kunne tare da cewa "yayanmu" "daxu na kira naji buzy, ke da wa kuke waya Afeefah?" Xaro ido tayi a dan tsorace tace "bbu kowa, ntwrk ne" "karya xa ki min knn" yarfe hannu tayi kmr xata yi kuka tace "yayanmu ni da kafata ke min ciwo ma tun safe bn san inda na jefa wayar ba" sauke ajiyar xuciya yyi yace "toh shknn princess, ya kafar ynxu" a hnkli tace "da sauki" yace "Adnaan xae kawo maki ice-cream na kira sa nace ya je ya siyo maki" washe hakora tayi tace "yauwa yayanmu nagode, nayi missin din ka ssae wllh" murmushi yyi yace "OK xan kira ki ltr ki min hira" tace "olryt yayana bye" ko ajiye wayar bata yi ba kiran Dr Sharif ya shigo wayar, kmr munafuka ta daga yace "ke da wa ku ke waya Zainab?" A hnkli tace "yayanmu ne Wanda ke lgs" yace "OK," tace "Sir na gaya ma Mamina tace to ka xo sae ka ja min kafar"
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:10 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
31__32
Adnaan ne yyi ma Dr Sharif iso har falon saukan baki, Afeefah dama tun da Dr Sharif ya kirata yace ya iso ta soma matsar kwalla tana kallon kafarta, Adnaan ya shigo dakin yace "ae sae ki tashi Hajiyata" mikewa tayi da kyar ta bi bayansa tana dingishi, kmr xata yi kuka tace ma Mami "don Allah Mami ki bar su anty Jiddah su rakani don kar in yi kuka" Mami tace "in xa su rakaki su rakaki mana" Jiddah ta mike Sadiya kam tace "bbu inda xani ni kam" Afeefah ta marairaice ta kalli kaninnta Sumayya da Rahama tace "ku baxa ku raka ni ba koh?" Mikewa Sumayya tayi tana dariya hka ma Rahamah snn suka nufi falon baki, Yana xaune yana danna wayarsa, Afeefah ta xauna edge din kujera a sanyaye tace "Sir ina yini" gyada mata kai kawae yyi, Xauna wa su Jiddah suka yi suma duk suka gaishesa, Jiddah sae kallonsa take da mugun mmki don tasan wnn ae lecturer ne, Dr Sharif ya amsa yana masu murmushi, Adnaan ya shigo falon yana kallonsu Jiddah da mmki yace "ku kuma me ku ke yi a nn" Afeefah ta marairaice tace "Allah sarki ya Adnaan ni fa nace su rakani kar in yi kuka" harara ya galla mata yace "sha sha sha kawae, har kina da bakin mgna" dariya su Sumayya suka yi, ya juya ya fice daga falon, Dr Sharif ya kalli Rahama yace "Get me cold water sis" mikewa Rahama tayi ta nufi fridge ta fiddo da ruwan sanyi ta mika masa ya karba snn ya mike ya nufi inda Afeefah take xaune, ya durkusa yana kallon kafarta, sae kuma ya mike ya fita daga falon yana rike da ruwan sanyin, ya wanke hannunsa snn ya dawo ya duka gabanta yace "Daurewa fa xa kiyi ki rufe ido" kai ta gyada masa hawaye na taruwa idonta, a hnkli ya daura hannun kan kafar, Afeefah ta sake kara ta dafa sa cikin muryar kuka tace "Sir wllh xafi yake min" hararanta yyi yace "take ur hands off me" ba shiri ta dauke hannunta daga kafadarsa, yace "Zainab!" Tace "Na'am" "ki rufe idon ki ki daure nace" Kai ta gyada masa hawaye na sakko mata, runtse ido tayi jin ya kuma kama kafar a hnkli, ba karamin daurewa ta dinga yi ba kar ta saki ihun bakinta, daga karshe dae dauriyarta ya kare ta kuma fasa ihu ta dafasa tana cewa "Wayyo Sirrr yana min xafi wllh" a dan tsawace yace "Zainab!" Muryarta na rawa tace "Sirr, ba kuka nake ba" yace "let go of me" cire hannunta tayi da sauri, yace "nace ki rufe idon ki" da sauri ta kuma runtse idonta, ba karamin axaba ta sha ba gashi Dr Sharif ya hanata kuka, hka tayi ta daurewa har sae da ta gaji ta saka masa kuka ssae, bae tanka ta ba ya gama abinda xae yi ya ji kafar yyi dae dae snn ya mike yana kallonta, juyawa tayi da sauri ta rufe fuskarta da kujera ta dinga kuka tana yarfe hannu, ya kalli Jiddah yace "Anty a dan taimaka min da man xafi" murmushi tayi ta Mike ta fita daga falon, ba a dau lkci ba dawo da man xafin ya karba ya duka gaban Afeefah juyowa tayi da sauri tace "Sirr" yace "srry shafa maki maganin xan yi kawae" mikewa yyi bayan ya gama shafa Mata, yace "Allah ya sauwake" Sadiya ce ta shigo falon autan Mami fadila na biye da ita rike da faranti me dauke da drink da ruwa, ta ajiye suka gaisa da Dr Sharif da take ma kallon mamaki ita ma, Afeefah tace "Sir kai fa aka kawo ma ruwa" murmushi yyi yace "am OK, tnx a lot" Sadiya tace "A'a da dae ka sha kadan sir" Murmushi kawae yyi ya xauna yana kallon fadila ganin ynda suka yi kama da Afeefah yace "hw are yhu" murmushi tayi tace "Fyn sir" "wani class kike?" Tace "am in ss1" ya ce "Nyc, art, science or a commercial student?" yar dariya tayi tace "Science student ce ni Sir" yace "Umm I c, wats ur favourite subject?" Ta wara ido tace "Biology Sir" ya xaro ido yace "Really?" Ta gyada masa kai yace "to in maki tambaya?" Mikewa xaune Afeefah tayi ta kyalkyale da dariya tace "Sir yi mata, bbu abinda ta sani sae kuka wa Mami" xaro ido duk occupant din falon suka yi jin abinda Afeefah tace, lkci daya suka saka dariya Dr Sharif dake murmushi yace "keep mute my frnd, ba ke taga kina yi ba" Fadila da har ta bata rae ta yi murmushi tana kallon Afeefah da tayi shiru bata ce komae ba, Dr shariff ya kalli Fadila yace "Dnt wrry, baxan maki question ba because yhu just started, amma ki maida hnkli ssae a karatu kin ji" Fadila tayi murmushi ta gyada masa kai tace "ngdd sir" Sumayya ya kalla yace wani class ke kike, tace "Ss2 sir" yace "dats Gud, a science student?" Gyada masa kai tayi tace "yes sir" yace "okk I will ask yhu questions some other tym" ya kalli Rahmah yace "ke fa" ta sunkuyar da kanta tace "am also in ss2 sir" yace "uhm great, I will also ask yhu questions some other tym" ta gyada masa kai tace "OK sir" Su Jiddah ya kalla yace "kuna 300lvl a buk studying Micro biology ryt?" Murmushi duk suka yi suka ce hka ne, yace "na taba shiga ajin ku?" Suka ce "ehh kana shiga, kuma muna haduwa a laboratory sosae," yyi murmushi yace "to ku maida hnkli a karatu kun ga ku ne manya, but if am nt mistaken kuna da yaya da ta taba Micro bio?" Jiddah tace "ehh Anty safeeya da Farida sun yi aure kuma" yace "Yea naga kuna kama ne da su" "Allah ya taimaka" duk suka ce Ameen, sosae yyi Mamakin duk yayyin Afeefah da kanninta mata ne, bae san cewa duk _'ya mace kyautar Allah_ ba ce, mike yyi yana kallon Afeefah ya ga ta wani hade rae, kmr xata yi kuka tace "Shine ni baka tambayeni komae ba koh sir" murmushi yyi yace "to izun ki nawa a islamiyya?" A hnkli tace "na sauke" dariya yyi yace "Ma'sha Allah ashe ke din Malama ce?" Murmushi tayi ta boye fuska yace "to Allah sa na tsoron Allah ne" tace "Ameen" to tashi ku je ki ce ma yayanku xan tafi, tace "Sir kafar fa?" Yace "a hka xa ki tafi" mikewa tayi tana durdurkusawa ta fita daga falon, ba a dau lkci ba sae ga shi sun dawo da Adnaan, Adnaan yyi masa sannu da aiki, Dr Sharif yyi murmushi yace "ae na gama wucewa xan yi," Adnaan yace "to mu shiga ku gaisa da Mamin mu," ba musa Dr Shariff ya bi bayan Adnaan suka nufi main falo, Mami na xaune falo Afeefah na xaune gefenta tana nuna mata kafarta suka shigo falon, sauke kafar tayi da sauri, Dr Sharif ya sunkuyar da kai ya karaso cikin falon da ladabi ya gaida Mami ta amsa da fara'a tana tambayarsa mutanen gida, yace "duk suna lfya" Mami tace "to ya sunan?" Murmushi yyi ya kuma sunkuyar da kai yace "sunana Aliyu" Mami tace "Au ashe ma 'da na ne, to mun fa gode Aliyu Allah maka albarka" yace "Ameen mama, ni xan koma" Mami tace "baxa ka ci abinci ba" yace "Alhmdllh mama na ci a gida" Mami tace "toh Allah tsare, mun gode ssae" sallama su Jiddah suka yi masa snn ya nufi kofar fita Adnaan na biye da shi a baya don ya rakasa, Mami ta buge Afeefah tace "baxa kiyi masa sae da safe ba" turo baki tayi tace "sae da safe," amma tuni ya fita, a bakin gate suka hadu da Abba cikin motarsa yana jiran Mai gadi ya bude masa gate, Adnaan ya karasa yyi masa sannu da xuwa da ladabi, snn yyi ma Dr Sharif alamar ya xo su gaisa, Dr Sharif ya karasa gun motar ya gaida Abba cike da ladabi, Abba na kallon Adnaan yace "bako kayi knn" Adnaan yyi murmushi Abba ya ja motarsa ya shiga gidan don mai gadi ya bude masa gate din, Adnaan ya raka Dr Sharif har inda motarsa yake snn ya kuma yi masa gdya yyi masa sae dae safe ya koma cikin gida, Karfe goma da rabi Afeefah ta mike daga falo don wucewa sama tayi bacci, ji tayi kafar ya rage mata ciwo ssae, ta nufi sama tana dingisawa ta shiga bedroom dinsu ta cire kayan jikinta ta shiga wanka, ko da ta fito turare kawae ta shafa ta sa kayan baccinta ta nufi kan gado ta kwanta ta ja bargon snn ta dauki wayarta, mis cals har shidda ta gani ta xaro ido ta bude da sauri don ganin ko na waye, ta ga na yayanmu har biyar sae na Dr Sharif guda daya, kmr xata yi kuka take kallon mis cals din ya Aliyu gashi ba ta da kati bare ta kirasa, kiran Dr Sharif ne ya shigo wayar, tayi shiru tana kallon wayar har ya kusan katsewa snn ta daga ta kara a kunne tayi shiru, A hnkli taji yace "Zainab!" Tace "uhm" "ba kiyi bacci ba" murya can kasa tace "ynxu xan yi" yace "OK ya kafar ynxu?" Tace "da sauki" yace "tell me d truth" a hnkli tace "Allah sir ya rage min ciwo ynxu" yace "OK Allah ya kara sauki" tace "Ameen" murya can kasa yace " yhu are starting exams next week, kina karatu kuwa Zainab" tace "Sir ina yi" yace "OK yhu knw kinyi missing test dina da yawa, hw are we goin to do now?" Kmr xata yi kuka tace "ni ma bn sani ba sir" yace "ina script din test din last wk da kika yi?" Tace "Na jefar sir" "Sbda nace ki fita?" A hnkli tace "ehh" murmushi yyi yace "don ma bn yage test din naki ba" Su jiddah ne suka shigo dakin da Sadiya, hkn yasa taki cewa komae, yace "Zainab!" Tace "Na'am" "kinyi shiru" juyawa tayi ta ga Su Jiddah sae kallonta suke, tayi murmushi tace "um um" Dr Sharif yace "Ko kin fara jin bacci ne?" Da sauri tace "ehh" yace "OK kiyi alwala kiyi addu'a kafin ki kwanta" tace "to xan yi" sallama yyi mata ya katse wayar ta ajiye tana kallon su Jiddah dake ta kallonta har lkcn, xata yi magana Jiddah tace "ke da waye" Afeefah na gyara kwanciyarta tace "Dr Sharif" xaro ido duk suka yi Sadiya tace "ko dae son ki yake Afeefah" mikewa Afeefah tayi da sauri ta xauna tana kallonsu, duk suka kwashe da dariya suka ce "tab soyayya ku ke ashe" Afeefah ta hade rae tace "wllh ba soyayya mu ke ba kawae dae...." Sae kuma tayi shiru ta rasa me xata ce masu, Suka kuma saka dariya suka ce "tab, Kinga 'yan matansa a Buk kuwa, duk da dae su suke ta haukansu, to a ina ma kuka hadu da shi" tsaki Afeefah tayi tace "ni dae ba soyayya muke ba" Jiddah tace "kya fada masu dae" Afeefah xata yi magana wayarta ya shiga ring ta duba ta ga ya Aliyu ke kiranta, xaro ido tayi tana kallonsu Jiddah tace "Don Allah Anty jiddah ki dauka ki ce masa ae nayi bacci tun daxu kafata na ciwo, idan yace ya kira ya ji buzy sae ki ce ke ce ke waya" Jiddah ta harareta tace "ehh Sannunki, ki ba Sadiya mana" da kyar ta lallabasu har da dan hawayenta ganin wayar ya kusa katsewa snn Jiddah tayi sallama kmr munafuka, a tsawace yace "who asked yhu to pick my cal ina wasa da ku ne, ina Zainab din" Jiddah tayi tsuru tsuru tana kallon Afeefah, Afeefah ta hade hannayenta a tsorace alamar ta rufa mata asiri, Jiddah tayi saurin cewa "yayanmu tayi bacci tun daxu, kasan likita ya xo ya kuma gyara mata kafarta" a tsawace yace "to wa ke waya daxu?" Jiddah da gabanta ke faduwa tace "ni ce yayanmu bata san na dauka ba ma, ta riga tayi bacci" yace "tasheta ki bata wayar" Jiddah ta juya tana kallon Afeefah ta shiga buga gado tana cewa "Zainab, ki tashi yayanmu ya bugo, Zainab, Zainab" tana shirin mika ma Afeefah wayar yace "kyaleta kawae, sae da safe" yana katse wayar Jiddah ta wurga wayar kan gado ta dinga kyalkyala dariya sadiya na taya ta, Afeefah tayi murmushi ta rungumeta tace "nagode sister" Sadiya tace "da kika ce masa waya kike bae tambayeki da Wanda kike wayar ba" Jiddah tace "ke dae bari ae abun ya bani mamaki" Afeefah a sanyaye tace "da ni ce da yayi min jaraba" Sadiya tace "wnn kuma ke kike shige masa ae" kwanciya Afeefah tayi bata kuma cewa komae ba, Dr Sharif ne ya fado mata, ta Mike da sauri ta nufi bayi tayi alwalan da yace tayi snn ta fito ta kwanta bayan ta gama addu'o'inta.
Washegari da asuba Afeefah tayi xaune bakin gado tana Mamakin mafarkin Dr Sharif har sau biyu da tayi daren ranan, mikewa tayi xata je yin alwala taji kafarta yyi mata sauki sosae, ba karamin farin ciki tayi ba tana kallon Jiddah da ta fito daga bayi tace 'kalli anty jiddah na fara iya taka kafar ynxu," Jiddah tace "ashe dae likitan gske ne lecturan" Afeefah ta harareta tace "ba sunansa lecturer ba, its either yhu cal him Dr Sharif, or Dr Aliyu tana kai wa nn ta shige bayi, su Jiddah suka kwashe da dariya, tana xaune kan darduma bayan ta idar da sllh wayarta ya shiga vibrate ta dauka ganin Dr Sharif ne, bayi ta shige ganin su Jiddah sun xuba mata ido, gaishesa tayi ya amsa snn yace " ya kafar Zainab" tace "Sir ya daina min ciwo ssae gashi ina tafiya ynxu" yace "Alhmdllh, Allah kara sauki" tace "Ameen" yace "xa ki xo sch yau?" Ta girgixa masa kai tace "um um sae gobe" yace "ki daure ki xo xan maku revision yau" shiru ta dan yi snn tace "to xan xo" sallama yyi mata ya katse wayar ta bude kofar bayin xata fito ta ga su Jiddah labe bakin kofar bayin, ficewa suka yi daga dakin gaba daya suna dariya, ta tabe baki tayi kwanciyarta.
Yau ya kasance laraba kuma ranan da su Afeefah xa su kare exams dinsu, sanye take da atamfarta red colour da blue ta daura farin lab coat kan kayan nata tayi rollin kanta da black gyale karami ta sa flat shoe fari, ba karamin kyau tayi ba ranan duk da bata yi make up ko kadan ba don bata taba shiga skul ba hijab ba sae ranan, shima kuma don practical xa suyi na exams, Maryam ma sanye take da lab coat din da alamar laboratory xa su da safen, Maryam da ke ta kallonta tace "gskya Afeefah kin cije ni yau" Afeefah ta harareta bata tanka ta ba, wani faduwar gaba ne ya xo mata ganin Dr Sharif shima da alamar laboratory xa shi don sanye yake da white lab coat din shima, sak likita idan ka gansa, sunkuyar da kai tayi ta rasa dalilin da yasa duk lkcn da xata gansa sae ta ji faduwar gaba ba kadan ba, Maryam kam kasa daina kallonsa tayi, ba ita kadae ba har 'yan matan dake wajajen, wasu sae gaishesa suke yana sakar masu murmushi yana amsawa. Da kyar Maryam ta iya bude baki ta gaishesa ganin kusan a tare suke tafiyar ya amsa yana kallon wrist watch din hannunsa yace "so early hka xa ku lab?" "Um" kawae Maryam tace ba tare da ta kallesa ba, shi kam sae satan kallon Afeefah yake, dai dai lkcn da ta dago ita ma ta saci kallonsa suka hada ido, dauke kai tayi da sauri tana murmushi kmr munafuka murya can kasa tace "Gud morning sir" bae tanka ta ba yana kallon Maryam yace "hope yhu guyz are ready for the exam?" Maryam tace "in'sha Allah sir" yace "dats gud, Allah bada sa'a" ta amsa da Ameen, ya kuma kallon Afeefah ya dauke kai snn ya bar su nn suna jan kafa ya nufi lab, Maryam tace "ina son maki tambaya Afeefah" Afeefah ta dago tana kallonta tace "ina jin ki" Maryam ta dan yi shiru, har sae da Afeefah tace "kin yi shiru kuma" Maryam ta kirkiri murmushi tace "ki gaya min tsakanin ki da Allah meye tsakanin ki da Dr Aliyu Sharif" Afeefah ta dan hade rae tace "kmr ya" Yake maryam tayi tace "ko kuma ma dae mu je lab, am only joking" Afeefah bata tan ka ta ba har suka isa lab din. Karfe sha daya suka fito daga exam, Afeefah ta nufi cafeteria Maryam dake bin ta a baya tace "ya exams din?" Afeefah tace "Alhmdllh," Maryam tace "to Allah ba mu sa'a" a takaice Afeefah tace "Ameen" bayan ta xauna kujera ta fiddo wayarta, text din Dr Sharif ta gani, ta bude ta karanta content din, "Yhu look awful bbu hijab yau Zainab, Hijab rufin asirin 'ya mace, kar ki kuma irin shigar nn ki xo sch plss" dan tabe baki tayi, dai dai lkcn da wani text din nasa ya shigo wayar kuma, "ina maki magana daxu a lab shine kika yi ignoring dina koh?" Reply ta mayar masa kmr hka, "ae nayi xaton da 'yan matan nn naka kke shi yasa," bae mata reply ba ta yi tsaki ta mayar da wayarta jakarta, Maryam da a tunaninta tun tambayar da tayi ma Afeefah daxu ne yasa ta daure fuska tace "me xa ki ci?" Afeefah ta girgixa kai tace "A'a na koshi ni" ko rufe baki bata yi ba Dr Sharif ya karaso cafeterian yan matan da tace yana ma mgna a lab daxun na biye da shi a baya, kujera ya ja ya xauna gefen Maryam yace "Ya exams Maryam?" Maryam ta kirkiri murmushi tace "Alhmdllh," yace "Ma'sha Allah, wishing u ol success, no carry over in'sha Allah" murmushi kawae Maryam tayi tace "Ameen" yan matan guda biyu dama duk sun xauna, ya juya yana kallon su yace "wani drink xa a kawo maku?" Duk suka ce fanta, Afeefah dae sae Satan kallonsu take tana yin kmr tana danna wayarta don yan matan ba karamin haduwa suka yi ba, fanta hudu yasa aka kawo na roba da snacks ya mika ma matan biyu ko wanne daddaya snn ya ba Maryam ma, Afeefah kuma ya ajiye mata gabanta, dauka tayi da sauri ta mayar masa ba tare da ta kallesa ba tace "Thanks bna jin yunwa" murmushi yyi ya bude shi ya fara sha, fira kawae yake da 'yan matan dake ta basa lbri, Afeefah ta Mike ta saka wayarta a jaka ta xuge snn ta gyara blck veil din kanta don har lkcn lab coat na jikinta tana kallon Maryam tace "sae mun yi waya" tana kai wa nn ta fice daga cafeterian yan matan suka bi ta da kallo, ta nufi inda ta saba xama ta jira su jiddah, bayan minti biyu da fitan ta Dr Sharif ya mike yana kallon yan matan da Maryam yace "excuse me, xan dan yi makin phone call" ya fice daga cafeterian ya nufi inda yasan xai ganta, xaune ya sameta tana danna wayarta kamshin turarensa kadae yyi announcin mata presence dinsa a gun, "Zainab!" Juyawa tayi tana kallonsa, ya xauna dan nesa da ita yace "me na maki kike fushi?" Hawaye ne ya taru idonta ta ki cewa komae sae jujjuya wayar hannunta take, yyi shiru yana kallonta, mota ne yyi parkin dan nesa da inda suke xaune, Afeefah ta kafa ma motar ido ganin kmr motar ya Aliyu, to amma ae bae dawo ba, wayarta ne ya fara ring a take, taga Aliyun ne ke kiranta, ta daga yace "Am in ur sch Zainab," wara ido tayi tace "Da gske yayanmu ka dawo ne" inda yyi parkin kawae ya gaya mata, ta juya tana kallon Dr Sharif tace "kaga motar yayanmu na Lagos ne can, he came to pick me," Dr Sharif yace "OK in je mu gaisa?" Shiru ta dan yi sae kuma tace "to" mikewa tayi ta nufi motar gabanta na faduwa Dr Sharif ya bi bayanta.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:10 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
33.....
Kallonsu kawae Ya Aliyu yake har suka karaso gun motar, Afeefah da a da idan yayansu ya dawo koma gaban waye xata iya rungumesa cike da farin ciki amma ranan sae ta kasa hkn sbda Dr Sharif, murmushi kawae take tana wasa da yatsunta tace "yayanmu shine baka gaya min yau xaka dawo ba koh?" Bae tanka ta ba sae kallon Dr Sharif da yake, Dr Sharif ya karasa gabansa ya basa hannu hade da masa sallama yana kallonsa shi ma, kin karba Aliyu yyi sae bayan kusan second biyar snn ya kirkiri murmushi ya mika masa nasa suka yi musabiha, Dr Sharif ya mayar masa da murmushin yace "Dr Aliyu Sharif," Bayan second kusan uku bbu yabo bbu fallasa Aliyu yace "Brrstr Aliyu Mahmoud" Dr Sharif yace "Nyc meeting yhu name same," ya Aliyu yace "Nyc meeting yhu too" juyawa yyi xae shiga motarsa Afeefah tace "yayanmu xa ka wuce ne" ba tare da ya kalleta ba yace "yea, sauri nake sae kin dawo." Murmushi tayi ta daga masa hannu alamar bye bye, bae ko kalli inda take ba ya ja motarsa ya bar wajen. Afeefah ta juya tana kallon Dr Sharif, ya dan yi murmushi ya koma inda suke xaune ya xauna ya fiddo wayarsa yana dannawa, ta bi bayansa ita ma ta xauna bayan minti daya ya juya yana kallonta yace "ya kuke da yayan nn naki Zainab" ta dan wara ido tace "Sau nawa xa ka tambayeni Sir nace maka babanmu daya fa," ya girgixa mata kai yace "Cousin din ki dae" xaro ido tayi tace "ka tambayi su Anty Jiddah mana, baka ji surname dinsa ba, Aliyu Mahmoud just like mine wllh yayanmu ne" gyada mata kai yyi kawae bae ce komai ba, ita ma bata kuma cewa komai ba, har bayan minti biyar snn ya kalleta yace "wat are yhu planning for the holiday?" Afeefah ta wara ido tace "a kd nake holiday dina ko Lagos, I knw I might b travelling to kaduna or Lagos tomorrow or next." Sae kuma tayi saurin cewa "A'a na ma san kd xan tafi, tunda yayanmu ya dawo" Yace "kuna da yan uwa a Kaduna ne?" Tace "ehh" yace "a wani unguwa" tace "unguwar rimi" yace "dukkanku ku ke tafiya?" Ta girgixa masa kai tace "A'a ni kadae nake xuwa, lkcn muna secondary sch idan mun yi long holiday shine muke tafiya da su anty jiddah idan sun yi kwana biyu sae su wuce ni su bar ni" Dr Sharif yace "OK, a lgs fa?" Tace "gun yayanmu nake xuwa holiday shine ke tafiya da ni" yace "yana da mata ne?" Girgixa kai tayi tace "A'a bae yi aure ba" shiru yyi bae kuma cewa komae ba, mikewa tayi tace "am goin home sir" bae tanka ta ba har sae da ta fara tafiya yace "shud I drop yhu?" Girgixa masa kai tayi da sauri tace "yayanmu xae min fada ka ga ya dawo, nd beside ka tafi gun yan matan ka kawae bna so" ta fadi hka tare da turo baki ta fara tafiya da sauri, murmushi yyi ya mike ya bi bayanta yace "Zainab!" Ba tare da ta kallesa ba tana ci gaba da tafiyarta tace "um" yace "wa yace maki yan mata na ne,?" Tace "ae na sani ne, gashi yau baka ko kalli practical exam dina ba, ka wani tafi wajensu kuna ta hira don su sun gama exams dinsu" murmushi kawae yake yace "ni ba 'yan mata na bne, kannin abokina ne" bata kuma cewa komae ba sae tafiyarta take da sauri, yace "Zainab" kmr xata yi kuka tace "Sir ni fa sauri nake ina son in je in ga me yayanmu ya kawo min" kuma kiran sunanta yyi a hnkli, hkn yasa ta tsaya amma bata juyo ba har ya iso gabanta ya tsaya yana kallonta yace "nace ba 'yan mata na bne su" kin cewa komae tayi ta sunkuyar da kanta da sauri don manyan idanuwansa ya xuba mata, ganin ynda students ke kallonsu, yasa a hnkli tace "Sir ka bar ni in wuce kaga fa kallonmu ake" juyawa taga yyi ya shiga tafiya, ta bi bayansa, har suka fita main gate bae ce Mata komae ba ita ma hka, a dai daita ya tsayar mata, ya fadi inda xata snn yana kallonta yace "shiga," ba musu ta shiga, ya ciro dari biyar ya mika ma mai adai daitan, ta wara ido tace "Sir kalli fa ina da kudi wllh" hararanta yyi ta rufe fuska da sauri, sae kuma ta bude tana kallonsa, sauke dara daran idonsa yyi daga kallonta da yake, a hnkli tace "ngd sir," yyi mata murmushi ta mayar masa tare da daga masa hannu tana masa bye bye shi dae beauty point dinta kawae yake kallo har mai a dai daita ya bar wajen.
Sha biyu dai dai Afeefah ta shiga gida, bbu kowa falon hkn yasa ta haura sama ta nufi dakin ya Aliyu, kwance ta samesa yyi rub da ciki idonsa a lumshe kmr me bacci ta dawo saitin fuskarsa ta sakar masa kara, bude ido yyi ta saka dariya tana kallonsa, ya mike xaune yana kallonta ya fixgota ya gaura mata wani wawan mari bata gama recover ba ya kuma kai mata wani, rikicewa tayi ta fashe da kuka ya mike tsaye ya nufi wardrobe dinsa ko ba a gaya mata ba tasan me xai dauko, ta Mike da gudu ta fice ta fada dakin Mami, Mami dake goge goge a dakin ta juya da mmki tana kallonta, bayanta ta labe ta dinga rusa kuka tana kiran Abbanta, Aliyu ya shigo dakin rike da belt, Mami ta fixgota daga bayanta ta jefar da ita nn tsakiyar dakin tace "fita ki ban waje ku je can ku karata ae shi ne me daure maki kugu a gidan nn, don yau ta bace maku sae ki shigo min daki munafuka" da gudu Afeefah ta Mike ta kuma komawa bayan Mami, Mami ta kuma fixgota ta wurgar, Aliyu ya cafketa ya fice daga dakin, Mami ta ja tsaki tace "munafukae kawae," kuka ssae Afeefah take tana ba ya Aliyu hkuri bae ko kalleta ba ya shiga bedroom dinsa da ita ya kulle, fuskar nn tasa a daure yace "waye wnn mutumin" cikin rawan murya tace "wayyo nima bn san sa ba yayanmu" tsula mata belt din yyi a kafafuwanta ta doka tsale hade da tsala ihu murya na rawa tace "tsaya tsaya yayanmu xan gaya maka wllh" a nutse yace "ina jin ki" jikinta na rawa tace "wani mutumi nee" tsula mata belt ya kuma yi ta kuma fasa ihu tace "wllh lecturan mu ne yayanmu," ya Aliyu yace "lecturer???" Ta fashe da kuka a tsorace tace "Wayyo yayanmu kaga ni bna kulasa kawae ya gan ni ne xan je gurin ka, kawata yake nema sae yake tambayata ko na ganta shine sae ga ka, yayanmu bae sanni ba nima....." Rasa abun cewa tayi kame kamen ma ta kasa, sae rawa jikinta yake tana hawaye shi ko ya kafa mata idonsa da ya kada fuskar nn tasa a daure, a hnkli ta sulale kasa tana kuka tace "don Allah don Annabi yayanmu kayi hkuri ni bni nace yaje gurin ka baaa, ni bani..." Kuka ne ya ci karfinta, ya dauke kai yyi wurgi da belt din hannunsa ya koma can karshen gado ya xauna ya rike kansa, bayan minti kusan shidda ya mike ya nufi kofa ya bude yana kallonta fuskarsa a daure cikin tsawa yace "xo ki fita" mikewa tayi da sauri ta fice daga dakin yyi bangin kofar ya koma ya kwanta, Afeefah ta fada dakin Mami, ta durkushe nn kasa tana rusa kuka kmr an aikota, ko kallon inda take Mami bata yi ba, ta gaji don kanta tayi shiru tana sauke ajiyar xuciya, sae a snn Mami tace "idan kin ga dama ki tashi ki tafi kiyi sllh snn ki hada kayan ki don gobe Adnaan xai kai ki Kaduna" mikewa tayi a sanyaye tana hawaye ta fita daga dakin ta nufi dakinsu don yin abinda Mami ta sa ta, sllh ta fara yi snn ta shiga shirya kayanta, tana cikin hada kayan tana hawaye su Jiddah suka shigo, da mmki sadiya tace "wa ya doke ki Afeefah, me ya faru" kin ce masu komae tayi, jiddah ta fita ta samu Mami sadiya ta bi bayanta suka tambayi Mami me ya samu Afeefah, Mami ta tabe baki tace "ita da Aliyu" xaro ido duk suka yi suka ce ya dawo ne, Mami tace "ya dawo daxu" sum sum suka fice suka koma dakinsu. Da yamma Afeefah na kwance wayarta ya soma ring a hnkli ta jawo wayar tana kallon mae kiranta ta ga Dr Sharif ne, ajiye wayar tayi a sanyaye ta juya kanta, ganin har ya katse ya kuma bugowa yasa ta kasa kin dagawa kuma, hawaye cike idonta ta dauki wayar tana kallo, ganin ya kusa katsewa yasa ta daga kiran a sanyaye tayi shiru, bude kofar dakin aka yi ta daga Kai da sauri taga ya Aliyu ne.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:11 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
34.....
Karasowa cikin dakin Aliyu yyi yana kallonta, Afeefah tuni wayar hannunta ya sulale kan gado ta jawo pillow da sauri ta rufe ganin bae lura ba, tsaye yyi bakin gadon yana kallonta taki dago kanta, yace "Zainab!" Da kyar ta iya bude baki a hnkli ba tare da ta kallesa ba tace "Na'am" xaunawa yyi gefen gadon yace "Ki gaya min meyasa ke kadae ce baki jin mgna ta a gidan nn" Shiru tayi bata komae ba, a tsawace yace "Zainab!" Dago kanta tayi tana kallonsa da idonta da yyi ja, lkci daya hawaye ya cika idonta a hnkli tace "kayi hkuri yayanmu baxan kara ba" rungumeta yyi yace "Sau nawa kike making min wnn promise din kina break din sa Zainab?" Cikin muryar kuka tace "Na daina yayanmu" dago kanta yyi murya can kasa yace "promise?" Kai ta gyada masa tana hawaye, mikewa yyi ya kama hannunta suka fita daga dakin ya nufi nasa da ita. Kwata kwata Afeefah bata saki jiki da shi kmr ynda ta Saba ba ranan, duk sae ta ji ta a takure abinda bae taba faruwa da ita ba suna tare da Ya Aliyu, tsarabar da ya yo mata ma bata wani nuna farin ciki kmr ynda take yi da ba, kawae dae tana xaune dakin ne ta kafa ma plasman dake ta aiki ido, shi kuma yana danna laptop dinsa, gaba daya hnklinta na kan wayarta da ta baro a daki duk ta kagu ta fita, ta rasa dalilin da yasa ta damu da kiran Dr Sharif hka, Sumayya ce tayi sallama ta shigo dakin tana kallon ya Aliyu tace "yayanmu wae Mami tace in kira Afeefah" ba karamin farin ciki Afeefah tayi ba don sae da ta sauke ajiyar xuciya, Mikewa tayi tana kallon ya Aliyu tace "yayanmu na tafi Mami na kirana" kai kawae ya gyada mata ta dauki ledan tsarabar da ya bata ta fita ta nufi dakin Mami, kasan dakin ta xauna tana kallon Mamin tace "gani Mami" Mami tace "kin gama hada kayan naki?" Afeefah ta gyada Mata kai tace "na gama" Mami tace "je kiyi ma Abbanku sallama ynxu, gobe da sassafe Adnaan xae tafi kd sae ki bisa kawae" mikewa Afeefah tayi ta fita ta nufi dakin Abba, yana xaune falonsa yana kallon news, ta xauna kasa, yace "ya aka yi Zainab, yau ba ki yi bacci da wuri ba knn" tayi murmushi tace "eh bnyi ba Abba, dama Mami ce tace in xo in gaya maka gobe xan tafi kd" shiru Abba yyi yana kallonta can yace "toh shknn Allah kai mu, tafi ki kira min ita" mikewa Afeefah tayi ta fita daga falon ta koma dakin Mami tace "Mami Abba yace in kira ki" Mami tace "to jera min kayan nn kafin in dawo" Mami na Kai wa nn ta fita ta nufi dakin mai gidan nata, Kallonta kawae Abba yake har ta xauna snn yace "ynxu dae nuna min kike kin fini iko da Zainab a gidan nn koh Zuwaira?" Mami ta kallesa da mmki tace "kmr ya knn?" Abba yace "wato ke a ganin ki ke ya kamata ki dinga yanke wasu hukucin a kanta knn don Kinga ina maki shiru koh?" Mami tace "don nace xata kaduna shine nayi laifi Alhaji?" Abba yace "sae ana gobe xata tafi ya kamata a gaya min? kuma ma wae sae ki aiko min ita tsabar ki gwada min kin fi ni iko da ita ko me" Mami tace "Allah baka hkuri, kuma don naga Adnaan xae tafi kadunan ne gobe yasa nace kawae ya tafi da ita da su Jiddah, kuma kasan da sassafe yake tafiyarsa ba kmr Aliyu ba." Abba yace "to baxa su yi tafiyar sassafen da shi ba, ae Ali na nn da yamma sae ya Kai su" Mami bata ce komae ba, ya Mike ya shiga dakinsa ya dauko dubu 50 ya mika ma Mami yace "gashi kiyi Masu siyayyar da ya kamata" Mami ta sa hannu ta karba tace "Allah kara budi" snn ta mike ta fita daga dakin. Afeefah na gama gyara ma Mami kayan da ta sa ta ta tafi dakinsu, Jiddah kadae ce tayi bacci, Sadiya kuma na danna wayarta, kan gadonta ta nufa da sauri ta daga pillow ta dauki wayarta ta ga Dr sharif bae kuma kiranta ba, juyawa Afeefah tayi taga Sadiya ba kallonta take ba, kmr munafuka ta shige bayi da wayar, dailing number tayi, yana fara ringing ga katse ya kirata, "Baki yi bacci ba?" Kunya ne ya kamata don ko duba Karfe nawa bata yi ba, da sauri tace "ehh naga mis cal ne" Dr Sharif yace "na kira kin dauka kuma kika yi shiru" tace "uhm yayanmu ne ya kirani" Dr Sharif yace "OK, ya su mama?" A hnkli tace "suna lfya" yace "me kike yi har ynxu ba ki kwanta ba" tace "na hada kayana ne, gobe ya Adnaan xae tafi da ni Kaduna" yace "Really?" Kai ta gyada masa kmr yana ganinta, yace "Ashe xan yi missin crying student dina" murmushi Afeefah tayi murya can kasa tace "ae xan dawo kafin a kare hutu" a hnkli yace "Shknn, journey mercy Dear" shiru tayi jin abinda ya kirata da, "Are yhu there?" Ya tambayeta jin shirun, Da sauri tace "um na ngdd" yace "welcm, sleep sweet!" murmushi tayi ya katse wayar, ta fito daga bayin a sanyaye.
Washegari misalin Karfe goma Mami tasa Aliyu ya kai ta kasuwa don yi ma su Afeefah siyayyan tsaraban da xa su tafi da kaduna. Afeefah na xaune dinnin tana breakfast don tashinta knn tunda tasan tafiyar sae da yamma, Jiddah ta sakko ta mika mata wayarta tace "Ynxu dae tsakanin ki da Allah soyayya kuke da Dr Sharif din nn ko Afeefah" Afeefah ta hade rae ta karbi wayarta tace "Kinga Anty Jiddah bana so, kawae don ya kirani mu gaisa shine xa ki ce soyayya muke ni bna so" kmr xata yi kuka ta kare mgnr, dariya Jiddah take ta bar wajen da sauri kafin ta fara mata kuka, Afeefah ta daga kiran ta kara a kunne, muryarta na rawa ta gaishesa bayan tayi masa sallama, "Me aka maki?" Tambayar da yyi mata knn jin muryarta, a hnkli tace "Su anty jiddah ke neman tsokanata" yyi murmushi yace "to kiyi hkuri" shiru tayi bata ce komae ba, yace "kin fasa tafiyar yau ne" girgixa masa kai tayi tace "Abbanmu ne yace mu bari da yamma yayanmu ya Kai mu" yace "OK Allah kai mu" a hnkli tace "Ameen" yace "ltr" shiru tayi har ya katse wayar snn ta ajiye ta ci gaba da shan tean ta a hnkli. Da yamma misalin Karfe uku Afeefah ta gama shirinta da su Anty jiddah da Sadiya don tare xa su tafi amma su Washegari xa su dawo kano, Aliyu da kansa ya karbi jakar kayan Afeefah ya kai bayan mota, ita kuma ta haura sama da gudu ta shige dakinsu, Dr Sharif ta shiga kira tana kallon bakin kofar dakin a tsorace, yana fara ring ya katse ya kirata, kmr munafuka tace "sir dama em ina son in gaya maka ynxu xa mu tafi" murmushi yyi yace "ko in xo in raka ku?" Xaro ido tayi da sauri tace "A'a" yace "To Allah tsare hanya Zainab" a hnkli tace "Ameen ngd" Addu'o'in da xata karanta ya shiga tuna mata, ji tayi ya Aliyu na kiranta da sauri tace "toh toh ngdd sir, byee" da sauri ta katse wayar ta boye cikin hijab dinta jin har ya shigo dakin harara ya galla mata yace "ba ki ji ina kiran ki ne?" kmr xata yi kuka tace "yayanmu ina cikin bayi ne fa" ficewa yyi daga dakin ta bi bayansa, Mami taje tayi ma sallama snn ta fita don su Jiddah har sun shiga mota, gaba ta xauna as usual, Mami ta fito ta masu addu'ar Allah tsare hanya snn ya Aliyu ya ja motar suka bar gidan. Karfe Shidda da yan mintuna suka shigo kaduna, Afeefah ta juya ta kalli ya Aliyu jin wayarta na vibrate a hijab, ya lura da hkn yace "ya aka yi princess?" Murmushi ta kirkira tace "Um um ba komae" bakwae saura suka isa unguwar rimi tsabar traffic din kd, horn Aliyu yyi mai gadi ya bude gate, kusan a tare suka shiga makeken gidan da wata mota dake bayansu, ya Aliyu yyi parkin a parkin lot, Afeefah ce ta fara fitowa dae dae lkcn da mutumin cikin motar ya fito bayan shi ma ya gama parkin, wara ido tayi ta nufesa da gudu ta rungumesa tace "Ya Ma'aruf" rungumeta yyi shima yace "waow Zainab ku ne dama da magrib" Su Jiddah suka karaso suka gaishesa suna murmushi su ma, Aliyu kam kin fitowa daga motar yyi sae kallon Afeefah da har lkcn tana jikin Ma'aruf yake ta madubi fuskar nn tasa a daure. Ma'aruf yace "Driver ne ya kawo ku?" Afeefah tace "A'a yayanmu ne!" Sae a snn Aliyu ya fito yana kirkiran murmushi ya nufi inda suke ya basa hannu suka gaisa. Cikin gidan suka nufa gaba daya Afeefah na ta jero ma Ma'aruf tambayoyi, "to ya Ma'aruf ynxu xaka iya shiga da ni gurin da kuke xama idan kuna tuka jirgin in gani?" Dariya yyi ya lakaci hancinta yace "ke dae ba kya girma yarinyar nn koh?" Turo baki tayi xata yi mgna taga wani mummunan kallon da ya Aliyu ke mata, tuni ta hadiye abinda xata ce ta shiga wasa da yatsunta har suka shigo falon gidan. Hajiya Khadija mahaifiyar Ma'aruf ce ta sakko falon da mmki tana kallonsu tace "dama ku ne da magariban nn Aliyu" murmushi Aliyu yyi yace "wllh kuwa Ammi," mikewa Afeefah tayi da gudu ta rungumeta. Hajiya khadija tayi dariya tace "ke dae bakya girma ko Zainab, an xo hutu knn" murmushi Afeefah tayi ta rufe idonta, Hajiya khadija ta karaso cikin falon ta xauna da fara'arta ta amsa gaisuwar Su Jiddah, tana kallon Aliyu tace "barrister Ali knn, ina su Mami?" Yace "suna nn lfya Ammi," tace "kai baka xuwa sae ka kawo Zainab hutu koh?" Dariya yyi yana shafa kansa don ya ma rasa me xae ce ya kare kansa, mikewa Ma'aruf yyi yana kallon Afeefah yace "mu je ki ban lbrin Buk, ki kuma gaya min gskya samarin ki nawa?" Dariya tayi ta mike ta bi bayansa, Aliyu ya bi ta da kallo lkci daya murmushin da yake ma Ammi ya bace daga fuskarsa.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:11 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
35....
Juyawa Aliyu yyi yana kallon Jiddah yace "tafi ki ce ma Zainab wa xae fito mata da jakarta a mota" mikewa Jiddah tayi, Ammi tace "Haba ko ni ba sae in fita in shigo mata da su ba, rabu da ita ke" murmushi jiddah tayi ta koma ta xauna, Aliyu ya dauke kai bae ce komae ba, 'yan gidan gaba daya suka sauko yi ma ya Aliyu sannu da xuwa, kawae kirkiran murmushi yake yana amsa masu, daga karshe ya Mike yace xae yi alwala ya nufi sama, dakin Ma'aruf ya shiga ya samesa xaune da Afeefah yana nuna mata inda yake xama idan yana tuka jirgi kmr ynda ya bukaci ya nuna mata, Aliyu ne ya shigo dakin ba tare da ya kallesu ba ya nufi bathroom, Ko da ya fito hararan Afeefah kawae yake amma bata ma san yana yi ba, sae cewa take "yayanmu xo ka ga ynda gaban jirgi yake, xo ka ga" jin bae ce komae ba yasa ta juya tana kallonsa wani harara ya galla mata ba shiri tayi tsit, Ma'aruf yace "ae ya fi ki sanin ynda gaban jirgin yake, kinyi xaton kowa bakauye ne kmr ke?" Murmushi ta kirkira bata ce komae ba ta mike, yace "A'a har kin gama kallon?" Tace "um sllh xanyi" yace "to je kiyi ki dawo don baki ba lbrin samarin ki ba" murmushi kawae tayi ta juya ta nufi kofa, kusan a tare suka fita da Aliyu, sae da ya kullo kofar Ma'aruf, snn ya fixgota ya cire hijab din jikinta ya kama kunnenta ya murda fuskar nn tasa a daure snn yyi mata wani wawan rankwashi murya can kasa yace "kar ki kama kanki ki ga" hawaye ne cike idonta tana shafa inda ya rankwasheta yyi kwafa ya sauka kasa, tana hawaye ta shiga dakin yan matan gidan. Afeefah na xaune kan darduma su ilham da Aneesah suka shigo tare da su Anty jiddah, rungumeta suka yi cike da jin ddin xuwanta don ba karamin sabawa tayi da 'yan uwan nata ba duk da sun girme mata duka, bude kofar dakin aka yi ya Salim kanin Ma'aruf ya shigo yace "iyye ashe cry cry ce a gidan namu yau shi yasa garin naga da hadari hadari " dariya Afeefah tayi tace "ni bna kuka ynxu ae" yyi dariyar shima yace "sae dae idan ba Zainab din da muka sani bace Mae ihu da birgima tana kiran Mami" da sauri ya fice daga dakin yana dariya su Jiddah da ilham na taya su, hade rae Afeefah tayi hkn yasa duk suka soma bata hkuri sae dae basu fasa dariyar ba, mikewa tayi ta dai dai lkcn da wayar hannunta ya soma vibrate, wara ido tayi ta fice daga dakin da sauri ta shiga dakin Anty Jamila da sauri ta rufe kofar ta daga kiran kafin ya katse, shiru tayi har sae da ya kira sunanta, sunkuyar da kai tayi ta gaishesa, yace "Kun isa lfya?" Gyada masa kai tayi tace "ehh tun daxu" yace "ya mutanen gidan?" Tace "duk suna lfya" yace "idan kin huta xan kira ki ki ban lbri" murmushi tayi tace "toh byee" tana kkrin katse wayar aka bude dakin Anty jamila ta shigo tana rike da hannun ya Aliyu wae sae fa ya ga abinda xata nuna masa, boye wayar tayi da sauri amma tuni ya gani, Jamila tace "A'a ashe kina nn Zainab sarkin kuka" yake Zainab tayi ta rungumeta don basu hadu ba, Jamila tace "ya karatun Zainab" tace "lfya Anty" Aliyu yace "nuna min abinda xaki nuna min jamila xan tafi masallaci its almost tym 4 isha" jamila tace "project ne wllh, bari idan ka dawo daga mosque" yyi murmushi yace "shine xa ki addabeni hka" tayi dariya tace "ehh mana manyan lauyoyi mu kuma yara" dariya yyi ya fice. Dakin Jamila Zainab tayi sllh, tana xaune kan darduma bayan ta idar ya Aliyu ya shigo dakin, kallonsa take har ya karaso inda take ya xauna gefen gado yana kallonta yace "ina wayar ki?" Ba karamin tsoro ne ya bayyana fuskarta ba kmr xata yi kuka tace "Yayanmu," daure fuska yyi yace "ki bani nace" daukan wayar tayi tace "tsaya toh yayanmu" yana kallonta tana ta danne dannenta, bae dae ce komae ba, tsaf sae da ta goge text din Dr Sharif da ma nmbrsa gaba daya a wayar snn kmr munafuka ta mika masa, karban wayar yyi ya kashe ya bude ya cire battery din snn ya ciro sim dinta tana ji tana gani ya 6alla sim din ya wurgar nn gabanta, xaro ido tayi tana kallonsa, ya mike ya jefa wayar kan gado snn ya fice daga dakin, kuka ta fashe da ssae kmr an aikota ta dinga rusa kuka tana kallon sim din, kmr warce ta tuna abu ta mike da sauri har tana tuntube ta fice daga dakin, dakin Ma'aruf ta nufa da gudu tunawa da tayi ta kira Dr Sharif daxu a wayarsa bae shiga ba. Kan gado ta samu wayar ta dauka da sauri taga bude taga nmbr kalle kallen inda xata ga pen da paper take daga karshe ta nufi gaban madubinsa ta bude taga pen da jotter da sauri ta dauka ta kwafi nmbr Dr Sharif snn tayi murmushi ta ajiye masa wayar ta fice daga dakin.
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:11 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
36__37
Afeefah na kwance daki tun fitowarta daga dakin Ma'aruf ita a dole tana fushi da Ya Aliyu sae kumbure kumbure take, tura kofar dakin aka yi Anty Jamila ta shigo tace "Zainab sakko ki ci abinci ana jiran ki" bata yi musu ba ta sauko daga kan gadon ta bi bayanta suka sauka kasa, ya Aliyu na xaune falo da Ammi da ya Saleem, Afeefah ta hade rae ta nufi dinnin, ta debi abincinta don su jiddah sun diba nasu, ilham tace "wnn dan abincin xae isheki Zainab?" Ba tare da Afeefah ta kalleta ba tace "ehh xae min" Anty jamila ta kalli Aneesah tace "ke kara mata me wnn dan abincin xae mata" da sauri Afeefah tace "wllh Anty ni ya isheni" kyaleta duk suka yi suka shiga cin abincinsu, da ke kadan ta xuba tuni ta cinye ta mike ta bar dinnin din, xata haura sama Ammi tace "har kin gama Zainab" tace "ehh na gama" dakin su Aneesah ta nufa ta shiga bayi don yin wanka, ko da ta fito kayan baccin ta ta fiddo a jaka tasa snn ta sa Hijab tayi kwanciyarta, balla sim dinta da ya Aliyu yyi ne ya fado mata nn da nn hawaye ya cika idonta taji wani mugun haushin sa kawae take ji ynxu, Ammi ce ta shigo dakin tace "ke baxa ki sauka falo kiyi kallo ba Afeefah," Afeefah ta ce "Ammi ni bna son kallon" Ammi tace "toh shknn, amma kar kiyi bacci sae kun gaisa da Baffan ki" Afeefah tace "toh" snn Ammi ta fita daga dakin, ko minti biyar Ammi bata yi da fita ba Ya Aliyu ya shigo dakin, rufe ido tayi da sauri kmr me bacci, ya karaso kan gadon ya xauna yana kallonta yace "Zainab!" Kin juyowa tayi bare ya sa ran idonta biyu, xagawa yyi ta daya side din yana kallon fuskarta ya kuma kiranta, nn ma taki amsawa, murmushi yyi don yasan idonta biyu sarae, ya mike ya fice daga dakin. Murguda baki tayi ta kuma tura kanta cikin pillow cike da jin haushin sa, Karfe tara da rabi Ilham da Jiddah suka shigo dakin suka ce Baffa na kiranta, mikewa tayi ta bi bayansu suka nufi falon baffa, murmushi yyi ganinta, ta xauna gefensa ita ma tana murmushin tace "Sannu da dawowa baffa" ya shafa kanta yace "yauwa mamata, ashe kun xo, ina su Abbanku da Mami," tace "duk suna lfya, sun ce in gaisheka" yace "Madalla, mun yi waya dasu daxu ma, ya makaranta ynxu kin xama 'yar jami'a koh" dariya tayi ta sunkuyar da kanta, baffa ya kalli Jiddah yace "ya baku xo min da Fadila ba Hauwa" jiddah tace "ba su yi hutu bne shi yasa" yace "Allah sarki, Adnaan na nn abunsa koh?" Jiddah tace "yana nn baffa" sun dde suna hira daga bisanni suka yi masa sae da safe dae dae lkcn da Ma'aruf ya shigo falon don yi ma Abban nasa sae da safe shi ma, Afeefah na shirin kwanciya Ma'aruf ya shigo ya xauna gefenta yace "gashi har xan tafi baki bni lbrin samarin ki ba koh?" Afeefah ta wara ido tace "ina xa ka Ya Ma'aruf?" Dariya su Ilham suka kyalkyale da suka ce "gidan sa mana" Afeefah tace "ohh na manta" dariya yyi yace "xa ki xo ki min sati koh?" Ta gyada masa kai tace "ehh xan xo yaya" yace "yawwa Kanwata" duk suka yi masa sae da safe snn ya fita daga dakin, Ammi ta shigo tace "Zainab taso ki kwanta bedroom dina" ba musu ta mike ta bi bayan Ammi.
Washegari da safe misalin Karfe goma su Jiddah suka fara shirin komawa kano, ya Aliyu ne ya shigo dakin da sallama, Afeefah da ke xaune gaban madubi tana shafe shafe ta hade rae tare da turo bakinta, gunta ya nufa yana kallonta yace "ina kwana Zainab?" Sunkuyar da kai tayi da sauri tace "yayanmu ni bn ganka ba, ina kwana," hancinta ya ja yace "dake ke makauniya ce ba" murmushin da bata yi niyya ba tayi, sae kuma a hnkli tace "ka yi hkuri" juyawa yyi yana kallonsu Jiddah yace "ina jiran ku a falo" har suka tashi tafiya Afeefah kin fita tayi har sae da Ammi tace "Zainab baxa ki je ku yi sallama da yayyin ki ba?" Mikewa tayi ba don ta so ba ta fita, kanta a kasa ta isa motar ya Aliyu ta daga ma su jiddah hannu snn ta nufi driver seat inda Aliyu yake ta dago kai a hnkli tace "Yayanmu Allah ya tsare hanya" ba tare da ya kalleta ba yace "Ameen" kmr xata yi kuka tace "yayanmu baka kalleni ba" fuskarsa a daure yace "in maki me?" Shiru tayi tana kallonsa lkci daya hawaye ya cika idonta ta juya xata bar wajen ya kamo hannunta, bbu yabo bbu fallasa yace "to me kike son in maki Zainab?" Girgixa masa kai tayi hawayen idonta ya gangaro, murmushi yyi yace "toh ngd Zainab, will miss yhu a lot" murmushi ita ma tayi, ya ciro handkerchief ya share mata hawayen fuskarta a hnkli tace "yayanmu kayi hkuri, daga yau xan fara jin mgnr ka" murmushi kawae yyi yace "Allah ya sa" har suka bar compound din bata daina daga masu hannu ba sae taji ba ddi kmr ta bi su, Aneesah ce ta ja ta tana dariya ta nufi cikin gida da ita ganin hawayen idonta. Da rana Afeefah na xaune falo suna kallo da su Anty jamila, Afeefah ta kalli ilham dake gefenta tace "Anty ilham dan ara min phone din ki don Allah, ilham tace yana sama a daki, mikewa Afeefah tayi ta nufi sama da sauri ta dauki wayar, ta fiddo nmbr Dr Sharif da ta ajiye a jakarta tayi dailin, bugu uku ya dauka tare da yin sallama, rasa abun cewa tayi kmr mara gskya tace " Sir ina yini" shiru taji yyi hkn yasa tayi saurin kallan wayar ta ga ko ya katse ne amma taga bae katse ba, sunanta ta ji ya kira ta amsa a dan kunyace, yace "me ya sami wayar ki?" Kmr xata yi kuka tace "yayanmu ne ya kwace" da dan mmki yace "sbda me?" Muryarta na rawa tace "wae don ina waya" Dr Sharif yace "uhm OK, wnn wayar waye" a hnkli tace "na sister na Ilham" yace "ok" shiru tayi bata kuma cewa komae ba, yace "ya mutan gidan" tace "duk suna lfya?" Yace "kinyi missin dina kuwa?" Shiru tayi ta kasa basa amsa, a hnkli ta ji ya kira sunanta, murya can kasa tace "Na'am" murmushi yyi ya kuma yi mata tambayar, cike da jin kunya tace "nayi!" Yace "karya kike" xaro ido tayi tace "wllh sir nayi missing dinka" yar dariya yyi yace "really kina son gani na knn!" Kunya ne ya kamata ssae, taki cewa komae, a hnkli yace "Zainab!" Tace "uhm" yace "baki son ganina knn" murya can ciki tace "ina so" yace "Toh in xo ki gan ni" rufe fuskarta tayi da pillow da sauri wae ita kunya a hnkli tace "Uhm" yace "I promise xan xo kd in gan ki dear" sallama yyi mata jin bata da niyyar cewa komae kuma, Afeefah ta ajiye wayar tana murmushi. Tun daga lkcn kullum sae sun yi waya da Dr Sharif da wayar Ilham, Aliyu kuma sau dayawa ta wayar Saleem yake kira yace ya bata, sae dae ynxu ta daina dokin kiran Aliyu kmr ynda take da, wani lkcn har pretend take tayi bacci idan aka kawo Mata wayar. Ranan da ta cika kwana uku Ya Ma'aruf ya xo da yamma, taji ddin ganinsa ssae, dakin Ammi ya nufa tana biye da shi a baya, bayan sun gaisa da Ammin tasa yace "Ammi na xo tafiya da Zainab ne tayi ma Amina kwana biyu," Ammi tace "To ae Abban ku bae sani ba" Ma'aruf yace "xan kirasa in gaya masa Ammi" Ammi tace "A'a da dae ka bari goben ka xo da safe ka samesa ka gaya masa sae ku tafi da ita" bata rae Afeefah tayi ta xamo daga kan gadon Ammi, Ammi tace "Au to Allah baki hkuri, ku tafi Ma'aruf idan ya dawo na gaya masa, amma kai ma ka kirasa," murmushi Afeefah tayi ta mike da sauri ta fice daga dakin don xuwa ta hada kayanta, jikinta ne yyi sanyi tunawa da tayi Dr Sharif yace mata gobe xae xo, can dae a xuciyarta tace to ba sae ya sameni can gidan ba, ilham ta samu da sauri dakin Anty jamila tace "Anty ilham idan Wnn da yake kirana ya kira kice bana nn amma xan kirasa" ilham tace "toh"
Karfe shidda na yamma Ma'aruf ya isa gidansa da Afeefah, bell ya danna bayan minti biyu wata kyakkyawa da baxata wuce 23 ba ta bude kofar rike da wani handsome boy a hannunta, rungumesu yyi gaba daya Afeefah ta kwalalo ido tare da dauke kanta da sauri, matar cikin sanyin murya tace "Sae ynxu Hubbi" yace "Ba nace maki xan tafi gida daga can ba, ba mu hanya bby" sae a snn Matar ta lura da Afeefah, ta bata hanya tana kallonta, Afeefah ta dukar da kai da sauri, kama taga matar take mata da warce ta sani amma ta rasa a ina, kmr munafuka tace "Ina yini Anty" "lfya lau, sannu da xuwa" matar ta amsa Mata a takaice. Har bedroom din da xata ajiye kayanta Ma'aruf ya kai ta, yace "feel at home dear" gyada masa kai kawae tayi ya fita. Tana xaune kan darduma ta idar da sllhn magrib Amina ta shigo dakin, bbu yabo bbu fallasa tace "ki sakko ki ci abinci" tana fadin hka ta juya ta fice, Afeefah tayi jigum tana da ta sanin biyo ya Ma'aruf, har ta yi sllhn isha matar bata kuma kiranta ta xo ta ci abinci ba, a xuciyarta tace to ko tana tunanin budurwarsa ce ni, Ma'aruf ne ya shigo dakin da mmki yace "Zainab ba Amina ta xo kiran ki ba, meyasa baki sakko ba" murmushi ta kirkira tace "um na koshi" ya galla mata harara yace "c'mon taso mu je ki ci abinci, ko sae na shigo na dago ki" mikewa tayi da sauri yyi dariya ya juya ta bi bayansa a sanyaye hka kawae taji ita tsoron matar ma take, da kyar take tura abincin gabanta a dinnin din tsabar irin kallon da Amina ke mata ga Ma'aruf ya isheta da surutu. Mikewa tayi daga karshe kmr xata yi kuka tace "yaya ni na koshi" yace "ba ki isa ba, Maza cinye shi" mikewa Amina tayi tana rike da yaronta ta bar dinning din ta haura sama, ya bi ta da kallo, can ya maido da dubansa ga Afeefah yace "sae fa kin cinye shi Zainab" komawa tayi a sanyaye ta xauna ta shiga tura sauran abincin, tana gama ci ya ki barinta ta haura sama, tayi da ta sanin biyosa ba kadan ba hka ya dinga mata hira daga karshe dubara ya fado mata tace ya bata wayarsa xata kira Mami da ya Aliyu snn ya bata ta haura sama da sauri ta shige dakin da ya ajiyeta ta kulle. Hawaye ta shiga yi cike da tsoron matarsa ta ci kukanta daga karshe ta shiga dialing nmbr Dr Sharif, bugu biyu ya dauka tace "Sir" yace "Zainab!" A hnkli ta gaishesa ya amsa tare da cewa ina kika je, tace "gidan uncle dinmu" yace "ok, am comin down to kaduna gobe" wara ido tayi tace "da gske Sir" yace "yea ko kar in xo" da sauri tace "ka xo" yyi murmushi yace "shknn xan xo idan Allah ya yrda, layin waye wnn" tace "uncle dina," yace "OK sae da safe" tace "Allah ya kai mu," snn ya katse wayar ta ajiye a sanyaye ta kwanta. Washegari da kyar Afeefah ta fito yin breakfast kmr ynda Ma'aruf ya umarce ta, ranan ma bata samu fuska gun Amina ba don da kyar ta amsa gaisuwar ta, sama ta koma a sanyaye ta xauna dakin da take, goma saura Ma'aruf ya shigo dakin yace "Zainab sakko ki taya Antyn ki girki a kitchen yau yayanta xae xo daga kano"
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 1:11 AM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
38......
Afeefah ta dauki hijab dinta a sanyaye ta sa don bata iya masa musu, ta bi sa suka sauka downstairs, yana gaba tana biye da shi a baya har suka iso kitchen din, Amina da ke kkrin jona blender Fadil na bayanta ta juya tana kallonsu yace "Honey ga ta xata taya ki aiki" bbu yabo bbu fallasa Amina tace "A'a taje tayi xamanta ngd" Ma'aruf yace "Haba ki bari ta taya ki mana" bnxa Amina tayi masa hkn yasa ya nuna ma Afeefah sauran tomatoes din da take wankewa tace "je ki karasa wanke mata" kai Afeefah ta gyada masa a sanyaye ta shiga kitchen din ta ci gaba da wanke mata kayan miyan, juyawa yyi ya bar kofar kitchen din ya koma sama. Afeefah na gamawa ta juya tana kallonta a hnkli tace "Anty na gama" ba tare da Amina ta kalleta ba tace "sannu" shiru Afeefah tayi tana tunanin abun yi kuma, kayan salad da cabbage da su carrots da ta gani ta nufa ta daukosu ta nufi sink don wanke su, Amina dae bata ce mata komae ba har ta gama ta yanka salad din da cabbage carrot kuma tayi grating dinsa, hka ta dinga kame kame a kitchen din Amina bata tanka ta ba har dae ta ga ba sauran aiki tayi jigum, can tace "kawo sa in rike maki shi Anty," ba musu Amina ta sauke Fadil dake bayanta ta mika mata ta karbesa ta fita daga kitchen din. Misalin sha daya Amina ta gama duk girke girken da xata yi ta bar kitchen din. Afeefah na kwance tana rungume da Fadil dake ta wasa a jikinta Amina ta bude dakin da sallama ta tsaya daga bakin kofa tace "bani shi xae ci abinci" mikewa Afeefah tayi ta kai Mata yaron ta karbe sa ta juya ta fice. Amina na fita Afeefah ta jawo wayar Ma'aruf dake gunta har lkcn, taga alamar private sim dinsa ne shiyasa bata ga an kira ba, nmbr Dr Sharif tayi dialing, yana dagawa ta gaishesa a hnkli, ya amsa yace "Kin tashi lfya Zainab?" Tace "um" yace "ina hanya fa" ta wara ido tace "da gske sir" yace "yea ko in koma" da sauri tace "A'a," yyi murmushi yace "to sae na xo" ita ma tayi murmushin tace "Allah tsare hanya" tana ajiye wayar jikinta yyi sanyi, to ya ma xata gaya ma ya Ma'aruf xata yi bako, ga matarsan nn da bata da kirki.
Mikewa Afeefah tayi daga kwancen da take jin har an tada sllhn Azahar ta nufi bayi tayi alwala ta fito, ko da ta idar da sllhn kayanta ta ciro don ita tsoron kwalliya ma take a gidan tun kayan baccin jiya ne jikinta duk da tayi wanka, ta dan yi shafe shafenta snn tasa wani gown dinta na material ta maka dogon hijab a kai ta koma ta kwanta, Amina ce ta bude kofar dakin tace "ki je ki dauki abincin ki kitchen fa" to kawae Afeefah tace mata, Amina ta rufe kofar, bayan minti talatin Amina ta kuma bude kofar dakin tace "baki sauka kin dauki abincin ba kuma" mikewa Afeefah tayi da sauri ta nufi kitchen a sanyaye, Aminan na biye da ita a baya ta nuna mata abincin nata da ta ajiye Mata kan faranti da drink da ruwa snn ta juya ta fita kitchen din. Plate Afeefah ta dauka ta bude shinkafar don ba iya cinye duka xata yi ba, ta dibi kadan ta bude miyar ta diba, kaji ta gani a daya kulan dake kan farantin ta dauki daya, coslow din ma bata diba ba ta dauki ruwa maimakon drink snn ta fita daga kitchen din ta haura sama. Kasa cin abincin tayi ta dan cakalkala ta mayar kitchen tana neman bolan xubarwa, bell din gidan aka danna sae da ta dan tsorata ta fito daga kitchen din da sauri rike da abincin don kar Amina ta gani, kallo daya Amina tayi mata ta nufi kofa tana rike da Fadil murmushi dauke fuskarta, Afeefah ta koma kitchen din kmr xata yi kuka, ita dae ta kawo kanta, da ta sani da bata fara bin ya Ma'aruf ba, Amina na bude kofar ta rungume yayanta cike da farin cikin gninsa, rankwashi Dr Sharif ya kai mata yace "kina ma da hnkli kuwa, kada ni xa kiyi" dariya ta kyalkyale da tace "kai yaya, kaga ynda ka canxa kuwa yayana, welcm big bro nah," murmushi yyi ya karbi yaron hannunta ta basa hanya ya shigo falon, Afeefah kam kasa kwakkwaran motsi tayi a kitchen din jin kmr muryar Dr Sharif take ji a falon, ga kamshin turare irin nasa da ya gauraye gidan, Amina kuwa baki har kunne ta ga yayanta da take bala'in so, Dr Sharif ya xauna yana rike da Fadil yace "ina Captain din?" Tace "wllh ya fita tun daxu yaya, amma nasan yana hanya ynxu," kitchen ta nufa da sauri sae ta ga Afeefah a tsaye, dauke kanta tayi ta dauki faranti da glass cup ta bude fridge ta fiddo drinks da ruwa ta daura kai ta fice daga kitchen din tana cewa "yaya ina momyna da fateema, meyasa ba ka xo min da teema ba" yace "suna gida, idan kina son ganinsu ae sae ki je kanon" tace "Ayya yaya dama wllh kila next wk xan tafi kanon sae ga shi kace min xaka xo" hiran yaushe gamo suka dinga yi da yayan nata don sun kusa shekara ba su hadu ba, mikewa tayi tace "bari in hado maka coffee yayana, nasan kuna tare har ynxu" murmushi yyi ta nufi kitchen, wnn karan da mmki take kallon Afeefah dake tsaye har lkcn a kitchen, a dan fusace tace "wae ke me kike yi a kitchen a tsaye ne" bata jira cewarta ba ta shiga yin abinda ya shigo da ita kitchen din, hawaye ya cika idon Afeefah, Amina na fita daga kitchen din ita ma ta fita a sanyaye tana rike da plate din abinci har lkcn, assuring kanta ta shiga yi cewar ae da Dr Sharif ne ya xo Kaduna da ya kirata tasan Mae irin muryarsa ne kawae, tana fitowa daga kitchen din suka yi ido hudu da shi, sake plate din shinkafar hannunta tayi a kidime ta juya da sauri xata koma kitchen din sae kuma ta nufi stairs da gudu kmr munafuka, ya bi ta da kallon mamaki, Amina ta mike da mugun mmki ita ma ta bi ta da kallo snn ta maido da dubanta kan shinkafar kan tiles tace "anya yarinyar nn na da lfya ma kuwa, ba da ni ba wllh" wayarta ta shiga nema don kiran Ma'aruf, murmushi kawae Dr Sharif yyi yana shafa kansa yace "wa xa ki kira?" A fusace tace "Baban Fadil xan kira mana, do ni bnsan ko tana da iskokai ba yarinyar bbu ruwana, Dubi fa abinda tayi ynxun nn" Dr Sharif da har lkcn yana murmushi yace "Uncle dinta ne mijin naki" tace "ni bn san ynda suke ba, jiya ya kawota" Dr Sharif yace "kira min ita" bata fuska Amina tayi tace "tayi maka me yaya, ka rabu da ita ina jin ba ita kadae take ba" hararanta yyi yace "nace ki tafi ki kira min ita" sama ta nufa ba don ranta ya so ba ta shiga dakin da Afeefah take, ta sameta xaune tana rusa kuka bakin ranta, mamaki ne ya cika Amina, sae abun ma ya kusa bata dariya, ta dake tace "me aka maki kike kuka?" Afeefah ta girgixa mata kai da sauri muryarta na rawa tace "gida xan wuce Anty" Amina tace "to sakko a mayar da ke" mikewa Afeefah tayi da sauri ta dauki jakar kayanta, Amina tace "A'a bar jakar xa a biyo ki dashi daga baya sakko kawae" ba musu ta bi bayanta kmr munafuka ita dae har lkcn bata yarda Dr Sharif ta gani xaune falon ba, suna shigowa falon Afeefah ta shiga rufe fuskarta da Hijab dinta ta nufi kofa da sauri, har ta kusa ba Amina dariya, Dr Sharif yace "Zainab!" Juyowa Afeefah tayi da sauri tana kallonsa har lkcn fuskarta a rufe, kuka ta saki ganin shi din ne, Amina ta shiga kallon yayanta da mmki jin ya kira sunan Afeefah, mikewa yyi ya karasa inda Afeefah take yana murmushi yace "sauke hijab din" saukewa tayi ta sunkuyar da kanta da sauri, ya tsura mata ido snn a hnkli yace "baki son ganina ne kuma" muryarta na rawa tace "ina so" Amina ta kwalalo ido da mugun mmki tana kallonsu, yace "toh share hawayen ki" a hnkli ta shiga share fuskarta yace "follow me," ba musu ta bi bayansa suka koma falon ya xauna kan kujera ita kuma ta xauna kasa gefensa har lkcn taki dago kanta, da mmki Amina tace "yaya kasanta ne dama wae?" Yace "ehh nasanta, student dita ce" Amina ta xaro ido tana kallon Afeefah, murya can kasa Dr Sharif yace "kuma budurwata! koh Zainab?" Afeefah ta rufe fuskarta da hijab da sauri ta daura kanta bisa gwiwanta, Amina ta fashe da dariya tace "kai yayana, wae da gske kke don Allah" murmushi yyi yana kallon Afeefah da ke jin kmr ta nutse wajen, yace "karya nayi Zainab?" Kin cewa komae Afeefah tayi ya sakko nn kasa gefenta ya xauna yana kallonta a hnkli yace "Zainab" murya can kasa tace "um" yace "wae ke ba budurwata bace?" Kin dago kanta tayi, yace "shknn bari in tashi in tafi since yhu re denying me" dago kanta tayi da sauri a kunyace tace "Sirr"
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 8:01 PM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
39.....
Dariya kawae Amina take tana kallonsu, Dr Sharif yyi murmushi yana kallon Afeefah yace "to gaya min me ya sa ki kuka?" Shiru tayi bata ce komae ba, ya kuma yi mata tambayar, ta daga kai a hnkli tana kallon Amina, sae kuma tayi saurin sunkuyar da kanta, kallon Aminar Dr Sharif yyi yace "ke kika sa ta kuka knn?" Da sauri Afeefah tace "A'a sir bata min komae ba" Amina ta yo waje da ido ta dawo kusa da su ta xauna tana dariya tace "wllh yaya bn mata komae ba tun jiya da ta xo ta ki sake jiki fa," Dr Sharif ya galla mata harara yace "ke din? Kin sake mata fuska ne bare ta saki jiki?" Amina ta xaro ido ta kuma ta saka dariya tace "Ayya yayana ka tambayeta wllh bn mata komae ba jiyan ma da suka xo ban jin ddi ne" hararanta kawae Dr Sharif yake, Afeefah kam murmushi tayi ta sunkuyar da kai a hnkli tace "ni bata min komae ba kawae gida nake son wucewa" Amina ta yi dariya tace "to ka dae ji, in ma na maki wani abun kiyi hkuri Anty Zainab" sae a snn Dr Sharif yyi murmushi, Afeefah ma tayi murmushin cike da jin kunya, Amina ta mike tace "bari in kawo maka abinci big bro" kallon Afeefah kawae Dr sharif yake har lkcn taki dago kanta, Amina ta dawo falon ta dire kulan abincin ta koma ta dauko sauran, da kanta ta shiga xuba masa a plate, daga kai yyi ya kalleta yace "ita ta ci ne?" Amina tace "bata wani ci na kirki ba, breakfast ma ina kula da ita bata yi na kirki ba" spoon ya dauka ya sa a abincin da Amina ta xuba masa ya dauko ya ajiye gaban Afeefah yace "oya start eating ynxu" murmushi tayi hade da girgixa masa kai tace "Um na koshi sir" hararanta yyi yace "C'mon" bata kuma yi masa musu ba, ta dauki spoon din a hnkli, Amina ta xuba masa wani tana murmushi tace "bari in baku waje sir" daukar Fadil tayi tana dariya ta haura sama. Kasa cin abincin Afeefah tayi tsabar yanda yake kallonta ga wani mugun kunyarsa da taji tana ji, murya can kasa yace "Zainab!" Ba tare da ta dago ba tace "um" yace "kunya ta kike ji ne wae?" Gyada masa kai tayi, yyi murmushi ya soma cin abincin sa, ganin taki ci ne yasa yace "to tafi sama ki je ki ci" da sauri ta mike ta dauki abincin ta nufi stairs ya bi ta da kallo. Fitowa Amina tayi jin Afeefah ta bude dakin da take ta shiga dakin tace "har kin gama cin abincin" murmushi Afeefah tayi tace "a nn xan ci" dariya tayi tace "kunyar sir din naki kike" sunkuyar da kai Afeefah tayi da sauri, Amina ta ajiye Fadil kan gado tace "ga Fadil nn toh" juyawa tayi ta fita daga dakin ta koma gun yayanta, kallo ta samesa yana yi tace "yaya ae abincin xae huce" yace "eh jira nake ya huce dama" tace "wae da gske yayana budurwar ka ce Zainab" ba tare da ya kalleta ba yace "gashi na fada gaban ki" murmushi tayi tana kallonsa don har tayi aure bata taba jin yyi maganan mace ba don cewa yake ba su ne gabansa ba, lallai Zainab tayi sa'a, jin tayi shiru yasa Dr Sharif ya daga kai yana kallonta, tayi masa murmushi tace "na taya ka murna yayana, Allah baka Zainab! don yarinya ce me hnkli daga jiya na lura da hkn ga sanin ya kamata" murmushi yyi yace "Ameen ya Allah"
Har karfe uku suna hira da yayanta ya Ma'aruf ya shigo falon, yana dariya yace "Dama ana ganin ka bokan turai, baka da kirki Haiydar ko kira bbu fisabilillah" Dr Sharif yace "ae kai naga kana kiran, ba dae mun baka mata ba dole ka mance mu" dariya Ma'aruf yyi yace "ka ji gori koh, ke Amina kira min Zainab shi ma in basa Kanwata ko xan samu sakat" dariya Amina tayi tace "to ae budurwarsa ce Zainab din" Ma'aruf yace "kai Haba a ina ya san ta? Wae da gske Dr" Mikewa Dr Sharif yyi yana murmushi yace "wnn ba Matsalar ka bace" excusing kansa yyi ya fita don amsa wayarsa, Amina tayi dariya tace "a kano ya san ta" bayani tayi ma Ma'aruf ynda suka hadu da Afeefah, Ma'aruf yyi dariya yace "to in ji kin daina kishi da ita ynxu dae koh? Don kinsan ko ina son Zainab ynxu ya xama dole in bar ma wnda ko auren ma bae taba ba sbda halaccin da yyi min" dariya Amina tayi ta kai masa duka tace "kai dear! hka nace maka ina kishi da ita" yace "ahaf sae dae idan ba Aminar da na sani bace" tayi dariya tace "uhm ae ynxu Zainab ta xama Anty"
Ko da Dr Sharif ya dawo mikewa Amina tayi ta bar masu falon ta haura sama, Ma'aruf yana kallon Dr Sharif yace "ashe dae Kanwata kke so, ya xama dole in maka halacci in sa a baka" Murmushi Dr Sharif yyi yace "Allah sa ku banin dae" Ma'aruf yace "Serious in har da aure kke son ta an gama" Dr Sharif yace "Da aure nake sonta mana" Ma'aruf yace "ka shirya auren ne ynxu?" Dr Sharif ya shafa kansa yace "Ae karatu take ynxu, it won't b fair in katse mata karatun ta" Ma'aruf yyi murmushi yace "ka manta Amina na karatu ku ka bani ita" Dr Sharif yace "hka ne but bn san ko xa ayi mata aure ynxu ba, naga yayyinta mata ma basu yi auren ba" Ma'aruf yace "kai dae ynxu kke son auren ko ba ynxu ba?" Dr Sharif yyi shiru yana kallonsa snn yace "idan xa a bani" Ma'aruf yace "kar ka damu, aurensu ilham nn da 'yan watanni ne, xan yi convincing Abba ya hada gaba daya idan har yhu re jet serious coz nasan halin ka Haiydar" Sauke ajiyar xuciya Dr Sharif yyi yace "wllh da aure nake son Zainab, amma bari in maka tambaya daya, ya ku ke da Zainab? kuma ka gaya min gskyan wani irin dangantaka ne tsakaninta da Aliyu, tace min dad dinsu daya, hka ne?"
Eeshatullah Goni๐๐
[4/18, 10:41 PM] Eeshatullah Goni: ๐ธ๐ฉ๐ป 'Ya mace kyautar Allah๐ฉ๐ป๐ธ
A true life love story
By Ashmaad
40.....
Shiru Ma'aruf yyi yana kallon Dr Shariff snn yace "Hka tace maka dad dinsu daya?" Dr Sharif ya gyada masa kai, Ma'aruf ya dan tabe baki yace "I wonder y they are still hiding things for the innocent girl, ba dad dinsu daya da Aliyu ba but don't tell her dat" kasa ce masa komae Dr Sharif yyi, can dae da kyar yace "to ya suke da shi? Nd y are they hiding it for her? Kana nufin shi ba dan gidan bne knn?" Ma'aruf yace "No! Ita ce ba 'yar gidan ba, ynxu dae mu bar xancen nn, ka bn go a head in yi ma dad maganan?" A sanyaye Dr Sharif yace "Baka gaya min ynda ku ke da ita ba" Ma'aruf yace " yar Kanin dad dina ne, her father is late" da mmki Dr Sharif yace "bn gne ba, make me understand plss, then wat is she doin in kano, mum dinta fa, kana nufin ba iyayenta bne a kano?" Ma'aruf ya sauke ajiyar xuciya yace "Ka ga da mu bar wnn xancen kawae Dr, she knw nothin about ol dis dat am sayin, infact duk gidansu bnda Aliyun da Adnaan sae yayyinta mata biyu da suka yi aure bbu wnda yasan ba yar gidan bace ita, kuma baxan so ta ji a bakina ba ko a gidana, in dae kana son Zainab da aure da gske ka kwantar da hnklin ka am there for yhu, ltr xa mu je mu samu dad am sure he will b vry happy don shi indae mace ta fito da miji aure yake mata bae jiran sae ta kare karatu kmr ynda dad dinsu Aliyu ke yi, tashi mu tafi masallaci, almost tym 4 sallat" har suka dawo daga masallaci Dr Sharif was nt him self, dama yasan ba biological brothern Afeefah bne Aliyu, ya ga alama da ddewa, Ma'aruf ya haura sama ya bar sa nn xaune yana ta sake sake, he is afraid of loosin Zainab, yasan tun daga randa ya fara sauke idonsa ya ji sonta, abinda bae taba faruwa da shi ba, da farko he was thinking tausayinta kawae yake don yaga alamar tana da rauni ga saurin hawaye, daga baya yaga ba hka bne don duk randa bae daura ido kanta a sch ba bai jin ddi, nd he is matured enuf ba sae wani ya gaya masa ya fada tarkon son Zainab ba, sauke ajiyar xuciya Dr Sharif yyi don yasan Ma'aruf will Neva let him down. Amina ce ta shigo dakin da Afeefah take ta ganta kwance tana bacci, tada ta tayi tace "lallai ma Antyn nn sae ki xo kiyi kwanciyar ki a nn kina bacci ki bar bakon ki a falo" mikewa xaune Afeefah tayi tana mitsika ido, Amina ta mata murmushi tace "to tashi ki kara shiryawa ki je ku yi hira, yace min sbda ke ma ya xo kano" Kai Afeefah ta gyada mata kawae ta juya ta fita, Afeefah ta mike ta shiga bayi, wanka ta kuma yi tayi alwala ta fito tayi la'asar, snn ta yi shafe shafenta, ta fiddo da wani riga da skirt dinta na atamfa ta sa, ba karamin kyau kayan yyi mata ba, tana kkrin sa Hijab Amina ta shigo dakin, xaro ido tayi tace "ko yar powder baxa ki shafa ba" murmushi kawae Afeefah tayi bata ce komae ba, Amina ta kama hannunta tace "xo mu je dakina ki shafa" bin bayanta Afeefah tayi suka shiga bedroom din Aminar ta xaunar da ita gaban madubinta, kwalliya ta shiga rangada mata tun Afeefah na nonnokewa sbda kunya har ta sake, light make up tayi mata, ta sa mata jan bakin da tasan xae amsheta, snn ta mata daurin dankwali ya xauna das a kanta, wae ina ma xa a iya kwatanta irin kyan da Afeefah tayi don Amina sake baki tayi tana kallonta, wane ba indiya ko balarabiya, ita kanta Afeefah sae da taji kunyar don bata taba kwalliya hka ba, hotuna Amina ta mata snn tace "to tafi kuyi hira da Sir din ki" rufe fuska Afeefah tayi da sauri cike da jin kunya, can ta dauki hijab dinta xa ta sa, Amina tace "meye hka xan gani?" Afeefah ta sunkuyar da kai tace "sa wa xan yi" Amina tace "Haba sae kace warce xata fita kofar gida, falo fa xaki xauna" karbe hijab din Amina tayi tace "yi tafiyar ki hka" Afeefah kmr xata yi kuka tace "baxan iya fita hka ba Anty" Amina ta sake baki tana kallonta can tace "to wllh baxa ki fita da hijab ba, gwara ki dauko mayafi toh" Afeefah ta marairaice tace "ban xo da mayafi ba anty" Amina tace "bari xan baki nawa," jan mayafinta mai kyau ta fiddo mata ganin atamfar na da ratsin ja ta mika mata tana murmushi tace "to ga shi ki yafa" a kunyace Afeefah ta karbi mayafin amma ta kasa yafawa don ba sabawa tayi ba, Amina ta karba tana dariya ta yafa mata shi a shoulder dinta gefe daya, snn ta dauki turare ta fesheta da shi ta fiddo mata red flat shoe dinta ta bata tace "sa kiyi tafiyar ki" a hnkli Afeefah tace "ngdd," snn ta sa ta fita daga dakin. Da kyar Afeefah ta sauko downstairs don ji take kmr ta nutse tsabar kunya, juyawa Dr Sharif yyi don ganin me sakkowa, ya kafa mata ido ko kiftawa bae yi, wani mugun sonta na fixgarsa, ta sunkuyar da kai da sauri, tana harhardewa ta karaso falon ta rakube gefen kujera kanta a kasa a hnkli tace "Sir ya hanya?" murmushi Dr Sharif yyi murya can kasa yace "Zainab!" Ba tare da ta dago kai ba tace "um" ya nuna mata gefensa yace "dawo nn" kin tashi tayi sae da ya kuma kiran sunanta snn ta mike da kyar kanta a kasa ta dawo kusa da shi ta xauna kasa, kallonta kawae yake, ta dago a hnkli tana kallonsa da dara daran idonta, ya lumshe ido yace "kinyi kyau" rufe fuskarta tayi da sauri murya can ciki tace "ngd Sir" Amina ce ta sakko ta shigo falon tace "baxa ku xaga kaduna ba yayana, da kun dan fita outing" kallon kanwartasa yyi yana murmushi yace "Yayanta xae bari in fita da ita?" Amina tace "ehh mana, bari in masa mgna" juyawa tayi ta koma sama, Dr Sharif na kallon Afeefah yace "wae mu je yawo?" Sunkuyar da kanta tayi bata ce komae ba lkci daya ya Aliyu ya fado mata hka kawae ta ji gabanta ya fadi. Amina ce ta kuma sakkowa tana murmushi tace "yayanta yace xa ku iya fita amma kar ku dde" juyawa tayi tace "ina xuwa" snn ta kuma komawa sama, ba a dau lkci ba ta dawo falon tace "Anty ki tafi yayanki na kira a sama" Afeefah tayi murmushi ta gyada mata kai alamar ta ji, farantin Drinks din dake falon Amina ta dauka ta nufi kitchen, Afeefah ta Mike a hnkli don xuwa kiran ya Ma'aruf, rasa inda xata bi da Dr Sharif baxae bita da kallo ba tayi, don wani kunya take ji idan yana kallonta, tana fara tafiya mayafin jikinta ya xame kafin ta ankara har ya kai kasa, ta xaro ido da sauri ta durkushe wajen kmr xata yi kuka tana kallonsa, Dr Sharif ya kauda kansa yana murmushi, mikewa tayi da gudu ta nufi stairs rike da mayafin a hannu bin ta da kallo yyi yana murmushi, ba a dau lkci ba Ma'aruf ya sakko Afeefah na biye da shi a baya yana kallon Dr Sharif yace "amma fa baxa ka dde min da kanwa a waje ba Dr" Dr Sharif yyi murmushi yace "In'sha Allah" makullin mota Ma'aruf ya basa yace "ga aron mota" dariya Dr Sharif yyi ya karbi makullin yace "thanks frnd" Ma'aruf yyi masu Allah kiyaye hka ma Amina suka koma sama, yana gaba tana biye da shi a baya ya nufi parkin lot, juyawa Dr Sharif yyi yana kallonta a hnkli yace "koma ki dauko hijab din ki Zainab" Afeefah ta juya ta koma cikin gidan ta ajiye mayafin ta dauki hijab dinta, Amina tayi dariya tace "lallai ma yaya" murmushi Afeefah tayi kawae ta fita ta samesa cikin mota yana jiranta.
Eeshatullah Goni๐๐
0 Comments: