Wednesday, 10 October 2018




IDAN MUTUM YANA CIKIN YIN SAHUR SAI YAJI AN KIRA SALLA YA ZAI YI?

Home IDAN MUTUM YANA CIKIN YIN SAHUR SAI YAJI AN KIRA SALLA YA ZAI YI?

_*IDAN MUTUM YANA CIKIN YIN SAHUR SAI YAJI KIRAN SALLAH YAYA ZAIYI??*_

                             *Tambaya*
Idan mutum yana cikin yin sahur, sai yaji kiran sallah yaya zaiyi?


                                    *Amsa:*
A irin wannan halin mutum zai qara sa abin da ke hannunsa ne. Domin hadisi ya tabbata daga Abu Huraira yace: Manzon Allah yace: *"Idan dayanku ya ji kiran sallah alhali qwarya tana hannunsa, kada ya ajiyeta, har sai ya biya buqatarsa."*

Amma anan sai ayi hattara, kada amayar da irin wannan dabi'a tazama al'adar kullum.

WALLAHU A'ALAM.

Gabatarwa:- Ãbûbäkår Êkâ.

Ya kai dan uwa mai Albarka ka taya mu yada wannan karatu/sako zaka samu lada mai yawa, domin yada ilimi yana da daga cikin Abubuwan da suke kusan ta bawa ga Mahalicci.
______________________________________

» Zauren 🔑 *_MIFTAHUL ILMI_* 🔑 (WhatsApp).

‎Ga ma su sha'awar shiga Zauren MIFTAHUL ILMI a whatsApp sai a turo da CIKAKKEN SUNA zuwa ga lambar mu (07036073248) ta ‎whatsApp.

Share this


Author: verified_user

0 Comments: