Friday, 8 June 2018




babban gida complete

Home babban gida complete

[4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 & *_Sumeeluv_* www.Seemaluv.wapka.me *_@Assalamu Alaikum, ina mai mik'a godiya ta agareki RUFAIDA YUSUF. Naji dad'i sosai matuk'a da yadda kika nuna soyayyarki ga JAMEESHA ' bama JAMEESHA kad'ai ba hardani, gaskiya munji dad'i sosai JAMEESHA tana godiya sosai..._* *45-46* A haka bacci yayi awon gaba dasu. *Washe gari* Da sassafe ' su Fadwa suka tashi, sai da sukayi sallah tukunna sukayi wanka ' Fadwa ce ta fara shiryawa sannan ta shiga kitchen domin had'a breakfast, Ta na cikin had'a tea ne Yaya Khaleel ya shigo . Cikin muryar rashin lafiya ' yayi mata magana, "Fadwa ' please ki had'a mun Coffee yanzu, ki kawomin d'akin...." Bai kaga k'arasawa ba ' amai ya taso mashi, cikin sauri ya k'arasa wajen sink d'in kitchen ' yaita kakarin amai. Cikin hanzari ' Fadwa ta d'ibi ruwa a cup, ta tsiyaya ruwan a tafin hannun ta, ta fara shafa mashi asaman kanshi. "Sannu Yaya Khaleel." Yawwa kawai yace ' sannan yabar kitchen d'in ya wuce d'akin shi. Nan tayi sauri ta had'a mashi Coffee d'in ba tare data k'arasa had'a masu kayan breakfast d'inba. Fadwa barin kitchen d'in tayi ' ta nufi d'akin Yaya Khaleel rik'e da cup a hannun ta, ciki ta shiga ta iske shi kwance saman gado ' rik'e da cikin shi, sannan ta sami waje ta zauna a bakin gadon. "Yaya Khaleel ' gashi na kawo." Tashi yayi ya zauna ' tukunna ya karb'a Coffee d'in ya rik'e a hannun shi. "Ki bud'e wancen drower d'in, zakiga Cimetadine ki d'auko min." Yayi mata nuni da yatsar shi ' haka yasa ta doshi wajen kai tsaye, ta d'auko maganin sannan ta dawo ta mik'a mashi. Harta juya zata wuce ya tsaida ta cewa, "Ina kuma zakije Fadwa?" Yanayin yadda yayi maganar ne ' yasa tajin tausayin shi sosai, hakan yasa ta juyo ta kalleshi tare da cewa. "Na'am?" "Baki bani ruwa ba ' zaki wuce kuma." "Bari in kawo ma." Juyawa tayi zata fita ' da niyyar wucewa kitchen, ya tsaida ita. "Ina zakije kuma? Bayan ga robar ruwa anan," Babu musu ta dawo ' ta d'auki robar ruwan ta mik'a mashi, sannan shi kuma ya b'alli maganin yasa a baku ta zuba mashi ruwan ya kora, Fadwa wani yarrrr takeji ' tsigar jikin sai tashi takeyi, don kuwa batason magani a rayuwar ta kokad'an. Yaya Khaleel ' sai a wannan lokacin ya kalli kwalliyar da ke fuskar Fadwa, a wannan lokacin ne yaji kishinta ya fara shiga cikin zuciyar shi 'Fadwa kam harta juya zata wuce yasake tsaidata, sai da ta yatsine fuska sannan ta juyo. "Dama a haka kike tafiya school d'in," Nan ta tsaya tana duba jikinta. "A'a zan sanya gele ai." "Nup! Ba dressing d'inki nake nufi ba, kwalliyar da kika cab'a nakeso ki gogeta yanzun nan." Sunkuyar da kai tayi ' tare da turo k'aramin bakin ta. "Ga tissue cen ' ki d'auka ki share wannan janbakin dake kan lips d'inki." Kallon wajen da tissue d'in yake tayi, sannan ta sake sunkuyar da kanta. "Yaya Khaleel plea..." Bata k'arasa ba ya daka mata tsawa. "Bakiji abinda nace maki bane?" Cikin tsoro ' ta d'auki tissue d'in ta zara ta goggoge bakin ta. "Na share." "Ke am not joking ' ko sokike in tashi maki?" Ta girgiza mashi kai ' sannan ta matsa gaban mirrow d'in tana gogewa, ganin yak'i goguwa ne ta gane cewa lallai 24hrs ta shafa a bakin ta ' cikin fargaba ta juyo ta kalleshi suka had'a ido. "Yaya Khaleel ' yak'i fita amma don Allah kayi hak'uri bazan sake sawa ba." Nan take ya diro daga gadon ' gami da cewa. "No ai saiya fita yau d'in nan." A hankali yakeyo kanta ' tanaja da baya, Sai da yaji ya k'ureta a bango tukunna ya kamo k'ugunta. Ganin haka yasa Fadwa tsorata sosai ' k'ok'arin k'wacewa takeyi amma ta kasa ' Yaya Khaleel kuwa k'ok'arin kissing d'inta yakeyi amma tak'i bashi had'in kai. "Ke!" Ya daka mata tsawa ' cikin tsoro ta d'ago kai ta kalleshi. "Bazaki daina wannan fizge fizgen ba?" Hawaye kawai ke tsiyaya a fuskarta. " Ya Khaleel ' kayi hak'uri don Allah, ka barni in wuce ' bazan sake sawa ba i promise." Jikinta rawa kawai yakeyi ' hakan yasashi sakin ta cikin sauri, gami da juya mata baya. "Get out!" ya fad'a cikin tsawa, Fadwa sauri tayi ta fita cikin rawar jiki ' ta koma kitchen tana maida numfashi. Sunan ta taji ankira ' haka yasa tayi saurin juyowa, don ta duba waye. "Are you Okay?" ganin Yaya Farook ne yasa tayi saurin share hawayen ta ' tare da cigaba da had'a tea d'in. "Of cause." Ta fad'a a tak'aice sannan ta cigaba da abinda takeyi. Abin ne yabawa Yaya Farook haushi ' yasashi k'arasowa kitchen d'in cikin fushi. "Bazaki fad'amin abinda ke damunki ba!" Fadwa banza tayi ta kyaleshi ' ta zuba tea d'in cikin plast, sannan ta d'auka zata wuce ya rik'eta. "Ki fad'amun abinda ke damunki mana Fadwa.!" Nan ta d'aga kai ta kalleshi ' tare da ajiyar zuciya. "Ya Farook ' ni babu abinda ke damuna, kuka kuma da kaga inayi wannan tsakani nane da wanda zan aura." Tana gama fad'in haka ta fizge hannun ta ta wuce, ba tare da ta tsaya ko inaba ta wuce parlor ' ta ajiye plast d'in, sannan ta koma d'akin su don sanarwa Ilham. Tana shiga suka cikaro da Ilham tana k'ok'arin fitowa. "Thought ko baki gama shiryawan bane," Cewar Fadwa. Juyawa Fadwa tayi suka tafi parlon a tare, suka zauna a dinning table. Zaman su keda wuya ' su Umma da Abba suka shigo parlon, sai da suka zauna sannan Fadwa da Ilham suka gaishesu. "Yawwa Fadwa idan kin tafi School ' ki nemi permission subaki hutu, don yau nakeson a fara shirye-shiryen bikin nan." To kawai Fadwa ta iya cewa ' don kuwa sai yanzu ne takejin damuwa a cikin zuciyarta. A gaban idonta Umma ta d'aga waya ta fara kiran dangi tana sanar dasu bikina ' wata kunya ce tazo mata had'e da bak'in ciki, yasa tayi zambur ta tashi tsaye. "Ilham tashi haka nan ' wallahi lokaci ya k'ure mana yau." Tashi Ilham tayi ta d'auki cups d'inda sukayi amfani dashi sannan ta zarce kitchen ita kuma Fadwa ta wuce d'aki don d'aukar handbag d'inta da gele. Su Fadwa basu wani b'ata lokaci ba suka fita driver ya d'aukesu suka bar gidan zuwa school. Bayan driver ya sauke su a school ne ' suka shige class cikin sauri, duk d'aukan su akwai lecturer a cikin. Saida suka shiga suka iske aji kowa sharholiyar shi yakeyi, tukunna suka sami waje suka zauna. "Ilham kince zaki fad'amin yadda kukayi da Abba jiya." "Hm aikedai bari kawai ' Abba cewa yayi in fad'awa Al'ameen cewa yanason ganin shi, don idan akayi bikin ki da one-week za'ayi nawa." "Toh Allah ya kaimu ' but ninaso ace tare za'a aurar damu wallahi." Wata uwar harara Ilham ta watsama Fadwa ' haka yasa Fadwa darawa kad'an, sannan tad'an bigi kafad'anta. Suka cigaba da surutun su ' kafin wani malamin ya shigo. *** *** *** *** *Around 1:54pm* Fadwa ta mik'e tsaye daga seat d'inta ganin lecturer na ciki ne yasa ta d'auki permission d'in fita. Kai tsaye ta wuce Office d'i shugaban school d'in ta sanar da ita komai, sannan akayi signing wata takarda ' aka bawa Fadwa. Koda ta fito daga Office d'in ta iske antashi duk an watse, sai Ilham ne kawai dake tsaye a k'ofar class take jiranta. Cikin sauri ta k'arasa wajen ' ta karb'i handbag d'inta sannan suka nufi inda driver ke tsaye yana jiransu. Shiga motar sukayi a gajiye ' tukunna yajasu ya maidasu gida, saida sukaji yayi packing ' sannan suka fito daga motar suka nufi cikin gida. Fadwa na bud'e k'ofar parlon taji wani shock a jikinta cak ta tsaya a wajen ' don ganin yadda mutane suka cika parlon , Ilham abinne ya bata mamaki ganin yadda Fadwa ta tsaya awajen. "Ke don Allah meye haka ' ji yadda kikasa mutane sunata kallon mu," Ilham gaishe su tayi da hanya ' sannan itama Fadwa ta gaishesu, Ilham ganin Fadwa tak'i tafiyane yasa ta kama hannunta ta jata suka wuce d'akin su. Bayan shigarsu d'akine Fadwa ta fad'a saman gado cike da gajiya. "ai kwanciya bai gankiba tukunna." "Kamarya?" Fadwa tayi tambayar ta k'ok'arin gyara kwanciya. "eh tashi zakiyi muje mu gyara d'akin saukan bak'i , don nasan ba wani datti yayyi ba k'urace kawai, don wallahi bazan iya sharing toilet ba ' kina gani harda mutane k'auye akazo, yoo koma mutanen birnin nefa?!" Fadwa ajiyar zuciya ta sauke ' tare da cewa. "To nidai yanzu ki daure kije ki farayi ' don wallahi agajiye nake." "to naji." Har Ilham ta tashi zata bar d'akin, sai kuma ta tsaya gamida juyowa. "Yawwa Fadwa ya kamata fa ' muyi arranging yadda za'ayi KAMU." "Eh jeki dawo dai ' koma menene saimuyi magana akai koh." Ilham ficewa tayi daga d'akin don zuwa gyarawa bak'i inda zasuyita kara kainan su, Fadwa kuwa nan bacci mai dad'i ya d'beta. *Dedicated To My Fan's* *_Seemaluv the brave💪_*😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 🌹GODIYA🌹 Dukkan Godiya Da Yabo Sun Tabbata Ga Ubangiji Mallakin Sammai Da Kassai, Wanda Ya Tsaida Ita Ya Kuma Shinfidata Ba Tare da Wani Majingi Ko Taimakon Wani Abin Halitta Ba. Tsira da Amincinsa Su Tabbata Ga Annabin Karshen Zamani Cikamakin Annabawa, Wanda Haskensa Da Kamshinsa Basa Gushe wa Daga Zuciyar Wanda Yafi Kowa Yi Masa Salati. 🌹SADAUKARWA🌹 Na Sadaukar Da Wannan Littafin Ga Marigayi Muhammad Abdulmumin Suraj Da Marigayi Lawal(Na Goggo )Allah Yaji Kansu Da Rahmarsa Ya Haskaka Makwancin su, Allah Ya Bamu Guzurin Ishesu Cikin Ni'imarsa Amin-Amin. 🌹IYA YENA🌹 Iyayena Alhaji Idris Musa Alhasan Da Hajiya Amina Ango Abdullahi, Allah Ubangiji Ya Biya Muku Dukkan Buka tunku Ya Kuma Yi Muku Sakayya Da Gidan Aljanna Kan Irin Tarbiyyar Da Kuka Bani Na Gode Kwarai, Allah Ya Kara Lafiya Da Tsawon Rai Amin Ya Allah. 🌹KANNAI NA🌹 -Hafsat Idris -Alhassan Idris -Fatima Idris -Sa'adatu Idris 🌹Allah ya bar Zumunci Yan Uwana.🌹 -Aunty Bara'atu -Aunty Mahadiyya -Aunty Hafsat (Ummi) -Aunty Khadija (Yarinya) -Aunty Fatima (Gaje ) 🌹KAWAYEN ASALI🌹 -Asiya Muhammad (Reality ) -Rabeeat Idris Baba (Slexy ) -Fatima Ango Abdullahi (Queenart ) -Zainab Abubukar (Sparkle) -Zainab Ibrahim. 🌹BAN MANTA DAKU BA🌹 -MISS XOXO -MELODY -CUTE ZARAH -ZAHRA BUKAR -ILILEE -MR SMILE -RAHEEM -ASY KHALEEL -MAMAN USY -SADNAF -ANKA -.........AND THE REST.... 1-2page🌹 Da Gudu Fadwa ta biyo Ta tana Fad'in, "Allah ilham ki bani Waya ta bana so. Fitowar Umma Keda wuya ilham taje bayan Umma ta Boye ' Umma ta ce, "Ilham? Fadwa kika tsokana koh? "Eh Umma duba fa Chatting takeyi da Wani Saurayin ta. Ilham Zata Nunawa Umma Wayar kenan ' Fadwa tayi Sauri ta Fizge Wayar daga Hannun ta. "Aunty Karya Ilham takeyi miki, ni banda Wani Saurayi. Umma zatayi magana kenan Yaya Farook ya shigo parlon cikin bacin Rai ' Fadwa Da Ilham suna ganin shi suka sunkuyar da kai cike da Nutsuwa. "Wannan wane irin iskancin banza ne ' bance maku idan ina bacci banason surutu ba? A tare suka Amsa mashi da cewa, "Ka ce!!! Yaya Farook kallon wayar da ke hannun Fadwa yayi, "Ke kuma ban wayar Nan ' nayi seezing dinta, Nan Hawaye suka cika idon Fadwa jikin ta na rawa Ta mika mashi Wayar, "Yaya Farook please am.... Tun Kafin ta Karasa fada ya daka mata tsawa da cewa, "Yimin Shuru. Yaya Farook Ansan Wayar yayi sannan ya juya ya Wuce Dakin Shi. Umma Koma wa tayi ta Zauna ba tare da ta saka masu baki a Maganar su ba, "To ai saiku dawo ku zauna tunda ya wuce. Cikin Sauri suka dawo suka zauna ' Fadwa kuwa idanu cike Da Hawaye. "Umma Don Allah kitayani bawa Yaya Farook Hakuri ' ya dawomin da Waya ta. "A'a babu ruwa na a maganar ku, Aikune dun bakwajin Magana. Fadwa maida kallon ta tayi ga Ilham wacce itama jikin ta dar dar yake saboda tsoro. "Ai duk Ke kikaja gashi nan ya Anshemun waya. Harara Ilham ta watsawa Fadwa, "Ke inda kinsan tsoron da ke jikina da bakimin wannan Maganar Banxan ba. Shuru sukayi nad'an lokaci sannan Fadwa tayi Zanbur ta mike tsaye tare da dafe kanta, "Nashiga uku ilham ' na manta ban sanyawa wayata security ba, gashi Yaya Farook zai iya shiga wani wajen dabam. Umma tashi tayi tare da cewa, "Ni yaran nan kuna neman kusamin ciwon kai wallahi ' bakin bazai ta'bayin shuru ba. Ta na gama fad'in haka ta wuce sashen ta. "Nifa Fadwa duk fa laifinki ne ' ke ce da kike yawon fito da wayar ki parlor gashi nan tsautsayi ya Afka mata. Cewar ilham. Fadwa koma wa tayi ta zauna tare da zuba tagumi, "Don dai Abba yayi tafiya ne Amma dashi zai kwatarmin wayata. Ilham najin haka tayi saurin toshewa Fadwa baki, "Ke wai bakisan duk Abinda muke fada Anaji ba? To nidai karki jamun duka ' kinsan halin Yaya Farook sarai don ya jibge mu bawani abu bane Awajen shi. "To yaji din mana ni ina ruwa na? Cewar Fadwa. Ilham mikewa tayi tsaye tare da yiwa Fadwa kallon Naman kaza. "Lallai kuwa jiki zaiyi tsami ' ni kinga tafiyata... 🚶 Ilham juyawa tayi a guje ta wuce dakinsu ' nan wajen Tabar Fadwa rai abace. Wacece Fadwa, 'yace Ga Alhaji Aminu Muktar ' kuma yace Ga hajiya Amina Shehu, Allah yayi masu rasuwa ne sakamakon Goborar da suka ' gaba daya suka kone. Fadwa ce kadai ta tsira, A lokacin Fadwa Tana da shekara Goma sha tara 19 ' Hakan yasa Alhaji Sulaiman wato Aminin Mahaifin Fadwa, Ya amince shi zai rike ta da Amana kuma zai saka ta cikin Y'ay'an shi ' tamkar shine Ya haifeta. Alhaji Sulaiman Mahaifine awajen Yaya Farook da Yaya Khaleel da kuma Ilham, haka zalika 'ya'yane Awajen Hajia Maimuna, wacce suke kira da Umma. 👄👄👄😜 Dedicated To My Fan's. ©ONLINE HAUSA WRITERS. [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 3-4page🌹 Fadwa na Zaune ' sai ga Yaya Farook ya shigo parlon, Ta na ganin shi ta mike tsaye. "Yaya Farook kayi hakuri don Allah. Ko kallon ta biyi ba ' ya Wuce. Ta na ganin ya fita ta nufi Dakin shi kai tsaye, "Yanxu zan sami damar Daukar wayata ' kuma inyi mirsisi . Tana gama Fadin haka ' ta hau yimashi bincike A dakin, gaba daya ta birkice dakin ' Fadwa ta du'ka zata bude Drower kenan taji magana kamar daga sama. "Kinyi ajiya a wajen ne dazaki dauka? Da sauri Fadwa ta dago kanta har tana Bige goshin ta ' Fargaba da tsoro ya hanata juyowa, "zaki juyo ki kalle ni, ko sai kinji saukan duka? Cewar Yaya Farook. 😨 Nan Fadwa ta hauyin adduoi kala kala ' saboda tsabar tsoro, A hankali ta juyo ta kalle shi. "Me kike nema a dakin? "Yaya Farook ' Don Allah kayi hakur.... Tun kafin ta gama rufe baki ' ya dauke ta da mari tasss.... Nan take Fadwa ta Dafe kumatun ta tare da Dukawa kasa, cikin kuka. Cen bata ankara ba taji saukar Hauri a jikinta, "Ahhhhgg! Nan take ta fara Aman Wahala ' a galabaice, "Zaki sake shigowa daki na ba tareda iznina ba? Zaki sake? Fadwa inbanda girgiza kai babu abinda takeyi Alaman A'a. "Good! Tashi ki fice mun a daki kuma ki dauko Mopper ki goge aman da kikayi!! A guje ta tashi ta fita ' cikin hanzari ta dauko Mopped ta goge Aman, Yaya Farook na kwance saman gadon shi yana kallon ta ' "idan kuma kingama ki dauko Perfume ki sa awajen ' don banason Karni yadame ni. To kawai Fadwa ta ce sannan ta je ta dauko turare ta sanya ma wajen. Da sauri ta fice donma kada ya tsaida ita, kai tsaye ta wuce dakinsu ' Ta iske Ilham akwance ta nata sharar baccin ta, Fadwa zuwa tayi ta zauna a gefen gadon ta kafa wani sabon Kuka tamkar yanxu ne Yaya Farook ya mareta. Kukan ta ne ya dami Ilham ' yasa ilham farkawa daga baccin da takeyi, Ganin Fadwa a cikin wani hali ne yasa tayi hanzarin gangarowa kusa da ita. "Fadwa? Me yafaru? Da sauri Fadwa ta share hawayenta ' "Babu komai Ilham ' kawai na tuna da Iyayena ne... Ilham rungume Fadwa tayi cike da tausayi, "ayya kiyi hakuri Fadwa ' kedai kirinka masu addua kawai, kuma duk abinda kikeso a Abbanmu na nan ko? Kai Fadwa ta daga mata alaman Eh, Sannan Ilham ta lura da shedan yatsu a fuskar ta, Alamun mari. "Subhanallah! Fadwa Waye ya mareki haka? Cewar ilham. Fadwa shuru tayi bata Ce mata komai ba, sannan Ilham ta ce. "Hmm Kinje daukan wayar ki dakin Yaya Farook ko? "Ilham na dauka yayi nisa ne sabida naga fitarshi, Amma ina shiga ya ritsani aciki. "Aikin gani Allah yakara ' yanzu ai jikinki ya gaya maki, Kina abu kamar bakisan wanene Yaya Farook ba. "ilham Yaufa tsawon Shekara Biyu kenan ' da zuwa na gidan nan Saidai inji Kuna labarin Wani Yaya Khaleel, wai waye shi. Ajiyar zuciya Ilham tayi gami da Zuba ta gumi, "Meyafaru naga kinyi ta gumi? cewar Fadwa. "hmm, Dole inyi Ta gumi domin kuwa Inhar Yaya Khaleel ya dawo ' to zaman parlor ma sai ya gagaremu. 😨Zaro ido Fadwa tayi cike da mamakin wannan Alamari, "To wai wanne yafi zafi cikin su? Cewar Fadwa. Nan Ilham ta gyara zama tare da kama Hannun Fadwa, "hmm Fadwa ai inhar Yaya Khaleel ya dawo to Yaya Farook dan kallo zai zama. Wani ihu Fadwa ta Saki ' cike Da Zulumi, "Ahhh🙆 to yaushe zai zawo? Cewar Fadwa. Dariya Ilham ta yi cike da buga kafa, "What are you eating nabaka is falling dawn?' abba ya ce mun Next month Yaya khaleel zai dawo, Kuma zai gama School din shi gaba daya. 😨😨😨😨 Ilham nagama fadin haka , Fadwa ta ruga da gudu ta fada Toilet... Sai da Tayi 5 minutes sannan ta fito ' tana fitowa suka hada ido Da ilham, Babu abinda ilham keyi inba dariya ba. "Ke ni bazan biye maki ba ' duk kinbi kin gama tsorata mun ciki, Ni yanzu ma bacci xan. Fadwa na gama fadan haka ' ta haye gado ta fara bacci, ita kuwa Ilham ta Dauki wayae ta ta hau chat. *AROUND* *7pm* Ilham Da Umma suka fito parlor Domin suyi Dinner dinsu, Shima Yaya Farook Fitowa yayi daga dakin shi yaje Yayi joining dinsu a Dinning table ' bayan Sunfara cin Abinci ne Umma ta ankara bata ga Fadwa a wajen ba, "ilham? Ina Fadwa take ne? "Umma tana daki a kwance ' wai zazzabi take ji, Yaya Farook ajiye spoon dinda ke hannun shi ' tare da cewa, "Zazzabi? And she is too big tazo ta fada abata magani ko? Umma bara inje induba ta, Kai Umma ta daga mashi alaman Tor, sannan Yaya Farook ya tashi ya nufi dakinsu Ilham. Koda ya shiga a Dukunkune ya iske ta acikin Blanket ' Ta na kuka, Yaya Farook karasawa yayi ciki ya zauna a gefen gadon tare da yaye Blanket din. Ganin yadda take rawan sanyine tausayin ta yakamashi, "Bakida Lafiya meyasa Bazaki fada ba? Fadwa shuru tayi bata ce komai ba, "Ki tashi ki shirya inkaiki Hospital yanzun nan. Har Yaya Farook ya mike tsaye da niyyar bata waje, yaji ta riko hannun shi. "Yaya Farook don Allah idan Munje kace Masu ' karsumin Allura please!!! Tausayin ta yasa ke shiganshi ' yayi sauri ya cire hannun ta daga Jikin shi, "Is Ok! Ki dai tashi ki shirya ' kafin kuma Raina ya baci yanzun nan. Ya na Gama Fadin haka ya juya ya fita cikin Sauri, Ya wuce dakin shin domin ya dauko key din mota. 👄👄👄😜 *Dedicated* *To* *My* *Fan's* [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 5-6page🌹 Har saida Yaya Farook Yaje ya dauko key din ya dawo parlor, ya zauna zaman jiran Fadwa. sai da ta Bata Minti 30,sanan Ta fito Parlon. "Yaya Farook gani! Cewar Fadwa. Tashi tsaye yayi tare da saka hannun shi cikin aljihu ' gami da yimata Wani mugun kallo, "Na dauka ko ' kinji sauki ne ai. "Don Allah nidai Farook ka kaimin yarinya aduba ta. Cewar Umma dake zaune a dinning table ta na kallon shi. Yaya Farook fitane yayi Fadwa na biye dashi a baya har suka isa wajen motan, Ya fara shiga sannan itama tashiga cikin hanzari mai gadi ya bude gate din ' tukunna Yaya Farook Yaja motar. Ba tare Da wani bata lokaci ba suka isa cikin Hospital yayi packing A gefe sannan suka fito, ganin Fadwa ba ta sauri yasa ya kama hannun ta ' Haka ya dunga janta har suka kai Office din Doctor din. Sannan likitan ya duba ta Ya rubuta mata magun gunan da za'a siya, Cikin jin Dadin Fadwa ta Ansa takaddar magungu nan don ganin babu allura ko daya aciki. Har ta mike tsaye Likitan ya tsaida ita da cewa, "Ki tsaya Akwai Allurar da za'ayi yanzu guda biyu, Data amai da kuma Wanda zata rage maki zafin jiki. Ta najin haka ta juyo ta kalli Yaya Farook, Suka hada ido ' Ganin Ya hade rai ne yasa ta sunkuyar da kanta ba tare da tace komai. "Idan kin shirya sai ki juyo. Cewar doctor, Jin haka Yasa ta juya ta mika mashi baya kamar da gaske ' Daya matso sai ta matsa haka suka dungayi da Dr din, Abin ne yabawa Yaya Farook haushi ' A fusace ya mike tare da finciko Fadwa ' ya rungumeta sosai ta yadda bazata iya motsi ba, "Doctor yi mata Allurar ' don sauri nakeyi. Cewar Yaya Farook, Fadwa bata ankara ba taji shigar karfe ajikin ta ' jin haka yasa tasaki ihu cike da kankame Yaya Farook, "Wayyo Allah Yaya Farook!!! "Shhhh, kiyi hakuri saura guda daya kinji ko? Cewar Yaya Farook. Fadwa ta naji tana gani aka sake tsira mata wani allurar, Sai da aka gama sannan Yaya Farook ya zaunar da ita. "Yanzu Zaku iya tafiya ' but saika dan rike ta saboda akwai Allurar da akayi mai sanya jiri. Ok kawai Yaya Farook ya ce ' sannan Ya rike hannun Fadwa suka fita daga wajen ' daker Fadwa Take jan kafar ta Yaya Farook ya lura da haka, "Zaki daga kafa kimin sauri Ko saina dauke ki tukunna? Dago kai tayi ta kalleshi a gala baice , "Yaya Farook bazan iya bane! Bata gama rufe baki ba ' taji ya dauketa cakk tamkar wata jaririya, Fadwa Kara lafewa tayi a jikin shi don kuwa batada wani karfi a jikinta. Haka ya ratsa cikin Hospital din da Fadwa a hannun shi ' mutane kuwa sai kallon shi sukeyi, kai tsaye ya nufi wajen Motar shi yasa key ya bude sannan ya zagaya ya saka Fadwa A seat din baya, "Saura kuma ki 'ki kwanciya. Abinda ya fada kenan sannan ya shiga mota yaja suka koma gida A cikin *30* *Minutes* . Horn Yaya Farook ya yiwa Maigadi yazo ya bude ' tukunna ya karasa ciki. Packing yayi cikin hanzari ya fito gami da Jan hannun Fadwa, "kokarta ki fito don Yanzu dai ' nima nagaji bazan iya Daukanki ba don nauyine dake!. Jin haka yasa Fadwa taja jikin ta fito daga motar cikin sanyin jiki, har suka shiga cikin parlor ' A zaune suka Iske *Ilham* tana Danna waya, Ganin su Yaya Farook ne yasa tayi saurin sake wayar a riga. "Ina Umma? Cewar Yaya Farook. "Tana Sashen ta, "Tor ki kawowa Fadwa Dinner dinta yanzu taci a gaba na. Cikin hanzari Ilham ta tashi ta nufi Kitchen, "Ke kuma bazaki sami waje ki zauna bane kokuwa? Cikin sanyin jiki ta zauna ' Gami da kallon kasa, don batamaso su hada Ido dashi. Cikin dan kan kanin lokaci Ilham ta dawo da plate a hannun ta, Jellof rice ce a ciki sai naman kaza cinYa daya. Fadwa ansan abincin tayi tare da toshe hanci ' "Aiko zaki amayar da Hanjin cikin kine ' saikin cinye abincin nan tass, bakina wani toshe hanci ba. cewar Yaya Farook, Tun da ta ansa abincin ' sai kollon shi takeyi, takasa sawa abaki. Ganin haka ne Yaya Farook Ya Ansa abincin daga Hannun ta tareda diban spoon daya, "Oya Ansa ' dakaina zanba ki ' kinayin Amai kuma kiji saukan duka. Ba musu Fadwa ta bude bakin ta Yasa ka mata Abincin ' daker ta iya haddiyewa. Ilham na tsaye a wajen Ta na kallon su ' Dukka dukka Spoon uku kawai Ta ci, ta fara Kakarin Amai ' Bata Ankara ba Taji saukan dundu tiim Abayan ta haka yayi Dai dai da Shigowar Umma Parlon, "Subhanallah ' Wai kai Farook mekakeso ka maida kanka? Mugu ko mene? Umma zuwa tayi taja hannun Fadwa, ta zauna a kusa da ita. "Ya jikin naki? Cewar Umma. "Umma da sauki ' Amma Umma na koshi da abincin haka bacci zanyi. Kai Umma ta daga mata tare da cewa, "Shikenan, *Ilham* rike ta ku tafi daki. Hannu *ilham* ta kamama *Fadwa* sannan suka tafi daki. Yaya Farook kallon wristwatch din hannun shi yayi yaga ' 9:20pm dare yayi sosai, sannan ya maida kallon shi wajen Umma. "Umma sai da safe , ni zan kwanta. "To Allah ya tashemu lafiya! A tare suka tashi kowannen su ya wuce sashen shi. yaya Farook na shiga daki ya cenja kayan jikin shi zuwa na bacci, sannan ya Haye gado tare da ciro Wayar Fadwa a drower gado ' ya shiga Gallery ya fara kallon pictures dinta inbanda smilling babu abinda yakeyi, Cen sai ya cikaro da wani hoton da tayi itada wani namiji A School ta dafa shi. Nan fa Zuciyar shi tafara mai radadi da zafi,. "Allah ya kaimu gobe saikin Fadamin Uban waye wannan. Ya na gama fadin haka jefar da wayar a kasa, Daker ya iyayin bacci a wannan lokacin. *Washe* *Gari* *Around* 4:00am Yaya Farook Ya tashi ya wuce masallaci, Bayan ya dawo ne ya koma bacci. Wajen 6:30 *Ilham* ta shi ' tashiga bathroom tayo Alwala sannan ta tada *Fadwa* daga bacci, "Fadwa tashi muyi Sallah ' kada lokaci ya kure. Cikin Magagin bacci ta tashi tafada Bathroom ita tayi Alwalan tukunna ta fito suka yi sallah, Bayan sun sallame ne Fadwa taga Ilham ta haye gado tare da Lullube wa. "Ilham bazaki je School bane yau? "Eh ' saboda bakida lafiya konaje school din bazaimun dadi ba. Murmushi kawai tayi sannan ta mike tsaye tare da cire hijjab dinta, "Allah yasa Yaya Farook ya gane cewa bazakije School ba. Nan take ilham taji cikin ta ya murda, "insha Allah haka bazata faruba. Fadwa hayewa gado tayi ' bacci yayi awon gaba da ita. Basu suka tashi ba sai wajen 7:30, koda suka tashi Ilham kitchen ta shiga domin hada Breakfast. Yaya Farook ' farkawa yayi daga Bacci yashiga bathroom yayi wanka ya fito sannan ya shirya ' ya fita siyowa Fadwa Magungunan ta, Ba shiya dawo ba saida aka gama hada breakfast sannan ' Yana shigowa parlor ya iske su Umma a dinning suna shan tea. Karasawa wajen yayi yasami waje ya zauna ' sannan ya gaida Umma cike da ladabi, Bayan ta amsa ne ya maida kallon shi akan Fadwa. "Idan kingama breakfast din ' kizo Ki sameni a daki Kisha magana. To kawai tace ' sannan Ya dauki tea dinshi ya sha, Yana gama wa ya mike tsaye gami da cewa. "kiyi ki gama Kizo ina jiranki ' don akwai inda zanje, "To wai Shi maganin dole saikai ne zaka bata? Cewar Umma. "Eh Umma ' Saboda Batason magani. Yana fadin haka ya juya ya wuce dakin shi, Ita kuwa Fadwa Hankalin ta atashe yake ' Cikin Zulumi ta ajiye cup din da ke hannun Ta tashi ta bishi Dakin. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 7-8pages🌹 Tana zuwa abaki kofa ta tsaya, Tayi Knocking gami da yin Sallama sannan ta shiga. A zaune ta ganshi ' yana dannan wayar shi, "Yaya Farook gani! dago kanshi yayi ya kalle ta ' tundaga sama har kasa sannan ya ce, "Ni zan biyoki Nan wajen inbaki maganin ko?😠 cikin hanzari ta karasa cikin dakin, kusa dashi ta tsaya ' Yaya Farook ya aje wayar shi a gefe sannan ya duk'a inda ya jefar da Wayar Fadwa ya dauko, Gami da Tashi tsaye. Damko kunnen ta yayi Tare da murdabawa, "Idan kika sake kikayi ihu ' Umma taji to abinda zanmiki sai yafi haka. Kai Fadwa ta daga mashi alaman To, sannan Yaya Farook ya kunna wayar tare da Nuna mata Hoton da yagani. "Uban waye wannan? Ya fada yana sake murda kunnen, "Yaya Farook Don Allah kayi hakuri ' Akwai zafi.... Cikin launi na kuka ta karashe maganar, Kunnen ta duk yayi jaaa duk da Kasan cewar Chocolate colour ce sai da yanuna. "Oh akwai zafi kike cemun? Akwai zafi kike cemun? Jikake timmm ' saukar duka a bayan ta, Cikin kuka tace. "Yaya Farook, kayi hakuri ' wallahi zan fada maka. Sakin kunnen yayi ' sannan ya sami waje ya zauna, "daman wannan School friend dina ne ' Kuma ni banmasan shi na dafa ba . Ta na fadin haka ya watso mata wata harara ' Cikin sauri ta, "Wallahi Yaya Farook ' ka tambayi Ilham, babu wani abu tsakanina dashi. Ta Na gama rufe baki ' Ya hada Wayar da bango, Ta fashe. 😱 "Idanma Akwai wani abu tsaka ninku, to na fasa Wayar ' Kuma bazaki sake yin Waya ba tunda abun naku iskanci zai koma, har itama Ilham din saina karba nata. Fadwa babu abinda takeyi inba kuka ba ' Yaya Farook mikewa yayi ya dauko mata magun gunan, ya cire mata wanda zatasha yanxu Ya bata tare da bata cup din ruwa ta rike a hannu. "In kinga dama kiyimin Amai a daki ' Jikin ki kuma yagaya maki. Daker ta iya shanye Maganin ' Aje mashi Cup din tayi sannan ta juya da niyyar tafiya, "ke!!! Na sallame kine? Tsayawa tayi gami da Juyowa ta kalleshi ' Lemon sweet ya dauko daga cikin drower din shi, Ya bata. "Bude kisa abaki yanzu, Saboda maganin da kikasha Akwaisu daci. Babu musu tayi yadda yace ' "Oya Share hawayen ki ' Fadwa Share hawayen fuskarta tayi ' sannan ta kalleshi. "And Yanzu kinsan me nakeso kiyi? Ta girgiza mashi alaman A'a. "Murmushi nakeso kiyi yanzu ' saiki wuce. Don dole Fadwa ta matso murmushin karfin hali ' tayi mashi, Shima Murmushi yayi mata gami da cewa. "Good gurl, kokefa ' yanxu kina fita ki wuce daki ki kwanta, ki huta. Juyawa tayi ta wuce ba tare da tace mashi komai ba, Ta na fita taja tsaki. "Mtsweee!!! Wai adaki mutum ahana shi kuka, Nidai Wallahi sai Allah yasaka min. Dakin su ta shige ta kwanta kamar yadda ya Umarce ta'. Yaya Farook Fitowa yayi ' ya nufi Parlor ya iske Ilham, "Ke! Babu School ne yau? Cewar Yaya Farook. Nan take ta mike tsaye Ta tako har inda yake cikin Dingishin kafa, "Yaya Farook, targade nayi dazun ' shiyasa. Tayi maganar gami da nuna mashi kafar, Harara ya watsa mata sannan Ya fice. Ta ganin fitar shi ' takoma wajen Umma ta zauna, "*Umma* don Allah cewa Yaya Farook ' ya rika shan Ruwan Buta, Seriously Umma ya cika fushi da yawa matar shi zatasha wuya. "allah ko? to bari yazo sai infada mashi ' abinda kikace game dashi. 😨"No Umma kada ki fada babu ruwa na walkahi, Ban shirya shan duka ba. Tashi ilham tayi zata wuce sai kuma ta dawo ta zauna tare da cewa, "Yawwa *Umma* please ki bamu izni nida Fadwa mu fita. "Ina kuma zaku je? Kinsan dai Fadwa batada lafiya koh? "Haba Umma Shopping mu keso muje ' kibarmu kawai , ai ta sami lafiya. Cewar Ilham, Umma dogon Numfashi taja sannan ta ce, "A'a Ilham kidai bari Yayanku ya dawo sai kuje,. To kawai Ta ce sannan ta tashi ta wuce dakinsu ' Jikin sanyin jiki. A kwance Ilham ta iske Fadwa ' tukunna ta sami gefen gado ta zauna, "Fadwa? Ki tashi kishirya muje ' Shopping. Cewar Ilham, Zanbur Fadwa ' tayi ta tashi zaune cike da fara'a. "Wow! Aikam yanzu zan tashi inyi makeup, but yanaga jikinki a sanyaye? "Umma ce tace wai saimun jira Yaya Farook,. Ajiyar zuciya Fadwa tayi ' gami da mikewa tsaye, "Shine duk zaki wani damu? Ki dai tashi ki shirya. Ilham itama mikewa tayi ta shirya ' suka caba ado sannan suka nufi Parlor suka zauna zaman jiran Yaya Farook. *Around* *2:30pm* Yaya Farook Ya shigo gida ' Cikin sallama sanan suka amsa tare da Mikewa tsaye, "Lafiya? Kuka mimmike tsaye kamar soldiers? sunkuyar Da kansu sukayi ' sannan Umma dake gefe ta ce, "Cewa sukayi ' wai zasuje Shopping shine nace subari kadawo, tukunna. Watsa masu harara yayi ' ya wuce gami da cewa, "Babu inda zakuje. Kallon junan su sukayi ' sannan suka koma daki cikin kunkunai. zama sukayi gami dayin shuru nadan lokaci, "Nidai gaskiya, xanje inroke shi ' don seriously inada abinda zan saya, Idan ba haka ba kuwa Gobe daga school zanje. Harara Ilham ta watsawa Fadwa, "I think you're very stubborn right? Fadwa kinfiso Kici dukan banza ko? Alright Allah yabaki Sa'a. Ameen Ta ce tare da mikewa ' ta wuce Dakin Yaya Farook, Knocking tayi sannan ta shiga ciki ' A tsaye ta iske shi ya na kokarin cire rigar jikin shi, hakan yasa Tayi saurin juya mashi baya. Hakan yasa Yaya Farook yin Murmushi cike da cije leben shi, ya daure fuska. "Ke!!! Lafiya kika juyamin baYa? Dalla juyo ki fuskan ceni. Cikin tsawa yayi maganar ' Haka yasa tayin hanzarin Juyowa ta Fuskance shi. "Yaya Farook ' daman nazo ne Innemi izni awajenka. "For What? "Yaya Farook ' Please kadan barmu Mu tafi shopping nida Ilham i really want to buy something. "No!!!, Ya fada cikin tsawa! Nan take Idon ta ya ciko da Kwalla, "Yaya Farook, don Allah.... "banace A'a ba? Ko so kike sai nayi kwallo dake? Juyawa tayi ta fita daga dakin cikin bacin rai' a zuciyar ta tace, "Lallai kuwa gobe After School zanje'... Ta na gama Ayyana hakan a ranta ' ta wuce parlor ta yi zamanta wajen Umma. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 *9-10* page🌹 *Some* *minutes* *later* Yaya Farook ' ya shigo cikin Parlor Ya iske Umma da Fadwa suna kallo, "Fadwa Kiramin Ilham. Jin maganar tayi kamar daga sama' don batasa da shigowar shi parlon. Cikin hanzari ta tashi ta kira Ilham na dan wani lokaci, sannan suka dawo parlon tare. "Yaya Farook gani! "Indomie zaki dafamin ' yanzun nan, kuma *30Minutes* na baki. Babu musu ko wani alaman damuwa a fuskar ta ' ta fada kitchen, A cikin wannan *30minutes* ta gama ' ta zuba a plate sannan ta kai mashi Parlor. "Yaya, Gashi nan. Ansa yayi ya fara ci ' cikin sauri, Tukunna Ilham ta koma Ta zauna. Yana gamawa yayi Hamdala ' gami dayin gyaran murya, "Mhnm, Ilham da Fadwa ' tashi zakuyi Yanzu Ku shiga kitchen, Ayi lunch da wuri domin akwai Abokina da zaiyi joining dinmu. Cikin hanzari suka tashi suka bar Parlon zuwa kitchen ' Jellof rice with chicken sukayi preparing yi. cikin *1* *hour* Suka kammala komai sannan suka jera Abincin Saman Dinning Table. Yaya Farook kira ne ya shigo cikin wayar shi ' yayi recieving dinshi, "Hello Taj? Harka iso ne? To shikenan ganinan zuwa. Abunda sukaji ya ce kenan sannan ya tashi ya fita ' cikin *5* *minutes* suka shigo tare da Abokin nasa. Bayan Isowar su parlon ne ' Abokin nashi ya duk'a ya gaida Umma ta amsa cikin kamala, sannan Ta tashi tare da cewa. "Fadwa biyoni da Abinci na Daki. Cike da ladabi ta zubawa Umma abincin ta a plate ' Ta bita da shi, ita kuwa Ilham zama tayi A dinning sannan Yaya Farook ya Umarci Abokin sa da suje su zauna domin suci abinci. Bayan zaman sune Ilham ta yiwa Abokin nashi sannan da zuwa sannan tayi serving dinsu Abinci ' "Wannan ce kanwar ka? Yayi tambayar ya na kallon fuskar Yaya Farook, "Eh ita ce Kanwa ta. maida kallon shi yayi kan Ilham wacce take cin abinci, "Well, sunana Tajuddeen ' amma zaki iya kirana da Taj. Ko kallon shi Ilham ba tayi ba ' tace, "Am Ilham by name. Ta na gama fadin haka ne ' Fadwa ta shigo parlon tunda ta shigo Taj ya ke kallon ta ' kai tsaye ta wuce inda Ilham take, bayan ta zauna ne ' ta Zuba abinci ta faraci, still idon shi na kanta. "Farook? Wannan kuma wacece? Kuma mene sunan ta. Cewar Taj, "Ai gaka gata ' ka tambaye ta mana. Fadwa Kallon Taj tayi ' tare da yimashi Murmushi, "Sunana Fadwa ' kuma nima kanwar shi ce, Kaima meye sunan ka? Tajuddeen yaji dadin yadda Fadwa ta saki jikinta, "Sunana Tajuddeen ' Fadwa you have a nice name. Jin Haka yasa Yaya Farook ya kalle shi, cikin bacin rai. "Meye haka kakeyi Taj? Cewar Yaya Farook, "Me nayi kuma yanzu? yaya Farook kallon Fadwa yayi ' haka yasa ta sunkuyar da kanta kasa, "Ku tashi ku dauki abincin ku , ku shiga daga ciki. turo baki sukayi ' sannan suka mike tsaye, suka bar wajen cikin kunkuni. "Farook naga Alaman Kana takura wa yaran nan ' meyasa? Taj yayi tambayar gami da Ajiye spoon din hannun shi. "look, idan ka koshine mutashi ' mukara gaba, don nalura kacika shirme! "No Farook, ba shirme nakeyi ba ' wallahi tunda naga kanwar ka naji inason ta. 😨, Gamm ' gaban Yaya Farook ya Fadi, "Wace Kanwar ta wa? *Taj* murmushi yayi gami da gyara zafi, "Kanwar ka nakeso, Fadwa!!! And I hope bazaka hana niba? Yaya Farook is totally speechless ' yama rasa abinda zaicewa Taj, haka yasa shi mikewa tsaye tare da Sanya hannun shi a aljihu. "Ya naga ka mike tsaye ' kuma kayi shuru? Cewar Taj, "Saboda kazo abu mafi wahala. "Meyasa? "Saboda bazan iya baka Fadwa ba ' Taj ka nemi wata kawai. Ajiyar zuciya yayi ' sannan ya ce, "hmm, Farook kodai inada wani mugun hali ne? "Taj, Bakada wani mugun hali ' Kawai dai... "Kawai dai me? Yaya Farook shuru yayi ya kyaleshi ' don kuwa zuciyar kemashi zafi,. "Hm shikenan Farook, Yanzu inaso ka bani Damar yiwa Fadwa magana ' na *30* *minutes* kawai. OK kawai Yaya Farook ya ce ' sannan ya kwalawa Fadwa kira, Cikin sauri ta iso Parlon. "Yaya Gani. "Tajuddeen ne yakeso ku gaisa. Kallon Taj tayi ' cike da fara'a, Taj Mika mata Card dinshi yayi. "Ga card dina nan, Zaki iya nema na ta wannan Number din. Murmushi tayi gami da Kala kanta alaman to ' sannan sukayi sallama ta koma daki. Yaya Farook da Tajuddeen, fita sukayi Don suga gari. Bayan Shigar Fadwa daki ne ' tayi tsalle ta fada saman gado cike da jin dadi, "Wai ke lafiyan ki kuwa? Cewar Ilham, mika mata Card dinda yabata tayi ' tare da cewa, "Kinga Card din da abokin Yaya Farook ya bani ' kuma yace In nemeshi. "Ke kuma shine kiketa wani zumudi kinma kasa kama kanki gaba daYa. Tashi Fadwa tayi ta zauna ' Tareda cewa, "Ilham nidai guy din yaymun ne wallahi, Shiyasa gashi kyakkyawa . Yatsine Ilham tayi ' sannan tace , "Kudai kuka sani ' daga ke harshi din. Komawa ilham tayi ta kwanta abinta. *AROUND* *6:00PM* Da yamma Yaya Farook ya maida Taj gida, sannan ya tsaya yayi Sallah a masallaci tukunna ya dawo gida. Bayan shigo warshi ne ya iske su Ilham suna cin abinci, "Ilham ina Umma? "Umma ta na dakin ta, Waje ya samu ya zauna ' sannan yace, "Amma taci abinci kuwa? "Eh ta ci abinci. "Tor yanzu ' Kinsan me nakeso dake? Ta girgiza kai alaman A'a, "Kije Ki dauko min wayar ki kikawomin yanzun nan, 😨, zaro ido tayi gami da cewa, "Yaya Farook Menayi? wata mugun harara ya watsa mata, batasan lokacin da ta ruga aguje taje ta dauko wayar ta bashi ba ' itadai Fadwa ta na Gefe ta kallo. Ilham dawo wa tayi Parlon tare da wayar ta ahannu ' ta mika mashi, "Yawwa, kema Babu ke bayin Waya daga yau Ilham. Cewar Yaya Farook, "Yaya Farook don Allah kayi hakuri, wallahi.... Tun kafin Ta gama rufe baki ' Yaya Farook ya tashi ya wuce dakin shi tare da cewa, "Ki biyoni ki karba. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😝 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 *11-12* pages🌹 Nan Wajen Ilham ta zauna ' kusa da Fadwa, Idanuwan ta cike da hawaye. "Karki damu Ilham ' ninasan meyasa ya karbe maki waya, Saboda Taj Yace in neme sane shiyasa. Cewar Fadwa, "To ni meyasa abun zai shafeni? "Hm kada kidamu ' Bari Abba ya dawo mu fada mashi. Da sauri ta kalle ta ' cikin fuskar mamaki, "Lallaima Fadwa ' to nidai wallahi babu ruwa na, Idan kika fadawa Abba kinsan dai ' Yaya Farook kanmu zai rama ko? Ajiyar zuciya Fadwa tayi sannan ta ce, "Tor Allah ya kyauta ' nidai xanje in kwanta don banajin yunwa, kuma inaso in tashi da wuri gobe. Tana gama fadin ta tashi ta wuce Dakin su ' itama Ilham tabi bayanta. *Washe* *Gari* Da sassafe Su Fadwa suka tashi ' cikin hanzari suka shirya sannan sukayi breakfast, Suka wuce School. Bayan shigan su cikin Class ne ' lecturer ya shigo Yagama lecture sannan ya fito, Haka Yasa Fadwa ta sami wayar wata friend dinta ' Ta kira Tajuddeen ta hanyar yin Amfani da Card dinda ya ba ta. Ringing Uku yayi ya dauka, "Hello Who's this? Cewar Taj, "It's me Fadwa. Jin haka yasa yayi murmushi ' tamkar yana ganin ta. "Wow! Fadwa Yakike ' kina Ina ne haka? Naji surutu. "ayya! Ina School ne yanzu. "Zan iya zuwa School din domin mu gaisa? Murmushi tayi har sai da yaji ' Sautin shi, sannan ta ce. "Eh Zaka iya ' But kazo 2:00 lokacin munyi closing. Ok kawai ya ce ' sannan ya kashe wayar, ita kuma ta maidawa mai wayar ' wayanta. Ilham na zaune A seat dinta ' fadwa tazo ta zauna kusa da ita tare da cewa, "guest What!!! "Fadwa you know that am not good in that ' so kawai ki fadamun menene? Cewar Ilham, "Taj, ne yace min zaizo School din nan Anjima ' Domin mu gaisa. "wanene Taj kuma? "Tajuddeen mana ' Abokin Yaya Farook, 😨 a tsora ce Ilham ta mike tsaye tare da cewa, "What!!? Fadwa? Keko? Amma shikenan Allah ya baku sa'a, "Ke miye? Duk kika wani tsora ta? Aidama na fada maki ' zanje Shopping yau so After closing Idanma driver ya zo bana nan, kawai ki wuce. "Ok ' ai dayake ma ba jikina ne zaiyi tsami ba. Harara Ta watsa mata sannan ta tashi ta bar wajen. Bayan anyi closing ne ' suka fito daga school suka tsaya abakin gate, Don jiran driver. "Yanzu Fadwa ' bazaki hakura da wannan Shopping din ba? Cewar Ilham, "Nifa gaskiya Ilham banason haka ' ni idan kina fadim haka banajin dadi, Kawai addua zakimin kada Yaya Farook ya gane cewa bana gida. Suna cikin haka ne driver yazo ' Ilham ta shige mota ta bar Fadwa anan wajen. Bayan wuce warsu ne ' nadan wani lokaci Tajuddeen yazo da motar sa yayi Packing daidai inda take tsaye, sannan ya sauke glass din motar. "Kiyi hakuri na bata maki lokaci ko? Murmushi tayi ' Tare da Girgiza kai Alaman A'a. "To yanzu dai ki shigo mota sai muyi magana, Shiga motar tayi kamar yadda ya umarce ta, Bayan zaman ta ne ta ce. "Nifa dama shopping nakeso inje ' Saboda sauri nakeyi banaso Yaya Farook ya gane. Shuru Taj yayi nadan lokaci ' sannan ya ce, "Yayan ki yana takura maki ko? Ta daga kai alaman Eh ' Sannan yasa hannu ya shafa kumatun ta, "kiyi hakuri ' Ai muna tare ko? tsoro taji ganin yadda ya shafa fuskar ta ' hakan yasa ta fara dar dar Dashi. Shima lura yayi da yadda Fuskar ta ya sauya ' haka yasa ya ciji lips dinshi gami da yin Murmushi, "Nina fasa Zuwa shopping din ma ' Bara kawai in sami taxi ya kaini gida. Cikin damuwa tayi maganar ' har saida Ya nuna a fuskar ta, bude Kofar motar tayi xata fita ' yayi sauri ya rike Gelen ta cikin fargaba ta juyo ta kalleshi. "Haba Fadwa, why are behaving like a kid? na lura tunda na taba fuskar ki ' yanayin ki duk ya cenja Why? Nan take jikin ta ya fara rawa ' cikin rawar murya tace, "Don Allah Taj ' ka sakemin gele na intafi, Please. "Tor yanzu bazaki bari intaba abinda yafi fuskarki tsadaba? 😨, Da karfi ta fizge gelen ta ta fito daga motar ' cikin hanzari ta tare Napep, bayan ta zauna ne ta kalli wristwatch din hannun ta taga 2:30pm ' nan gaban ta ya sake Faduwa. "Don Allah bawan Allah kayi sauri mana! "To aibaki fadamun inda zan kaikiba hajia. Cewar mai keke napep, Nan ta fada mashi inda zaikai ta ' sannan suka dauki hanya. Ba ita takai gida ba sai wajen 2:56pm, Tana sauka ta mika mashi kudin shi sannan ta shige gida ' Saida ta tsaya a bakin kofa tayi Adduo tukunna ta bude ta shiga ciki. Ta na shiga da Yaya Farook ' ta fara hada ido, Ya watso mata wata muguwar harara gami da Karkada kai ' Gaban ta ya fadi dakerr ta iya hadiye miyau, sannan ta waiga bata ga Umma a kusa ba haka zalika babu Ilham a kusa. Haka ta taka tare da yin sallama ' ta wuce ciki, "Hmm Ba yanzu zan kama kiba tukunna! A zuciyar shi ya fadi haka, ' ita kuwa sai jin dadi takeyi ganin bai tsaida ita ba, Cikin fara'a ta shige daki ' akwance ta iske Ilham ta na Assignment, Sannan Fadwa ta ajiye handbag dinta a saman Drower ta koma ta zauna a gefen Ilham, "Ke! Ilham Yaya Farook ' baimin komai ba wallahi. Ilham dariyar mugunta tayi tare da jan tsaki, "saida ya tambaye ni ' ina kika tsaya nikuma na fada mashi duk abinda nasani,sannan ya ce yau jikin ki zai gaya maki kuwa. "Na shiga ukku ' ni Fadwa banda ruwan wanke kai yau, inama ace Abba zai dawo yau. Cewar Fadwa, Tabe baki Ilham tayi ' sannan ta cigaba da abunda takeyi, Ita kuma Fadwa ta tashi ta cire kayan jikinta ta daura towel ' tukunna ta shige bathroom don Watsa ruwa. Bayan Shigan ta Bathroom ne Yaya Farook ya shigo dakin, "Ina Fadwa? Cikin tsawa yayi maganar ' haka yasa Ilham firgita, Ta yi saurin cewa, "Tashiga wanka! "Ok Tana fito wa kice tazo ta sameni ' kada kuma ta batamun lokaci.. To kawai ta ce sannan ta maida kanta akan Assignmenta dinta. Bayan *5* *Minutes* Fadwa ta fito daga wanka, Ta na fitowa Ilham ta ce. "*Yaya* *Farook* yazo da kansa kuma yace kina fitowa kije kisame shi ' yanzu. Raras gaban ta ya Fadi ' Gami da zaro ido. "Ilham please kicemun wasa kike! Shuru Ilham tayi ta kyaketa ' aibabu shiri Fadwa ta baza a guje taje dakin Yaya Farook, saida tayi Knocking Sannan Ta shiga ' tama manta Towel ne a jikinta, Yana ganinta ya mike tsaye . "Yaya Gani! Daf ita Ya matso ' sannan ya riko hannun ta yajata har cikin Dakin, "meyasa Bakijin magana Ehe!!!! SunkuYar da kai tayi ba tare da tace komai ba, "Ba zaki fadamun inda kukaje ba saina mareki? Hawaye ke zubo mata a fuska amma babu yadda ta iya, "Yaya Farook, Tajuddeen ne yazo School dinmu Shineee.... Bata gama rufe baki ba ' taji saukan mari a fuskar ta Tasss.... "Ahhhgggg!!!! Sauri Dafe wajen tayi ' cikin kuka, "Fadamun Ubanwa ya gayyace shi wajen ' idanba ke ba!!! Hannu biyu yasa ya dafa kafadunta gami da girgiza ta, "Kinsan meyasa nadamu ke? Kuma kinsan meyasa nake miki haka? Hmm Saboda ina sonki!! Ina sonki Fadwa!!! Jikinta yayi sanyi ' tsayawa Tayi ta na kallon shi cike da mamaki, "nan *BABBAN* *GIDA* * NE!!* Kuma cikin shi kike ' Fadwa kinsan waye Taj dahar kika saki jiki dashi haka? Ya fada gami da Girgiza ta ' da har sai da Towel din jikinta ya Kwance, Sauri Fadwa tayi ta rike Towel din ' cikin kuka ta ce, "Yaya Farook don Allah kayi hakuri ' bansan haka abun yake, please kayi hakuri. Harya daga hannun shi zai sake marin ta ' sai kuma ya fasa, ya sauke hannun tare da juya mata baya. "Fita ki bani waje ' before i did something that you will regret it. Juyawa tayi ta bar dakin' da gudu cikin kuka ' ta shige dakinsu. Saman gado ta fada ' kuka kawai takeyi tamkar ranta zai fita. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 @ *_I_* *_Honestly_* *_Dedicated_* *_this_* *_page_* *_to_* *_All_* *_Members_* *_of_* *_PWF_* *_Group_* ' *_you_* *_Gurls_* *_are_* *_simply_* *_Amazing_* *_in_* *_Anyway_*!!! *13-14* pages🌹 Kukan ne Ya dami Ilham yasa tayi saurin Rufe Littafin ta, "Haba don Allah Fadwa, Sai ka ce wata karamar Yarinya? And beside ke fa kika jawa kanki. Cewar Ilham, Fadwa tashi tayi ta d'auki Hijab ta sanya sannan Ta bar D'akin da gudu, bata tsaya ko ina ba sai a harabar Lambu. Numfashi taja nadan wani lokaci ' sannan ta share hawayen fuskar ta Gami da cewa, "Tabbas Taj baida hali mai kyau, to Amma aishima Yaya Farook d'in mugune ' Ta Ya zaayi yace yana sona? Kilama dai Banji dai kyau bane. Juyawa tayi cikin sauri ' ta nufi d'akin Yaya Farook, Bud'ewa tayi gami dayin Sallama. Akwance ta ganshi saman gadon shi yana kallon Fanka, Tsoron tambayanshi taji ' yasa ta juyawa zata koma inda ta fito, "Fadwa??? Ji tayi ya kira sunan ta ta wata irin sigarda bazata iya Fayyace wa ba ' Haka yasa ta juyo ta fuskance shi, sannan ya Sauko daga gadon ' ya tako har inda take ya riko hannun ta gami da murza gannun, "Is Everything Alright? Yayi tambayar ya na kallon cikin kwayar idonta, hakan yasa ta kasa Cewa komai ' sai dai ta tsinci kanta da cewa, "Yaya Farook ' dama hakuri nazo in baka. Nan ya saki hannun nata tare da juya baya ' Yayi Murmushi sannan ya ce, "No Fadwa idan har akan maganar Taj ne ' to bazan hakura ba.... Har sai kince min.... sai kuma yayi Shuru ' bai k'arasa maganar ba. "Yaya Me kakeso in fad'a? I promise you duk abinda ka ce inyi to zanyi shi ' Inhar zaka yafemun. Da sauri ya juyo ya kalle ta, "Fadwa ki ce kina sona! 😨zaro ido tayi cike da mamaki , ganin haka yasa Yaya Farook ya d'aure fuskar. "Meye kika wani zaro ido ' ko na fad'a abunda bazaki iya bane? Sunkuyar da kai tayi gami da girgiza kai, "Yaya Farook Ina sonka.... . Ta fad'a Tare da rufe Fuska ' k'o k'arin Juyawa tayi zata fita Yayi saurin fizgota, Har sai da tad'an tokare shi. "ina zakije? Mun gama magana ne dazaki wuce? Yayi maganar cikin Fad'a, Mamaki ne ya cika ta ganin yadda ya sauya cikin k'ank'anin lokaci. "Ba Dake nake magana ba?!! Cikin tsawa Yayi maganar ' nan take idanuwan ta suka ciko da hawaye, "Yaya Farook kayi Hakuri, nakasa.... bata k'arasa maganar ba ya dakatar da ita da cewa, "Come on, yimin shiru ' yar wannan maganar ce zaki cemun kinji kunya? Dama tuncen kina Sona... D'ago kai tayi ta kalleshi ' Cike da mamaki, harta bud'e baki zatayi magana yayi saurin taron Numfashin ta da cewa. "Karki fad'amun wata maganar Banza Anan wajen, Kuma zan gayawa Umma tayi maki Aure tunda Shi kikeso. "Yaya Farook Hakuri don Allah... Dariya taso ta kwace mashi yayi saurin Juya mata baya ' ya ce, "Oya fita kibani waje!!! Jiki a sanyaye ta bar d'akin, Kitchen ta nufa ta bud'e fridge ta d'auko ruwan sanya tasha, sannan ta wuce dakin su. Tana shiga ta iske Har Ilham tayi wanka ta shirYa, "Hm Harkin shirya nikuwa ko Mai banshafa ba! Cewar Fadwa, "Ke kuwa kina mene? Ajiyar Zuciya tayi ' sannan ta sami waje ta zauna, "Hm Babu komai ' Ai tunda kika koreni d'azun Daga d'aki nawuce Lambur. OK kawai Ilham ta ce , sannan ta wuce Parlor ' cikin sauri Fadwa ta sanya kaya Cikin shigar Tamfa tukunna tayi makeup, itama ta fito parlor ta zauna tana Kallo. *AROUND* *4:32PM* Umma ta fito daga sashen ta zuwa Parlor, Cikin hanzari tazo ta sami su Fadwa da Ilham a zaune. "Ku tashi maza, Ku shiga kitchen don Abban ku yacemin jirgin su ya kusa sauka. Jin haka yasa Fadwa tayi zambur ta mik'e tsaye cikin Fara'a ta ce, "Wayyoo Allah na Abbana Zai dawo ' Umma naji dad'in wannan Good news d'in. Nan suka fara gardama ita da Ilham akan Abunda zasu dafa, Hayaniyan sune yasa Yaya Farook fitowa Daga D'akin shi, Kai tsaye ya tunkaro inda suke hayaniyar ya tsaya yana kallon su. Ilham ce ta fara ganin shi ' tayi saurin Tab'a Fadwa, Amma inaa... ta riga tayi nisa. "Haha Tunda har kikayi Shuru ' to da magana ta za'a amfani..... Cewar Fadwa, Ta narufe baki taji anyi gyaran murya ' Haka yasa tayi saurin juyawa domin Ganin waye, Ido hudu sukayi Da Yaya Farook ' nan take cikin ta ya murd'a saboda tsoro, "Surutun Ubanme kukeyi? Ilham ce tayi k'arfin hali ta ce, "A'a dama Abba ne Umma tace zaidawo yau, shine nida Fadwa Muke Magana Akai. Harara Ya watsa masu ' dukkansu suka sunkuyar dakai, sannan ya ce. "Allah Ya dawo dashi lafiya ' inji wani ya bud'e baki ya kai k'arata wajen shi kuga yadda zanyi daku. Ya na gama fad'in haka ya Koma d'akin shi. Bayan ya wuce ne Ilham ta ce, "Hm Kadaiji dashi, Kinji Fadwa Mutafi Kitchen domin musan Abunyi. Jan hannun ta tayi suka nufi kitchen suka fara preparing girke girken Abinci kala Uku, Cikin *2hours* da y'an mintoci suka kammala komai, sannan suka jera a dinning table cike da Fara'a. Yaya Farook fitowa yayi daga d'aki cikin hanzari ya wuce masallaci , Acen yayi Magrib sannan Ya dawo. Fadwa tsayawa tayi a bakin kofa Tana jirar isowar Abba ' bud'e k'ofa taji anyi hakan yasa tayi saurin jan handle din gami da cewa, "Oyoyo Abb.... kasa k'arasa maganar tayi ganin Cewar ba Abba bane ya dawo Yaya Farook ne ya shigo, Cikin tsoro da sanyin jiki tace. "I thought Abba ne ya dawo shiyasa.... Harara ya balla mata tare da jan tsaki ' sannan ya je wajen dinning table yayi zaman shi, Itama komawa tayi ta zauna Ilham kuwa babu abinda takeyi inbanda dariya. *_Kuyi_* *_hakuri_* *_wannan_* *_Don_* *_bashida_* *_Yawa_* *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 *15-16* pages🌹 Suna cikin Haka ne Umma ta shigo Parlon Ta sami Waje ta zauna Sannan Ta kalli Fadwa ' Ganin yadda jikin ta duk yayi sanyi, "Fadwa ya naga duk jikin ki yayi sanyi? Ko Halan Farook ya dake ki? Cewar Umma, Saida Ta kalli Yaya Farook sannan Ta girgizawa Umma kai alaman A'a, Suna cikin Wannan ne Sukaji Sallama Abba ' Ilham ce tayi zambur ta mik'e tsaye tare dayin Ihu, "ahhh!!! Yeee Abban mu ya dawo. Gaba d'ayan su Mik'ewa sukayi tsaye cikin murna suka tunkare shi, Ilham ta karb'a jakar hannun shi tare da cewa. "Abba sannu da dawo wa! Amsawa yayi Cike da fara'a sannan ya kalli Fadwa wacce ta rakub'e a bayan Umma ita a dole ta na fushi, "Haba Wa ya tab'amin Y'ata Fadwa? Cewar Abba, Nan ta saki Fuskarta Tayi murmushi sannan ta ce, "Abba kaine Kaimin Laifi da baka dawo da Wuri ba ' amma Yanxu Tunda Kadawo shikenan. Gaba d'ayansu dariya sukayi sannan suka nufi Dinning Table domin cin abin, Ilham kuma sashen Umma ta nufa Domin ta ajiye jakar Abba. Bayan Sun zauna ne ' Fadwa ta fara Yimasu Sarving Abincin, Sai da tabbatar ta zubawa kowa sannan Ta koma tazauna itama Ilham ta zo ta zauna suka fara cin Abinci ' Abba kallon Yaya Farook yayi sannan ya kuma kalli Ilham da Fadwa, "Fadwa?? Abba ya kira sunan ta cikin kamala ta d'ago kai ta kalle shi tare da cewa, "Na'am Abba. "Naga kin rame mun ne, A kwai mai takura maki ne? Abba na fad'in haka ta kalli Yaya Farook taga shima ita yake kallo ko zata ce wani abu, "A'a Abba babu mai takura mun, nayi rashin Lafiya ne. Ta na gama rufe baki Umma tayi sauri ta ce, "Karki wani boye mashi ' babu mai takura maku inbanda Farook. "Haba Umma ki barta ta fad'a Da bakinta mana , ai ita tasan babu abinda nake mata. cewar Yaya Farook, Shuru kawai Fadwa tayi ta sunkuyar da kanta. "Hmm aini dama Nasan za'a rina Wannan zaman gidan naka wasane? Ainasan duk wannan bak'in halin kansu zai kare. Abba na gama fad'an haka Fadwa ta mik'e tsaye da niyyar wuce wa d'akin su. "Ina kuma zakije? Cewar Ilham, "Wallahi bacci nakeji sosai ' shiyasa zanje in kwanta. "Tohm nidai bacci ba yanzu ba, Fadwa d'aukan plate d'inta tayi tare da yiwa Umma da Abba sallama , sannan ta kad'a kanta ta wuce d'aki. Bayan Wuce warta ne da y'an mintoci, Yaya Farook shima ya tashi gami da yimasu sallama ' kai tsaye ya wuce d'akinsu Ilham, Ko sallama bai yiba yana shiga ya iske Fadwa har tayi shirin bacci rigar bacci ne ma a jikin ta ' tana zaune a kujerar Madubi. Ganin mutum kawai tayi a tsaye a bayanta, hakan yayi matuk'ar bata tsoro ' a firgice ta mik'e tsaye tana shirin yin ihu yayi saurin Toshe mata baki, "Are you out of your sense? Akwai wanda zai shigo d'akin nan bayan nine? Girgiza mashi kai tayi sannan ya sake mata baki ', "Yaya Farook Lafiya? Tayi tambayar ta na kallon idon shi, "Fadwa meyasa bakiyi sallama dani ba kafin Kije ki kwanta? Yayi maganar a sanyaye ' ita kanta saida tayi mamaki, "Am sorry Yaya Farook. "Ba kya tunanin halin da zan shiga? Zaro idanu tayi cike da Mamaki a zuciyar ta tace, "Oh ni Allah Yau kuma Yaya Farook ni yake fad'awa haka. K'ara matsowa yayi dafff da ita suna shak'an numfashin junan su, sannan ya riko habar ta. "Am totally in love with you Fadwa ' am in love with your dress, Abun ne ya bata tsoro ganin yadda ya sauya lokaci d'aya gashi kuma su biyu a d'akin hakan yasa ta cewa, "Yaya Farook please Kaje kada Ilham ta zo ta sameka a nan wajen kaji. Saurin sakin ta yayi tare da cewa, "Tor Promise me that we will Always be together. Kai ta d'aga mashi Tare da cewa, "I promise you that i will always be with you!! Tana gama fad'in haka Ya juya Ya fita daga d'akin ya wuce d'akin shi. Bayan fitan shine Ilham ta shigo d'akin a tsaye ta sami Fadwa, "Kinyi wani tsaye kamar soldier ' ya akayi. ta fad'a tana kokarin cire rigar jikinta don sanya ta bacci, Murmushi kawai Fadwa tayi sannan ta ce. "I think am in love with him. ta fad'a tana k'ok'arin Hayewa saman gado, Cikin sauri Ilham ta sanya rigar bacci itama ta d'are saman gadon Tare da zurawa Fadwa ido, "In love with who ' Fadwa? "No lokaci baiyi ba tukunna Ilham ' kibari sai lokaci yayi sai in fad'a maki. Ya tsine Fuska tayi gami da jan pillow, "Kyadaiji dashi kuma idan tayi wari aizanji. Cewar Ilham, smilling Fadwa tayi sannan suka kwanta. *** *** *** *** *** *Washe* *Gari* ... Da sassafe Fadwa ta farka daga bacci ' Jitayi tamkar an d'ora mata dutse a marar ta saboda Azabar Ciwo, "Ahhhghh Ilham don Allah ki tashi ki taimaka min, Cikin Magagin bacci Ilham ta farka , Ganin yadda Fadwa keta hawaye ne yasa Baccin idon ya washe. "Meke damunki? "Menstrual cramp, ke damuna Ilham please... ki bani pain reliever please. Cikin hanzari Ilham ta diro daga gado taja side drower ' ta ciro Paracetamol ta bata, sannan ta nufi Kitchen ta d'auko ruwa ta kawo mata. Bayan ta sha maganin ne ta tashi cikin dabara Ta sanya Pad (Always) a jikin ta sannan ta koma ta kwanta , bacci yayi awon gaba Da ita. Ilham Bathroom ta shiga tayo wanka tukunna ta fito ta shirya ' Sannan ta wuce Kitchen don ta had'a Breakfast, Cikin Sauri ta had'a tea tazuba cikin Plask takawo parlor ta ajiye, Su Umma da Abba suka shigo cikin Parlon Suka zauna sannan Ilham ta gaishe su. "Ina Fadwa?? Cewar Umma, "Umma Tana daki batajin dad'i Menstrual cramp ke damunta. "Subhanallah to tasha magani daiko? Cewar Abba, Kai Ilham ta d'aga mashi Alaman Eh sannan ta zuba masu Tea din Ta basu, Itama ta cigaba da shan nata tea din. Bayan ta gama breakfast d'inta ne ta wuce d'aki domin tayi shirin wucewa School, Tana shiga ta d'auki Handbag d'inta sannan ta juya ta fito daga d'akin. Ta na fitowa suka had'e da Yaya Farook, ta gaishe shi sannan ta juya Zata wuce Yayi saurin dakatar da Ita da cewa. "Ita Fadwa bazata je School d'in bane yau? "Eh Batada Lafiya ne! Ok Kawai ya ce mata sannan tayi tafiyar ta. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 @*JAMEESHA* *_wannan_* *_page_* *_d'in_* *_nakine_* *_i_* *_just_* *_feel_* *_like_* *_dedicating_* *_this_* *_page_* *_to_* *_you_* *_because_* *_of_* *_love_* *_and_* *_friendship_* *19-20* pages🌹 Bayan wasu y'an lokuta k'alilan ne Umma ta ga kiran Yaya Khaleel ya shigo cikin Wayarta, Murmushi tayi gami da girgiza kai tukunna ta d'auka, "Sallamu Alaykum, " "Hello Umma!? Umma yau zan dawo gida in sha Allah." "Tor Khaleel Allah ubangiji ya tsare ' har jirgin naku ya tashi ne?" "A'a Umma But yanzun nan zai tashi ' shiyasa nakira!" Addua Umma tayi mashi sannan sukayi Sallama ta kashe wayar. Umma tashi tayi ta wuce d'akin su Ilham ' koda ta shiga Fadwa ce kawai tagani, "Fadwa Ina Ilham? " Cewar Umma, "Umma Ta shiga wanka ne," "To idan ta fito Kice mata ' kushiga kitchen ku shiryawa Khaleel Abinci, don yau zai dawo." 😱To kawai Fadwa tace sannan Umma ta juya ta koma parlor ' nan wajen ta tsaya tana kokwanto akan Maganar Umma, "Kai Kardai Yaya Khaleel dinda Ilham ta bani labari? Wayyo ' shikenan mumbanu " Cikin hanzari ta mike tsaye ' Ba tare da tasan abinda zatayi ba , kai da komowa kawai takeyi ' tana cikin hakan ne Ilham ta fito daga bathroom dauke da karamin towel a hannun ta tana goge gashin kanta, ganin yadda Fadwa keta yawo a dakin ne yasa ta tsaya cak ta na kallon ta. "I hope ba wani laifin kika kara Daukowa kanki ba?" Cewar Ilham, Tsayawa tayi ta kalleta with sad face ' sannan tace, "Kin fito kina wani Goge gashi ' verysoon zaki manta da wannan ai!!" "Me kike nufi?" "Eh Umma tace Mu shiga kitchen Mu shiryawa Yaya Khaleel abinci ' don ya kusa dawo wa, "What!!?" Cikin tsawa da muryar tsoro tayi magana ' Hakan yasa ta samu waje ta zauna a sanyaye tare da cewa, "Shikenan, ya dawo Lafiya ' basai na shiga harkar shiba sannan zansha wuya?" Shuru sukayi nadan lokaci sannan Ilham ta ce, "Please Fadwa kije kifara Kafin Ingama shiryawa ' koma mene ne sai indaura daga baya." Ok kawai Ta ce mata sannan ta fita daga Dakin Zuwa kitchen. *Around* *3:00pm* Bayan Fadwa da Ilham sun kammala Komai sun jera a dinning table ne ' Abba ya dawo Gida, "Anata preparation din dawo war Khaleel ne?" Yayi magana cikin sauri ya na k'ok'arin wuce wa sashen shi, Ilham ta d'ago kai ta kalle shi cikin sanyin jiki. "Eh Abba wai haka aka ce." Komawa sukayi suka zauna a harabar Parlor suna kallon, Yaya Farook ya shigo d'auke da leda Guda biyu a hannun shi ' Wurgama ko wannen su yayi Fuska a daure ya sami waje ya zauna. Cikin sauri Fadwa ta bude ledarta da kwalin waya ta fara hada ido ' xambur ta mike tsaye cike da murna, "Wayyoo Yaya Farook..." Juyowa tayi ta kalleshi cike da Fara'a, ganin ya daure fuska ne yasa Ta koma a zaune jiki a sanyaye. Itama Ilham bude nata tayi taga wayace ' sannan tayi mashi godiya, kai kawai ya daga Mata alaman Yaji ' sannan yace, "Yau Khaleel zai dawo Hope ' kun kammala komai." A tare suka amsa da cewa Eh, Sannan kowannen su ya mik'e tsaye d'auke da wayarshi a hannu suka wuce d'aki. Shima Yaya Farook tashi yayi ya wuce d'akin shi, yana shiga ya ciro wayar shi ' yayi dailing wata new Number. Fadwa na zaune bayan sun kunna wayan ' cikin jin dadi Itada Ilham sai taga kira ya shigo Wayar, "Kai!! Ilham harda Sim a ciki." Abunda ta ce kenan ' tayi saurin yin recieving call din, Sai jitayi ance. "It's Me Farook, kizo d'akina Yanzun nan." Yana gama fad'in haka ya kashe wayar, kallon Ilham tayi Cike da mamaki. "Wane ne?" Cewar Ilham, Smilling tayi mata ba tare da tace mata komai ba ' ta tashi ta bar d'akin, kai tsaye ta wuce dak'in Yaya Farook ' saida tayi knocking sannan ta shiga tare dayin Sallama, "Yaya Farook gani! Juyowa yayi ya kalleta ' sannan ya jawo hannun ta ya zaunar da ita a saman gadon shi, "I hope kinji dad'in Gift d'inda na baki?" Ya fad'a yana k'ok'arin zaunawa kusa daita, "Eh Yaya Farook na gani ' kuma na gode sosai" "Fadwa you completely changed my life ' koda nayi niyyar yin wani abun saboda Soyayyar ki sai inji nakasa, because i love you so much." Yana gama fad'in haka yayi kissing d'inta a goshi, "Tashi ki wuce d'aki, bazan iya jore ganin ki a nan wajen ba ' komai zai iya Faruwa Fadwa!!" Cikin Sanyin Murya yayi Maganar ' hakan yasa taji wani Yarrrrr a jikinta, da sauri ta mik'e sannan ta bar d'akin cikin hanzari. parlor ta wuce kai tsaye ' Suka had'e da Umma zataje kitchen, "Lafiya Fadwa? Naganki kamar Wacce aka biyo ne?" Had'd'iye miyau tayi daker, tare da zurowa Umma idanu tana tunanin k'aryar da zatayi mata. "Fad'amin mana, Don Fuskarki ta kasa boye tsoron da take d'auke dashi, " "Amm...well Umma babu komai ' and please don't worry about me, tsaka nagani a kitchen shiyasa naji tsoro." "To shikenan Allah ya kyauta." Ameen Ta ce sannan ta k'arasa Parlor ta zauna ' zamanta keda wuya taji ana Knocking K'ofa, tashi tayi taje ta bud'e. Cikin izza ya shigo Cikin parlon ' Fadwa baki ta saki ganin yadda ya shigo kai tsaye, "Malam lafiya? Kuma wa kake nema? " Juyowa yayi ya kallet ta cikin b'acin rai da jin haushin tambayar da tayi mashi, yasa ya dawo daff da ita ya tsaya tare da k'are mata kallo. "Ke? .." Kasa k'arasawa yayi saboda haushi, sannan ya juya zai k'arasa cikin gidan tayi sauri ta rike mashi riga. "Malam magana nakeyi ai...." Ji kake Tasss ' tun kafin ta gama rufe baki ya sharara mata mari, "ke!! Wace ce dazaki yimun irin wad'an nan tambayoyin, Koda yake dama haka y'an aiki suke ' To nine Khaleel kuma idan kika cigaba da Yimun tambayoyi dukan banza zakisha." Zukunna wa Fadwa tayi rik'e da fuskarta hawaye na gangaro mata ' Lallai ta tausayawa kanta jin Yadda sukayi Arba da Yaya Khaleel for the first time, Haka nan Ta share hawayen ta tare da mik'ewa tsaye. "kayi hak'uri Bansan kaine Yaya Khaleel ba... Tsaki ya ja gami da zama a saman kujera, "Naji kije ki kiramun mutanen gidan." Juyawa tayi ta nufi d'akin su ta iske Ilham a zaune, Ilham d'ago kai tayi ta kalle Ganin fuskarta babu annuri ne yasa tayi saurin mik'ewa tsaye, "Fadwa? Ya dawo ko?" "Hmm ya dawo mana ' tunda harya watsamin mari" Zaro ido tayi sannan ta fita d'akin cikin sauri ta nufi kitchen ta fad'awa Umma, sannan ta zarce d'aikin Yaya Farook shima ta sanar dashi ' ita dai Fadwa zama tayi a bakin gado ' cike da jimamin marin da tasha. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_P.W.F_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 *17-18* pages🌹 Bayan wucewar ta yayi sauri ya shiga cikin d'akin nasu, A kwance ya iske Fadwa rungume da pillow ta na bacci ' zuwa yayi ya zauna a gefen ta setin fuskar ta, a hankali yasa hannu ya shafa saman goshin ta tare da kissing d'inta a goshi. Sannan ya tashi ya wuce parlor, a zaune ya sami Umma da Abba suna hira ' zuwa yayi ya tsugunna ya gaishe su sannan ya koma ya zauna. "Ka karya kuwa Farook? Cewar Umma, "A'a Umma ban karya ba tukunna. Yaya Farook maida kallon shi yayi akan Abba ' sannan ya ce, "Ammm... Abba dama nazo ne natuna maka ' maganar Neman Aikin. "Kaga Farook na manta aigwara daka tunamin ' kaje d'akina zakaga Wani envelop ka d'auko min. Cikin hanzari ya tashi ya nufi d'akin Abba ' cikin minti Uku ya dawo d'auke da Envelop d'in rik'e a hannun shi, Sannan ya mik'awa Abba cike da ladabi. "A'a rik'e a wajenka domin nakane, Wannan itace takardar samun Aikin naka Farook. Murmushi yayi Har sai da hak'oran shi suka bayyana saboda jin dad'i ' cikin fara'a ya ce, "Thank you so much Abba, nagode sosai Abba ' Allah ya bani ikon kyautata maku. Ameen suka amsa a tare ' sannan Abba ya ce. "A Company din Abokina ka sami aikin ' gobe Insha Allah zan kaika. Cikin Farin ciki Ya tashi ya wuce d'akin shi ' nan ya dinga kiran Friends d'inshi suna Congratulating d'inshi. ya na gama wayar ya d'auki key d'in motar shi ya fita. *Around* *10am*... Fadwa ta farka daga bacci ' ta nufi bathroom tayi wanka sannan ta fito, Simple makeup tayi ta sanya doguwar rigar atamfa ' tukunna ta nufi parlor ta taradda Umma da Abba ta gaishe su sannan ta juya zata koma ciki Umma ta tsaida ita da cewa, "Fadwa yaya jikin naki? "Da sauk'i Umma. "To Allah ya k'ara sauk'i, Ameen ta ce sannan ta juya ta wuce. kai tsaye ta nufi Lambu ta zauna tare d'aga kanta sama tana kallon yadda Tsuntsaye keta safa da marwa a wajen, abun Yayi matuk'ar burge ta yasa ta tashi ta k'arasa cen cikin Lambun tana kallon tsuntsaye kala dabam dabam. Cikin ta ne ya fara mata k'ara sakamakon Karya wanda batayi ba, hakan yasa ta tsinki Tuffa(Apple) a wajen ta ci saida taji ta koshi sannan ta cigaba da kallon Cikin Lambun. Yaya Farook dawo wa gida yayi ' Ya shigo parlor babu kowa sannan ya wuce cikin gidan, d'akin su Fadwa ya fara lek'awa ganin bata cikine yasa ya tafi Lambun shima kai tsaye, A zaune Ya hangi Fadwa ita kad'ai Fuskar ta cike da Fara'a, Ya k'arasa wajen ' jitayi anrufe mata Ido. "Waye please? Ilham kece ko? Shuru yayi ya kyaleta ba tare da yace mata komai, "Mtsw Dalla malama ki sakemun ido na. sake mata ido yayi sannan ta juyo ta kalle shi, ganin shine yasa ta tsorata ta mik'e tsaye gami sakin k'ara, "Ahhghh, Yaya Farook kayi hakuri bansan kai bane. D'aure fuska yayi ya matso daff da ita, "Na sami Aiki Fadwa. "Wow! Alhamdulillah Yaya Farook naji dad'i kuma na tayaka Murna. Murmushi yayi Tare da tallabo fuskar ta da hannu biyu, "Fadwa ai kece yadace azo a tayaki Murna ' Domin Wannan samun aikin tamkar ke ce kika sameshi. Haka ya fad'a ya na k'ok'arin Kissing d'inta, "Yaya Farook what are you trying to do? Tayi tambayar gabanta na dukan uku uku, tana k'ok'arin Kub'uce wa ya k'ara matseta. "Yaya Farook please ka daina mana ' banajin dad'in hakan.... Cikin sauri ya saketa Tare da juya mata baya yana maida numfashi, itama ta juya tayi gami da dafe k'irjin ta hannunta na rawa ta ce, "Yaya Farook Am sorry but i just can't. "Yes bazaki iya ba ai ' saboda bakya sona Fadwa. Da sauri ta juyo ta kalle shi idanuwan ta sun kad'a sunyi jaaa. "Yaya Farook na dad'e da fara Son ka a cikin Zuciya ta , kad...... Bata kaiga k'arasa maganar ba Ya dakatar da ita da cewa, "Inhar kina sona dagaske ' to kije ki fad'awa Su Umma domin suyi mana Aure, Fadwa baxan iya jure rashinki a kusa dani ba. mamaki ne ya rufe ta ' yasa ta je Gaban shi ta tsaya, "Yaya Farook kada ka d'auramun nauyin da banice Ya dace insauke shi ba. Tana gama fad'in haka ta juya zata wuce yayi sauri ya rike hannun, "Fadwa bazan iya fad'a ma Umma da Abba ina sonki ba. Saurin fizge hannun ta tayi cikin bacin rai sannan ta juya ta wuce. D'akin su ta wuce direct ' tana shiga ta fada saman gado, wasu zafafan hawaye ke zubo mata a fuskar ta, "Wannan wace irin soyayya ce? Wannan wane irin azabtar wa ce? Dama haka Soyayyar take?.... Cikin kuka ta k'arashe maganar, tashi zaune tayi ta share hawayenta sannan ta wuce Kitchen ta daura girki. *** *** *** *** *** *AROUND* *1:56PM* Fadwa ta gama girkin ta zuba cikin Plask ' sannan ta kawo parlor ta ajiye, ta wuce sashen Umma ta fad'a mata cewa ta gama Abinci, koda ta dawo iske Yaya Farook tayi a dinning table a zaune ' yana kallon ta cike da murmushi, Kawar da fuskar ta tayi sannan ta k'arasa wajen cikin sauri ta Zuba mashi abinci, fuskarta babu annuri a cikin ta. Bayan tayi sarving d'inshi ne ta koma ta zauna Suna kallon kallo, "Bazaki zuba abincin bane? Shuru tayi ta kyaleshi sannan ta zuba ruwa a cup tasha, "Fadwa am i not talking to you? "Am not hungry! Abunda ta ce kenan ' ta mike tsaye da niyyar barin wajen yayi saurin tsaida ita, "Fadwa son da nake miki bashine zai hanani hukunta ki ba idan kikayi laifi. Cikin fad'a yayi maganar hakan yasa ta jin tsoro ' gudun kar jikinta ya dimamu ne yasa ta saki fuskarta tare da yin murmushi, "Yaya Farook don Allah ka barni ' wallahi banajin Yunwa. "Fadwa ban yarda ba ki dawo ki zauna,... Yana gama fad'an haka Umma ta shigo parlon cikin hanzari Fadwa ta boye a bayan ta, "O'o lafiya? "Umma, Yaya Farook ne wai dole sainaci abinci yanzu ' ni kuma banajin yunwa, "Ha'a Farook banason zalunci, antaba yin abune dole ne wai? sosa kai yayi Cikin fara'a Sannan ya ce, "Umma ni ban mata dole ba ni kawai... Tun kafin ya k'arasa Umma ta ce, "Yi tafiyar ki kinji ki kyaleshi, Saida tayi mashi gwalo sannan ta juya ta wuce. *2:00pm* Bayan sun gama cin abinci ' Umma ta dawo harabar parlor ta zauna' shi kuma Yaya Farook ya d'auki key din motar shi ya fita, Ilham ce ta shigo cikin parlon a gajiye ' Ta gaida Umma sannan ta nufi d'akin su, ta na shiga ta Iske Fadwa a zaune ta na duba handOut. Zuwa tayi ta jiye Handbag dinta sannan tace, "Ke baiwar Allah ya jikin naki? Ajiye handout din tayi a gefe ta d'ago kai ta kalle ta, "naji sauki kad'an Ilham. "To gwara da kika warke da wuri don gobe munada test din Anatomy. Cewar Ilham, "Tabb hmm Allah dai kawai ya taimake mu kawai. Ameen Ilham ta ce sannan ta dauki towel ta daura ' ta fada bathroom donyin wanka. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 *23-24* pages🌹 *Washe* *gari*.... Da sassafe around 6:22Am ' Fadwa da Ilham suka tashi sukayi Sallah, Bayan sun idar da sallah ne Ilham tayi wuff ta tashi tana k'ok'arin d'aura towel a jikin ta, "Ilham kada kiyi wanka yanzu ' saboda gyaran d'aki yana jiran mu." Cewar Fadwa, Ilham tsayawa tayi tana kallon Fadwa d'auke da alaman tambaya a fuskar ta, "Gyaran d'akin ina kuma? " "Gyaran d'akin Yaya Khaleel kuwa, domin kuwa ya ce yau da safe zamu gyara shi ' Ai auna arzik'i mukayi jiya don wallahi da jikinmu ya gaya mana." Tsaki Ilham taja ' tare da jan kwafa, "To wallahi ' babu wani gyaran d'akin da zamu tsayayi, don kuwa test garemu yau ' shi ya gama nashi karatun mu zaizo ya takura mAna, " "Tab!! To aini mantawa nayi banyi mashi bayani ba tun jiya d'in." Ya tsine baki Ilham tayi gami da buga cinyar ta, "ke kika sani, wallahi ki zauna nan harkisami Carryover ' shine na farko wanda zai jibge ki, " Fadwa mik'ewa tayi tsaye tare da yaye hijab d'in jikin ta, "To yanzu yaza'ayi kenan mu fita ba tare da kowa ya sani ba? " "Yanzu dai kibari inshiga wanka ' infito saike ma ki shirya. " Ilham harta juya zata shige bathroom Fadwa tayi saurin dakatar da ita da cewa, "Ilham Amma kinsan dai bazamu fita ba tare da ' mun shirya musu breakfast ba ko?" "Fadwa wai wane breakfast kuma? Bayan kinsan muddin muka tsaya tofa ' gyaran d'akin nan tamkar mun gama yin shine, kawai mubar musu Umma idan ta tashi saita had'a kokuma d'aya daga cikin su." Ta na gama fad'in haka ta shige bathroom ba tare da ta jira abunda Fadwa zata ce ba. A bakin gado ta zauna Tayi jugum ' babu abinda take tunowa sai irin marin da Tasha wajen Yaya Khaleel. "Anya kuwa Ilham zan iya bin shawarar ki kuwa? Haka ta fad'a idanuwan ta cike da tsoro. " *Some* *Minutes* *Later* Bayan Ilham ta fito daga bathroom ne Fadwa ta shige cikin sauri ' Tukunna Ilham ta fara Shiryawa. Yaya Farook saukowa yayi daga gado ' gami dayin mik'a sannan Ya fad'a bathroom cikin Sauri yayi wanka tare da yin Alwala, sannan ya fito yayi sallah. Bayan ya idar ne yaji cikin shi tamkar anyi mashi yasa aciki, Hakan yasa yayi saurin mik'ewa tsaye. "Ashhh wace irin yunwa ce da sanyin safiya haka? " Fita d'akin yayi cikin sauri, ya nufi kichen ' lipton ya fara nema baigani ba, ganin haka yasa Ya nufi d'akin su Ilham cikin sauri, "Ke zo ki had'amun Tea insha yanzun nan Yunwa nakeji, " Jitayi maganar ta daki zuciyar ta ' kallon shi ta juyo tayi, cikin k'unk'uni tace. "To, " Yaya Farook juyawa yayi ya koma d'aki ya cigaba da shiryawa, Ilham bayan ta kammala shirin tane ' ta je ta tsaya bakin Kofar bathroom, "Fadwa dalla kiyi sauri, inba haka ba wallahi Tafiyata zanyi ' kinga har Yaya Farook ya sani aiki ko? " Cewar Ilham, "Ke naji ' yanzun zan fito dalla, " Tsaki taja sannan ta wuce kitchen ' cikin d'an k'ank'anin lokaci ta had'a mashi ta kai mashi d'aki, "Yaya Farook ga tea d'in nan, " Nuni yayi mata da yatsa ' alaman ta aje saman side drower, Bayan ta ajene Ta juya ta wuce ' tana komawa d'aki ta iske Fadwa a zaune ta na Shafa mai, "Wai ke Fadwa kanki d'aya kuwa? amma kinsan dai sauri mukeyi ko?" Cikin hanzari ta tashi tasa kayanta sannan Tasha powder sama sama ' tukunna ta d'auki gelen ta yafa a kirji, "Tow Am done. " Ta fad'a rik'eda k'ugu ' sannan Ilham ta d'auki gelen ta itama ta yafa, suka fito parlor cikin sand'o har suka fita cikin garage ' Fadwa ce ta kwankwasa wa driver kofa, "Ka fito mun shirya! Cewar Fadwa, " Ba tare da wani b'ata lokaci ba driver ya fito, ya bud'e motar sannan suka shiga ' tukunna yayi hone mai gadi ya bud'e gate d'in suka fice. Bayan wuce warsu ne ' Yaya Farook ya fito rik'e da key d'in shi a hannu ya wuce Office,. Yana fita Umma ta fito daga sashen ta ita da Abba ' kallon dinning table tayi taga babu komai, "ha'a inasu Fadwa ne? Ya haryanzu basu Had'a breakfast ba?" Abba zama yayi a kujerar harabar parlor, "Kila basu gama bane da wuri, " Cewar Abba, Umma d'akinsu ta nufa ganin basa cikine yasa ta wuce kitchen domin duba, nan ma haka ' cikin hanzari ta Koma parlor, "Wallahi basa gidan, kardai sun tafi School ne yaran nan." "Kinga bara kawai in wuce wajen aiki ' zan karya acen, tunda kikaga haka to sunda uzri ne a gabansu." Yana gama fad'in haka ya tashi ya fita, Haka yai daidai da shigowar Yaya Khaleel parlor , a tsaye ya iske Umma tayi folding hannayen ta ' sannan ya zukunna cike da ladabi, "Umma ina kwana! " "Lafiya k'alau Khaleel ya gajiyan jiya? " "Lafiya lau Umma ' Umma lafiya na ganki haka? Yayi tambayar tare da mik'ewa tsaye, "Hm Khaleel al'amarin yaran nan ne yabani mamaki, School suka wuce ba tareda sun had'a breakfast ba." Cikin yanayi na mamaki yace, "what!! Lallai ransu zai b'aci yau, nasan wannan iskanci Wannan yarinyar ce Fadwa jikinta zai gaya mata. " Umma zatayi magana yai saurin taren numfashin ta da cewa, "Umma karki damu nima gwani ne a kitchen ' da lafiyata da komai bazaki shiga kitchen ba ina kallo. " Murmushi yayi mata sannan ya juya ya nufi kitchen ' indomie ya dafa cikin d'an k'ank'anin lokaci sannan ya kawo Ya aje a dinning table. Umma na zaune a harabar parlor ' tana kallon kai da komo wanshi, saida ya gama jera komai sannan ya dawo ya zukunna inda take zaune. "Umma ga abun karya war nan na kammala, " To Umma ta ce sannan ta tashi ta nufi dinning table ta zauna ' cikin hanzari yayi sarving d'inta sannan shima ya zuba, "Amm Umma Yaya ya tashi kuwa?" "Gaskiya banji motsin shiba Khaleel," Tashi yayi ya nufi d'akin Yaya Farook, ya murd'a kofar yaji a kulle sannan ya juya ya koma parlor. "Farook d'in na nan kuwa?" Cewar Umma, "a'a Umma k'ofar shi a kulle. " "Ohh Hakane yaune zai fara shiga Office," OK kawai yace sannan ya maida kallon shi a kan plate d'in indomie d'inshi ya cigaba da ci. *** *** *** *** *** *Around* *11:30am* Su Fadwa sun fito daga exam hall ' rik'e da handbag d'insu a hannu. "Yanzu inda munsan zamu gama da wuri ' aida mun sanarwa Driver, " Cewar Fadwa, "ai bari kawai in kirashi ' don naga inada Number d'inshi. " Ilham ciro wayarta tayi daga handbag d'inta tayi dailling number d'in Driver, "Hello, kazo ka d'auke mu daga school ' don munyi closing. " To kawai driver ya ce ' sannan ta kashe wayar, cikin hanzari driver yaje ya d'auko su daga school ' ya kawosu gida haka yayi daidai da fitowar Yaya Khaleel cikin Garage domin shan iska. Bayan su Ilham sun fito daga motor ne suna k'ok'arin shigewa gida, Yaya Khaleel ya dakatar dasu da cewa. "Where did you think you're going to????" Yayi maganar cikin yanayi na fad'a , a tsorace suka tsaya tare da juyowa suka kalleshi. "Yaya Khaleel ciki zamu shiga," Cewar Fadwa. "ciki ko? To kushiga!! Aike dama daga ganin kwayar idonki to baza kiyi kunya ba!!!. " Fadwa kallon Ilham tayi suka had'a ido sannan ta sunkuyar da kanta k'asa, "Ubanwa kuka mayar y'an iska??? Umma? Kokuwa Abba?? Ko kuma nida Yaya Farook?" "Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri ' zanyi maka bayani," Cewar Fadwa. "Zakimin shuru ko sai nazo na tattaka ki? To bari kuji infad'a maku, da zarar kun shiga ciki kun aje wannan kima kiman handbags d'in naku ku zarce d'akina ku jirani. " Tsoro duk ya gama cika Ilham idanuwan ta kuwa ' gabb suke da zubar da hawaye, d'ago kai tayi ta kalleshi gami dayin fuskar tausayi. "Yaya Khaleeel please.... Bata kaiga k'arasawa ba ya daka musu tsawa, "zaku b'ace mun da gani kokuwa?" Da gudu suka shige cikin gida ' cike da tsoro. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 *21-22* pages🌹 Umma kai tsaye ta baro kitchen Ta nufi parlor Ilham da Yaya Farook suna biye da ita ' Suna Isa cikin Parlon suka iske Yaya Khaleel a zaune ya d'aura k'afa d'aya kan d'aya yana kallon TV, Jin Sallamar su ne yasa yayi saurin Juyowa ya kallesu tare da mik'ewa tsaye cike da Farin ciki, Cikin sauri ya rungume Yaya Farook Cike da jin dad'i, "Yaya! Nayi kewar ku sosai wallahi" Cewar Yaya Khaleel, Murmushi yayi sannan suka sami waje suka zauna ' Yaya Farook yace, "Khaleel kenan ai muma haka ' and Yanzu ai Kewa ya k'are tunda gaka a gida," "Hakane Yaya!" Umma ce ta katse masu ' magana da cewa, "O'!! Hanta da jini kenan, To ai saiku tashi Aje aci abinci ' don nasan Khaleel da yunwa ka shigo." Dukkan su Dariya sukayi sannan suka mik'e tsaye da niyyar Zuwa dinning table Yaya Khaleel yaja kunnen Ilham gami da cewa, "Ke haryanzu rashin kunyar ki tana nan ko? Bakisan kimun sannu da dawo wa ba ko?" Saida ya bari Umma tafarayin gaba tukunnan ya zungure ta ' har saida ta fad'a saman kujera tukunna ya k'ara gaba. Cikin hanxari ta tashi kamar zatayi kuka sannan ta nufi dinning d'in. Bayan zauna wansu ne Ilham tayi Sarving d'insu , ta zubawa kowa sannan ta zuba nata ' saida suka fara ci sannan Umma ta lura Fadwa bata wajen, "Ilham me Fadwa takeyi ne ' da bazata zo taci abinci ba? " "Bara inkira ta Umma." Abin da Ilham ta ce kenan ta tashi ta bar wajen domin kiran Fadwa ' Yaya Khaleel kuwa Mamaki ne ya cika shi, "Fadwa kuma? To bakuwa mukayi a gidan?" Abinda ya ce kenan A zuciyar sannan ya cigaba da cin abincin. "Kaii!!.. Umma abincin nan yayi dad'i wallahi Kodon na dad'e banci abincin ki bane? " Cewar Yaya Khaleel, Murmushi Umma tayi ' Cike da fara'a ta ce, "Uhmm.. Khaleel kenan aibani nayi wannan abincin ba dakake ta zuba santi. " "To Umma wane yayi? Kardai kice Ilham ce tayi abincin nan." Tambayar ne ta bawa Yaya Farook dariya, "To mai ka maida Ilham ' ina gidan nan ace bata iya abinci ba? Aiko da taci najaki." Cewar Yaya Farook, "Ai Ilham da Fadwa sune sukayi maka wannan girkin." Tana gama rufe baki Fadwa da Ilham suka k'araso parlon ' cikin sauri bayan sun zauna ne Yaya Khaleel ya d'ago kai ya kalleta, "Umma wannan ce Fadwa d'in? Ita kuma wacece? Na d'auka y'ar aiki ce ai." Yayi maganar ya na kallon Umma, Nan Umma ta bashi labarin duk abinda ya faru ' da yadda akai ta dawo gidan da zama. Nan take tausayin ta ya kamashi ' cike dayin dana sanin Marin ta da yayi mata, Fuskewa yayi😎 sannan yace. "welcome to our house Fadwa," "Yaya Khaleel aini ba bak'uwa bace kai zan cewa haka ai," b'ata rai yayi ya maida kallon shi ga abinci, Shi kuwa Yaya Farook Ita kawai ya ke kallo cike da shauk'i, Umma ta na gamawa ta tashi ta wuce sashen ta ' ganin haka yasa Yaya Farook mik'ewa da niyar Wuce wa d'aki tare da cewa, "Dare yayi 8:00 yanzu ' idan kin gama kizo ki gyaramun gado na, don inaso inyi bacci ne. " D'ago kai tayi ta kalle shi suka had'a ido tasan cewa da ita yakeyi, Sannan ya juya ya wuce. Ilham cikin hanzari ta kammala cin abincin ta tashi da niyyar tafiya ' Fadwa tayi sauri ta rik'eta, "Please Ilham ki tsaya kid'an jirani na kusa gamawa. Yaya Khaleel d'ago kai yayi ya kalli Fadwa, " "A'a tunda kina zaune da aljani ai dole kice ta tsaya ta jira. " Maida kallon shi yayi akan Ilham wacce duk ta gama tsorata ' cikin tsawa Yace, "Come on ke kuma ki wuce kije ki kwanta ' tun kafin inb'ata maki rai a wajen nan. " Da gudu ta k'arasa d'akin, Fadwa kuwa kasa cin Abincin tayi ta tsaya tana kallon plate d'in. "Look! Idan kin k'oshi ne to ki tashi ki kwashe plates d'in don nagaji da ganin ki. " Cikin sauri ta tashi ta hau hahhad'a plates d'in wajen, tana cikin haka ne ta ture Cup da ruwa aciki ' sam batasan ma tayi ba, haka ruwan nan yadinga malalewa har ya sauka a jikin Yaya Khaleel ' shigar ruwa yaji a jikin sa yasa yayi sauri mik'ewa tsaye, "Kutma!! " Jin haka yasa ta juyo ta kalle shi a razane, "Fadwa jik'ani kikayi? Lallai jikin ki zai gaya maki." "Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri ' bada sani na nayi haka ba." Matsowa yayi kusa da ita ya d'aga hannu zai sharara mata mari kenan Abba ya dakatar dashi da cewa, "Karka kuskura , Koda wasa kada kasake ka mareta ' Au ashe muguntar taka tana nan ko? " Abba ya fad'i haka yana k'arasowa wajen, Yaya Khaleel sauke hannun shi yayi Sannan ya watsa mata harara ' tare da cewa , "zamu had'u ai. " Bayan Abba ya sami waje ya zauna ne ' yace, "Me kika masa? " "Abba Ruwane ya zuba a jikin shi by mistake ' shine yace... " Bata k'arasa ba ta sunkuyar da kai, "Kyaleshi ' karki damu dashi, Yanzu dai zo ki zubamun abinci na ' don yau na wuni ina aiki. " To kawai ta ce sannan ta zuba abincin a plate ta aje mashi ' Tukunna tayi mashi sallama don bacci takeji, har ta kama Hanya zata wuce Yaya Khaleel ya ce. "Ki biyoni da trolley d'ina d'akina" Babu musu taja trolley d'in nashi tabishi dashi ' tafiya yake ta na binshi abaya, ganin sun wuce d'akin Yaya Farook ne yasata mamaki. "Mun bani, i thought d'akin Yaya Farook zai kwana ' innalillahi kenan yanada d'aki dabam wanda bamu gyara shi ba. " Haka ta fad'a a zuciyarta jikin duk yayi sanyi, suna isa bakin k'ofar Yaya Khaleel yasa hannu ya bud'e d'akin ya shiga kai tsaye sannan itama tashiga, tsayawa yayi yana k'arewa d'akin kallo ranshi abace ' ganin haka tasan cewa lallai yau zasuci ubansu hakan yasa ta fara zubda hawaye tunkafin ya yanke hukunci. "Yanzu haka ake gyaran d'aki agarinku??" shuru tayi ba tare da ta ce komai ba ' jin haka yasa shi juyowa a fusace, "Fadwa ba dake nak....." Kasa k'arasa maganar yayi ganin yadda hawaye kebin fuskarta, cikin hanzari ya matsa kusa da ita tare da cewa. "Fadwa are you Okey?" "Yaya Khaleel don Allah kada kabigemu ' wallahi aikine yayi yawa shiyasa muka manta da gyara d'akin, kuma ni nad'auka tare da Yaya Farook zaka rik'a kwana....." Tana gama rufe baki yayi saurin rungume ta ' tare da shafa bayanta, "is Okay! Fadwa ki daina wannan kukan ' tunda banyi bugunba tukunna. " Yadda take ta mutsu mutsune ' ya gane cewa batason Hugging d'inne, Raba jikin shi yayi da nata gami da cewa, "Yanzu dai kije ki d'auko min bed sheet, sai kizo ki samun a gadon inkwanta kafin gobe sai ku gyara." Ok ta ce sannan ta juya ta fice cikin hanzari ' bata wani b'ata lokaci ba ta dawo d'auke da bed sheet a hannun ta ' ta mik'a mashi ya karb'a gami dayin kissing d'inta a goshi hakan yasa ta zaro ido, "is a normal thing ' so don't fall in love with me, don nasan halinku Y'an nigeria ' saboda haka zaki iya tafiya." Yana fad'in haka ta kama hanya ta wuce d'aki ta kwanta, Kwanciyar ta keda wuya ta tuna maganar Yaya Farook ' da sauri ta tashi zaune, Ilham dake kwance ta na chatting ne tace. "Lafiya kuwa ?" "Lafiya kalau kitchen zanje don k'ishi nakeji." Ok kawai Ilham ta ce sannan Fadwa Ta tashi ta nufi d'akin Yaya Farook, Handle d'in ta murd'a taji a k'ofar a bud'e yasa ta shige cikin sauri. Akwance ta hangi Yaya Farook hakan yasa ta kiran sunan shi, "Yaya Farook" Jin yayi shuru ne yasa ta k'arasa cikin d'akin tare da cewa, "To ko yayi bacci ne?" Hayewa tayi har tsakiyar gadon shi ' sannan ta sunkuya tana kallon fuskar shi, bata ankara ba taji ya jawo ta jikin shi, lips dinta daff da nashi ' haka yasa ya matse ta sosai yadda bazata iya Kuccewa ba ' nan fa ido Ya raina fata, "Yaya Farook na d'auka ko kayi bacci ne shiyasa." Ta fad'a tana k'ok'arin janye jikinta, "Yau anan nakeso ki kwanta ' Inaso ki d'ebemun kewa Fadwa," "Yaya Farook please ka bari intafi ' kasan banason irin wad'an nan abubuwan." Ta fad'a tare da yi mashi magiya, "Ke ! Am serious fa ' Karma ki bari raina yab'aci." Ya fad'i haka cike da d'aure fuskar. Murmushi tayi mashi tare da kashe mashi ido d'aya (wink), Sannan ta sa hannu a k'irjin shi ta fara yinmashi waiwayi a Wajen, Nan take ya farajin launin jikin shi yafara sauyawa ' cikin wata murya yace, "Fadwa stop it ' kidaina yimin wannan abun please," "A'a" Ta fad'a saida ra bari ya sakan kance sannan tayi wufff ta sauko daga gadon ' cikin Sauri har tana had'awa da gudu tabar d'akin, Yaya Farook Sai ninshi yakeyi yana mutsu mutsu. D'akin su tashige a guje ' har saida Ilham ta razana, "ke kuwa ina kika shiga? Don na je kitchen ban ganki ba," Fadwa kwanciya tayi gami da jan blanket ' sannan tace, "Well, Ilham lambu naje." "lambu da daddaren nan Fadwa?" "yes ' fruit naje nasha, A tsorace na dawo shiyasa Ma kika ganni a haka." "ke kika sani dai." Abunda tace kenan ta maida kanta akan waya ' nan bacci yayi awon gaba dasu. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 @ *_I_* *_proudly_* *_dedicated_* *_this_* *_page_* *_to_* *Jameesha* & *Husna* *_Good_* *_Friends_* *_Are_* *_Hard_* *_to_* *_Find_* *_Difficult_* *_to_* *_Leave_* *_Impossible_* *_to_* *_Forget_* *_Nikam_* *_babu_* *_abinda_* *_zance_* *_sai_* *_godiya_*...*_dana_* *_sameku_* *_a_* *_matsayin_* *_Friends_* *25-26* *pages*🌹 Suna shiga cikin parlor suka iske Umma a zaune tana kallo ' basu san lokacin da suka tsugunna a k'asanta idanuwan su ciccike da hawaye, " Umma don Allah kicewa Yaya Khaleel karya dake mu! Cewar Ilham," Umma rage k'arar TV d'in tayi da remote sannan ta kalli Ilham, "Ai bansan bakida Kunya ba sai yanzu Ilham ' inbanda kun raina mutane kwatafi ba tare da kun had'a mana abin karya waba? " Sunkuyar da kai Ilham tayi Hawaye kawai ke zubo mata, "Umma don Allah kiyi mana Hakuri ' wallahi Uzri mukeda shiyasa amma insha Allah haka bazai maimaita kanshi ba, " Cewar Fadwa, "Au kema zaki nunamin taki rashin kunyar kenan ko? Ai Fadwa koma wane irin Uzri ne daku ' ai kamata yayi Wani cikin ku yazo yaimun bayani, bawai ku kad'a kanku ku fita ba." Umma na gama rufe baki Ilham taji saukar dundu a bayan ta, a kid'ime suka waiga domin suga waye ' Haba ido hudu sukayi da Yaya Khaleel, haka yasa suka tashi a guje tare da cillar da handbags d'insu zuwa d'akin shi. Suna shiga d'akin shi suka zube a k'asa Cike da tsoro, Yaya Khaleel kwafa yayi gami da girgiza kai sannan ya biso. "To banda mugun duka dai ' don nasan halinka. " Cewar Umma, Kai tsaye ya zarce d'akin shi ba tare da yacewa Umma komai, Cikin zafin nama ya bud'e k'ofar ganin su yayi a zukunne kowan nen su da hawaye sharkaf a fuskarshi, fuskar nan tashi a d'aure ya nufi wardrope dinshi ya zaro belt ' da Fadwa ya fara had'a ido sannan ya nufo kanta, ganin haka yasa tayi zambur ta mik'e tsaye. "Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri ' Karka dakemu please...." Cikin kuka ta k'arashe maganar ta cike da shash shek'a, "Ohhh Kokowa xamuyi koh? Aike dama nasan babu abinda bazaki iya ba.... " Jikake zafff zafff ' saukar belt a bayan ta, Da gudu ta nufi wajen gadon shi ta rakub'e cikin kuka tace. "wayyo!!! Yaya Khaleel don Allah kayi hakuri please forgive us....." Komawa kan Ilham yayi wacce ko ina najikin ta rawa yakeyi, "Ke dan ubanki ' da hankalin ki da komai, zaki biyewa wancen tsageran? saboda kin manta wanene Yaya Khaleel ko? To jikinki zai fad'a maki kuwa." Sai da ya sauke mata belt shida a jikin sannan ' ya k'ara mata da hauri a jikin ta, saboda tsabar kuka Ilham ko hawaye ya daina fita daga idonta. "Tashi ki fita ki bani waje ' idan ba haka ba saina kakkarya ki a wajen nan. " Da gudu Ilham ta bar d'akin jin haka yasa Fadwa mik'ewa tsaye Cikin sauri zata fita, ya cafko ta A gigice ta juyo ta kalle shi. "ina kike tunanin zaki? Ba tareda jikin ki ya gaya maki ba? Mara kunya!!!" Jin saukar belt tayi a k'afa funta ' yasa tayin tsalle cikin rad'ad'i ta k'ank'ame shi jikinta sai rawa yakeyi, "Ya..Yay. Yaya please kaimin afuwa ' wallahi zan iya mutuwa...." Wani zirrr yaji tundaga k'afar shi har saman kanshi, shuru yayi nad'an lokaci sannan ya finciko ta da karfin tsiya har saida ta fad'a k'asa, a hankali yake takowa inda take ' ganin ya nufo ta da belt d'in ne hankalin ta ya k'ara tashi , "Yaya wallahi wannan ba plan d'ina bane Ilham ce tace muyi haka, please karka kasheni. Jin haka yasa shi tsayawa cak ' tare da wullar da belt d'in a saman gado, "Tashi ki fice mun da gani ' gobe idan Ilham tace ki shiga wuta sai ki shiga...." Da sauri ta mik'e tsaye gami da had'awa da gudu ta fice daga d'akin, ba ta tsaya ko ina ba sai a saman gadon su. Saida ta gama dawo wa normal sannan ta lura da Ilham rik'e da bucket d'in ruwan d'umi a hannunta tare da K'aramin towel tana gasa jikinta, "Ilham?" A gajiye Ilham ta juyo ta kalli Fadwa, "Ya akayi?" Fadwa tashi tayi ta zauna cikin jin zafin jikin ta, "Meyasa Yaya Khaleel ya tsane ni?" "Mtsww wannan wace irin banzar tambaya ce ' ni dalla ki kyaleni naji da d'aya mana aida kinsani kin tambaye shi kafin ki fito.!" Ya tsine baki tayi sannan ta tashi ta fada bathroom don yin wanka da ruwan d'umi, ko da ta fito bata iske Ilham a d'akin ba nan ta d'aga kai ta kalli a goge, "Ok! Lokacin girka lunch yayi 2:00pm Ilham na kitchen yanzu. Bayan ta zauna agaban mirror ne ta fara gyara jikinta ' wayar ta tayi k'ara, cikin hanzari ta d'auka ganin Yaya Farook ne yasata yin picking cikin sauri. "Hello Yaya.." "Baby na yakike? Hope kina lafiya?" A wahale ta ce, "lafiya kalau Yaya" "Meyasa meki naji kamar bakida lafiya Fadwa!" Jitayi kamar ta fad'a mashi abinda ya faru sai kuma ta fasa, "Well, Yaya Farook babu komai ' is just that nad'an sami bacci ne d'azun. . Ok yace tare da yinmata sallama sannan ya kashe wayar ' a tsanake ta tashi ta sanya kaya ajikin ta doguwar riga atamfa, sannan ta fito ta nufi parlor ganin Yaya Khaleel tayi a zaune ' nan take cikin ta murd'a ta juya xata koma ya dakatar da ita da cewa, "Kije ki gyaramun d'aki na yanzun nan kuma ke kad'ai. To tace sannan ta juya ta nufi d'akin shi, bayan y'an lokuta k'alilan ne ta dawo parlon ta zauna tare da cewa, "Yaya Khaleel na gama. ok ya ce ba tare da ya d'ago kai ya kalleta ba. *Around* *2:30pm* Ilham ta gama jera abinci da duk wani abun buk'ata a saman dinning table , sannan ta haura sama ta yiwa Umma magana ' hakan yayi daidai da dawo war Abba daga wajen aiki, Fadwa da Ilham da sauri suka tunkari Abba tare da yi mashi sannu ' sannan Fadwa ta karb'a bag d'in hannun shi ta kai sashen shi, Yaya Khaleel ya tare Abba cikin ladabi ya zukunna a gaban sannan ya ce, "Abba sannu da dawo," Yawwa Abba ya fad'a sannan ya nufa dinning ya zauna, tukunna Umma ta fito cike da fara'a a fuskarta ta zauna gami da yiwa Abba sannu da dawowa, Ilham ce ta tashi donyin sarving d'insu Fadwa tayi saurin karb'ar Spoon d'in tare da cewa, "Ai Abba nane so kibari na zuba mashi," Nan Ilham ta koma ta zauna gamida balla mata harara ' Abin haushi ya bawa Yaya Khaleel yasa yaje ya zauna awajen , "Ke kiyi ki zuba min yunwa nikeji!" Ya fad'a a gadaran ce ' Abba ya kalle shi, "banson takurawa fa Khaleel ' hannu biyu gareta ba takwas ba. Saida Fadwa ta zubawa kowa tukunna ta nemi waje ta zauna ta fara bawa ciki abinci , saida kowa ya kammala sannan Ilham ta tashi ta tattara plates d'in wajen ta wuce kitchen dasu. Umma da Abba tashi sukayi suka tafi sashen su ' Yaya Khaleel kuma ya fita harabar gida don shan iska, fitar shi keda wuya Yaya Farook ya dawo ' shigowa yayi tare da yin sallama, Fadwa da ke a zaune ta amsa mashi cike da fara'a. "Baby na ke kad'aice a parlon?" Yayi tambayar a gajiye gamida zaunawa, "Eh ni kad'aice Yaya, In zubo maka abincin ne?" Juyowa yayi ya sakar mata wani kallo ' tare da yin murmushi, "Yes, but ki zubomin ki kawomin d'akina." To tace mashi sannan ta yunk'ura ta nufi kitchen kasan cewar Ilham ta tattara komai ta kai kitchen, koda ta je kitchen babu kowa har Ilham ta gama ta wuce d'aki. Cikin hanzari ta zuba abincin d'an daidai a plate tare da d'aukar roban ruwan sanyi ta nufi d'akin Yaya Farook ta aje masa a saman side drower sannan ta juya zata fita ya turo k'ofar, a tsora ce taja dabaya ta tsaya Yaya Farook ya k'araso daff da ita gami dayin mata kiss tare da rungume ta. "i missed you so fucking much Fadwa!!" Nan take ta saki wani k'ara cikin sauri ya saketa gamu da tallabo fuskarta nan yaga idonta yayi jaaa Alaman daf take dayin kuka, "Babyna lafiya? Ko dai bakida lafiya ne?" Yayi tambayar yana kallon Cikin idonta, "Yaya Farook ' ka famamin inda aka dakeni ne d'azun!" Nan ya waro manyan idon shi ' cike da mamaki, "What!!! Waye ya dakeki??" Ranshi abace yayi tambayar ' sunkuyar da kai kawai tayi hawaye na d'iga a hankali...... *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄✌ [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *27-28* *pages*🌹 Sake tambayar ta yayi cikin tsawa, "Nace waye ya dake ki!!!? Ranta abace ta d'ago kai ta kalleshi, " "Waye zai dake ni idanba Yaya Khaleel ba!! " Jin haka yasa jikin shi yin sanyi ' Cikin d'an k'ank'anin lokaci ya ce, "hm Fadwa ai bakwajin magana ne ' ni nasan Bro ba zai dake ki haka nan ba, sai idan kinyi laifi." Tsayawa tayi tana kallon cikin kwayar idon shi cike da mamaki, "I know that Yaya Khaleel d'an uwanka ne and ni ban fad'i haka da wata manufa ba and beside kai ne ka nemi kasani. " fuuuu ta juya zata fita yayi saurin rik'e mata hannu, "I know that you're hurt Fadwa ' but ki kiyi hak'uri bazan iya cewa Khaleel komai ba. " "Is OK, na fahimta. " Fizge hannun ta tayi ta fice daga d'akin , har ta nufi d'akin su sai kuma ta juya ta nufi d'akin Yaya Khaleel ' kasan cewar tasan cewar baya d'akin yasa ta bud'e Kofar a hankali gami da yin sand'o, ta na shiga ta tura ta rufe. Ciki ta k'arasa cikin izza ' ta hango Album a saman gadon shi tare da diarry d'insa a gefe. Cikin sauri ta hau saman gadon ' gami da d'aukan Album d'in ta d'ora a cinyarta, ( *Ohh* *Ni* *Seemaluv* *kodai* *Fadwa* *ta* *mance* *d'akin* *da* *shiga* *ne*?) Budewa takeyi a hankali ta na kallon hotunan shi da abokanan shi mata da maza, haka taita kallon hotuna daga wanda zai bata dariya sai wanda zai bata haushi ' a haka har ta bud'o wani hoto, ganin hotun yasa gabanta fad'uwa. "Dama Yaya Khaleel haka kake? Daman abunda kake tsina nawa a American kenan? Wannan kuma wacece to!!. " Hoton cikakkiyar mace ce kyakkyawa ' haihuwar Uwarta, wacce babu kaya ajikinta ta na zauna. Cike da tsoro Fadwa ta rufe Album d'in tare da jan dogon tsaki, "Mtsww wannan wace irin rayuwa ce? Yanzu shi kuma Yaya Khaleel me yakeyi da wannan picture d'in?" Ta fad'a cike da takaici ' sannan ta jefar da Album d'in a gefe ta d'auki Dairy d'in. Bayan ta bud'e ne taga An rubuta, (Dear Diary...) A America ; ranar Litini ce na tafka babban kuskuren da ban tab'a tunanin zan tabka shiba a rayuwa ba, haka yasa duk idan na tuna dashi nakan zubda Hawaye..... Fadwa bata kaiga k'arasawa ba taji an bud'o k'ofa bamm , da k'arfin tsiya hakan yasa ta razana ta mik'e tsaye cikin rawar jiki rik'e da Dairy d'in a hannun ta, Yaya Khaleel tsayawa yayi cak yana kallon ta cikin mamaki cen ya hangi Dairy d'in shi rik'e a hannun ta hakan yasa shi k'arasowa wajen ta cikin zafin nama da b'acin rai, "Uban me kike min a d'aki? Ke wane irin stubbornness ke damun ki?" Ya fad'a tare da kama kunnen ta, "Ahhhggh Yaya Khaleel please am sorry ' zaka ciremun kunne!!!" Ta fad'a Idonta cike da hawaye, Yaya Khaleel ya fizge diary d'in nashi gami da cewa, "Bincike kike yimin dama? Da kikayi binciken ubanme kika binciko fad'amin, Iyee fad'amin nace!!!!" Ya k'arashe maganar cikin tsawa, hakan yasa ta fashewa da kuka ' don kuwa tasan idan har tayi wasa to kuwa wani dukan zata sake sha, "Yaya Khaleel don Allah ka tsaya kaji ' wallahi Allah ba bincike nake yi maka ba Yaya Farook ne ya ce inje in nemo masa biro, shine nazo nan ina dubawa....." Ta na gama rufe baki ya d'auke ta da mari tasss, a gigice ta dafe wajen tare da sakin k'ara, "Ahahhgg..." "Ke!! Ni zakiyiwa k'arya da rainin hankali? Kaff d'akin ku babu mai Biro sai kin shigo nan? Iyeee ba tambayar ki nakeyi ba??" Kwata kwata kasa magana tayi saboda kukan da yaci k'arfin ta, girgiza kai kawai takeyi Alaman a'a. "In banda ke kin gama raina mutane ' Diary na a hannun ki sannan ki dubi tsabar idona kice Biro kikazo nema, Kakkarya kine kawai yau bazanyi ba Fadwa." Sakin ta yayi ya nufa Wardrope d'inshi ganin haka ya bata damar fallawa a guje ta bar d'akin , kai tsaye ta wuce d'akin su cikin tsoro ta tura k'ofar ta rufe da key. Ilham wacce keta waya tun d'azu ne ganin halinda Fadwa ke ciki yasa ta yanke wayar ta cillar da ita saman gado, tayo kanta cikin hanzari. "Lafiya Fadwa? Meyasa meki?" Tayi tambayar tare da d'ago fuskarta, nan ta ga shedar hannu Alamun mari. "Subhanallah meya sameki? Waya mareki! Halan Yaya Khaleel?" Nin shi kawai Fadwa keyi sama sama ' saboda azabar da takeji a fuskar, Ilham rik'e hannun Fadwa tayi sannan tajata zuwa gado. "Fadwa idan akwai wanda ya dace ki fadawa damuwar ki to ni'ce, " d'ago kanta tayi ta kalleta da rinan nun idanun ta, "Ilham d'akin Yaya Khaleel na shiga ni karan kaina bansan meya kaini ba, Bayan na shigane ya iske ni aciki shine yayi mun wannan mugun marin ' Ilham wai meyasa Yaya Khaleel ya tsane nine? Meyasa kokad'an baya d'aukata amatsayin k'anwar sa?" D'an k'aramin tsaki Ilham taja sannan ta rungume Fadwa tare da bubbuga mata bayanta , "Amma dai Fadwa kinsan ko wajen Abba za'aje kece bakida gaskiya ko? Kuma tunda kinsan cewa ya tsaneki ai sai guji fad'awa tarkon shi, kuma sanin kankine gidan nan babu mai nuna miki banbanci ' yadda akemun haka kema ake miki.." Saurin share hawayen ta tayi tare da cewa, "Nagode Ilham ' lallai kin cika y'ar uwa, " Ilham tashi tayi ta wuce parlor, Fadwa kuwa a zuciyar ta tace . "Naji duk abinda kika ce Ilham ' amma ni gaskiya koda zai kakkarya nine kamar yadda yace, to fa saina binciko abinda Yaya Khaleel ke b'oyewa a diary d'innan. " Nan ta tashi ta fad'a bathroom ta wanke fuskarta sannan ta wuce parlor, suka ci gaba da kallo. *** *** *** *** *Around* *4:30pm* ... Su Fadwa na zaune a parlor suna kallo Umma ta shigo parlon ' bayan ta zauna ne ta ce, "Aikin ku kenan kallo ' to kun d'aura girkin yamma ko?" Fadwa cike da fara'a ta juyo ta ce, "A'a Umma ai d'azu tare muka had'a mukayi, "yawwa aiko kun kyauta, yanzu ku tashi kuje ku kira Farook da Khaleel ' Abban ku keson magana daku gaba d'aya. " To sukace a tare, sannan suka tashi suka tafi ' ba tare da wani b'ata lokaci ba suka iso parlon, Umma na ganin sun iso ta tashi ta haura sashen su don kiran Abba. Yaya Farook da Yaya Khaleel a k'asa suka zauna cike da ladabi, su kuwa su Ilham suna saman Kujera don ita Fadwa ma harda hard'e k'afafu d'aya kan d'aya Yaya Farook ya d'ago kai ya kallesu, "Wane irin iskancin banza ne? Ba ankira mun nan don su Abba zasuyi magana damu bane? Shine kuke zaune d'are d'are a saman kujera?" Jin haka yasa Yaya Khaleel juyowa ya watsa masu wani irin kallo ' ai tuni suka sulale k'asa cike da nutsuwa. *Dedicated* *To* *My* * Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *29-30* *pages*🌹 Suna cikin haka ne Umma da Abba suka shigo parlon ' cikin kamala suka sami waje suka zauna daga bisani Abba yayi gyaran murya, "Ba komai ne yasa nace ku hallara anan ba ' illa maganar da zanyi wacce bata wuce uku zuwa hudu ba, wacce kuma ta k'unshi had'in kanku baki d'aya." Abba gyara zama yayi sannan yace, "Zan fara da kai Farook! Well Alhamdulillah yanzu ka sami aiki ' to me kuma ya dace kayi yanzu?" Sai Umma tace, "Aure!!" Yaya Farook yana jin haka ya d'ago kai ya kalli Fadwa, ya ga itama shi take kallo cike da fara'a sannan Abba ya cigaba da cewa, "nayi tunanin in had'a ku kai da Fadwa aure amma sai Umman ku ta ce had'in baiyiba ina ma laifin a had'a Khaleel da Fadwa? Dana duba sai naga Eh shawarar da ta kawo tayi, Amma nan da Two weeks kai Farook mukeso ka kawo mana wacce zaka aura!." Jin haka gaban Yaya Farook ya fad'a, ita kuwa Fadwa idanuwanta cike suke da hawaye ' Yaya Khaleel kuwa ai abun ba'a magana don kuwa zuciyar shi tuk'uk'i kawai takeyi. "Ke kuma Ilham yanzu kina iya bawa samarin naki damar zuwa domin ku fahimci juna ' amma mind you ba kowane zaki kawo cikin gidan nan ba!" Bayan ya gama ne Umma ta ce, "Ko kunada abun cewa game da wannan zabin?" Yaya Farook gyara zama yayi tare da kai zuciyar shi nesa ya ce, "Umma & Abba, bamuda abin cewa illa mu gode maku domin kuwa farin cikin ku shine farin cikin mu ' bak'in cikin ku kuwa! Shine namu, saboda haka wannan zab'in yayi." Abinda Yaya Farook ya fad'a yayi matuk'ar tab'a zuciyar Fadwa, hakan yasa ta farajin jiri na d'ibarta. Abba da Umma sunji dad'in kalaman Yaya Farook sosai ba kad'an, "Allah yayi maku albarka ' Allah kuma yasa naku y'ay'an suyi maku biyayya," Ameen suka ce sannan Umma tayi musu umarni da su tashi su tafi, bayan sun tashi Fadwa taji jiri na d'ibarta harta kaiga babu abinda take gani a gabanta face duhu ' hakan yasa ta yanke ji zata fad'i Ilham tayi saurin rik'eta. Cikin tashin hankali Umma da Abba suka yo kanta, "Innalillahi lafiya Fadwa? Meke faruwa ne?" Cewar Umma!, Yaya Farook ne yayi saurin sanya yatsun sa guda biyu wajen hancin ta, "Subhanallah bata numfashi, Khaleel yi maza kaje ka tada mota akaita hospital. " Cikin hanzari Yaya Khaleel ya fice ' Abba kuwa duk ya gama rud'ewa domin daka ganshi zaka gane cewa yana cikin tashin hankali, "Fadwa don Allah kada ki mutu ' banason rasaki amatsayin y'a kamar yadda Allah ya d'auke min mahaifinki amatsayin amini!" Cewar Abba, "Don Allah mai gida ka kwantar da hankalin ka ' insha Allah Fadwa rayayya ce in Allah ya yarda," Yaya Farook d'aukar Fadwa yayi cen caka kaff d'aukar jarirai, yaje ya sata a mota sanna ya dawo ciki ya Umarci Ilham taje ta d'auko gelenta, bata tare da wani b'ata lokaci ba tadawo rataye da gele a k'irjin ta sannan suka fice ita da Yaya Farook , har Umma zata bisu Abba yayi saurin rik'ota, "Bazakije a haka ba! Ki kintsa tukunna sai mufita tare . " Ya fad'a tare da samun waje ya zauna sannan Umma ta haura sashen ta domin kintsawa, cikin hanzari ta Umma sauko parlon sanye sa hijab d'inta a jiki, "A'a ki dakata tukunna harsai sun dawo sannan mu tafi baki d'aya," To kawai tace masa sannan ta sami waje ta zauna gami dayin tagumi. Bangaren su Yaya Farook kuwa tunda Khaleel ya tada mota suka wuce gudu kawai yake zabga wa ' cike da tausaya wa Fadwa. Cikin d'an k'ank'anin lokaci suka isa asibiti, bayan sunyi packing ne Yaya Farook ya fito cikin zafin nam ya d'auki Fadwa sannan suka shiga ciki, suna shiga ne sukayi kicib'us da Doctor zai shiga wani Ward d'in Yaya Khaleel ya tsaidashi, "Doctor!!! Please wait you have client here!!." A tsanake likita ya juyo ya kalle su sannan ya kwalawa Nurse kira ' cikin hanzari tazo wajen, "Yes Sir! "Ki hanzarta ki basu Ward ' kafin inzo yanzu! OK tace sannan tayi masu jagora zuwa d'akin, bayan Yaya Farook ya kwantar da ita Nurse d'in ta fita zuwa kiran Doctor ' Ilham na zaune a gefen Fadwa, "But Yaya baka tunanin Zab'in nan dasu Umma sukayi ne yajawo wa Fadwa wannan abin?" Cewar Yaya Khaleel, "What!!!? Karda insake jin wannan maganar daga bakinki Khaleel!! Ai duk abinda su Umma suka yanke shine daidai, " "But nifa Yaya gaskiya bana son ta," Yana gama rufe baki ya d'auke shi da mari tasss, "Ashe bakada hankali Khaleel?" "Kayi hak'uri Yaya, nayi kuskure insha Allah bazan sake ba!" Ya na fad'in haka ya tashi ya fice ya nufi wajen mota yayi zamansa, bayan fitar shine likita ya shigo ward d'in kai tsaye ya zarce inda Fadwa ke kwance ' stethoscope yasanya a k'irjin ta domin sauraron Numfashin ta, sai da ya kammala sannan ya cire ya juyo ya fuskanci Yaya Farook. "wato tayi doguwar suma ne, Amma insha Allah nan bada dad'ewa ba zata farfad'o." . "To likita thank you so much," "You are welcome ' yanzu zan turo Nurse tazo tayi mata settling IV fluid, " OK kawai Yaya Farook yace sannan Likita ya fita, cikin d'an k'ank'anin lokaci Nurse tazo tayi mata settling drip, sannan ta fita. *Around* *6:42pm* Yaya Khaleel ya shigo cikin ward ' ya sami Yaya Farook zaune a kujera, "Yaya wai har yanzu bata farka ba?" "Eh wallahi Khaleel," "Yaya yanzu kamata yayi mutashi ita Ilham a maida ita gida ' don taje ta d'an shiryowa Fadwa abinda zataci , bayan Munyi sallah sai mu taho da su Abba gaba d'aya ' nasan kafin nan ta farka." "Hakane Khaleel muje!! Yaya Farook mik'ewa yayi suka fita Ilham ta bi bayansu, fitarsu keda wuya Fadwa ta bud'e ido cike da kasala haka yayi dai dai da shigowar likita. "Alhamdulillah ina y'an uwan naki?" Yayi tambayar tare da dafa k'arfen gadon nata, kai kawai ta girgiza mashi sannan ya ce. "Oh may be lokacin da kika farka basu nan ' bari inje sallah in dawo, Abinda ya fad'a kenan ya juya zai wuce tayi saurin tsaida shi da cewa, "Doctor!! Please meke damuna? Juyowa yayi ya kalleta tare da sanya hannun shi a aljihu, "A yadda na fahimta ' kamar kinsami wani bad news ne wannan ne kad'ai zai iya samar da shock a jikin d'an adam harta kaishi ga suma," "haka ne doctor tabbas bad news ne nasamu ' but please doctor can you do me a favor?" Tayi tambayar tana kallon kwayar idon shi, "For what? "Doctor please ' idan y'an uwana sukazo kace masu na suma ne saka makon ciwon kan da yasami cikin d'an k'ank'anin lokaci please." "is Ok i can do that for you ' akwai wannan sirrin tsakanin Doctor da patients d'insa, so you don't have to worry about that." Murmushi tayi masa tare da cewa thanks ' sannan ya fice. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *31-32* *pages*🌹 Bayan sun Isa gida ne ' Yaya Khaleel yayi packing motar Ilham ta fito sannan su kuma suka wuce masallaci, Ilham tana shiga ciki ta iske Umma a zaune ' jin motsine yasa Umma d'ago kai ta kalle ta a razane, "Haba Ilham ki shigo haka babu Sallama? Yaya jikin Fadwa?" Ilham samun waje tayi ta zauna ' sannan tace, "Umma Fadwa insha Allah zata sami sauk'i, likita ya ce zata farka bada dad'ewa amma mudai har muka baro ta bata farka ba😢." Umma hannu biyu tasa ta rufe bakinta, tare da yin salati. "Umma karki damu Insha Allah zata farfad'o, bari in shiga wanka kafin su Yaya su shigo. " Kai kawai Umma ta d'aga mata sannan ta tashi zata wuce sai kuma ta tsaya, "Umma ina Abba ne?" "Abban ku yana masallaci," To tace sannan ta wuce d'akin su. *Around* *7:00pm* Abba da su Yaya Farook suka shigo gida cikin nutsuwa, bayan sun shiga ciki ne Yaya Farook yace. "Abba i think ' ni kawai zan koma hospital d'in yanzu, don jiki na yabani Fadwa ta farfad'o kuma baza taji dad'i ba idan ta farka taga babu kowa." A zuciyar Yaya Khaleel kuwa cewa yayi, "Mtsww Don Allah ji Yaya kuma! To dama wane dad'i kuma akeso taji itada take a gadon Hospital? " "To shikenan Farook , maganarka haka take ' to amma ka ci abinci kuwa?" Cewar Abba, "A'a Abba wallahi banajin yunwa. "Haba Yaya yaza ai kace bakajin yunwa? Don Allah ka tsaya kaci abinci and beside likitocin nan suna iyakar yinsu ' am sure Fadwa zata sami sauk," Cewar Yaya Farook, Yaya Farook kallon shi kawai yayi tare da cewa, "Bani key d'in mota!" sannan ya juya ya wuce ' ba tare da yace masa komai ba. kai tsaye ya wuce hospital d'in, direct ya nufi d'akin da Fadwa take ' koda ya shiga a zaune ya iske ta hawaye kawai ke zubo mata a fuska, da sauri ya k'arasa kusa da ita tare da tallabo fuskarta gami da share mata hawaye. "Ko kad'an bana son inga hawaye na fita daga idonki, A fusace ta d'ago rinan nun idanun ta ' ta kalleshi cikin b'acin rai, "Hawaye?!! Hawaye fa kace!" Ya d'aga mata kai alaman Eh, "Ko dayake a fatar bakin ka kawai ya tsaya ' saboda nasan duk duniya babu wanda ya kaika son ganin hawaye na!!..." Ta k'arashe maganar cikin matsanan cin kuka, "Subhanallah Fadwa meyasa zaki jefeni da wad'an nan kalaman? Nasani wannan hukuncin da su Abba suka yanke ' dole zai yi mana ciwo amma we just have to accept the fact, dole zamu yarda da k'addara kumm..." Tun kafin ya gama rufe baki ' ta d'aga mashi hannu alaman dakatar wa sannan ta goge hawayen ta, "K'addara? K'addara fa kace! Wannan ai ba ita ake kira da k'addara ba Yaya Farook, Yaya Farook ko a yanzu zaka iya warware komai ' kafad'a masu cewa ni kakeso ' ka fad'a masu cewa akwai soyayya tsakanin mu ple...." Ba ta kaiga k'arasa maganar ta ba ya daka mata tsawa da cewa, "Me kike nufi!!? Kina nufin inkoma ince masu zab'inda sukayi baiyi ba ko kuwa mene? "Eh abinda nikeso kenan kayi ' idan kuma ba haka ba to Wallahi zan bijire , ba don komai ba sai saboda kwata kwata babu soyayya a tsakanin mu da Yaya Khaleel ' baka ganin yadda yake treating d'ina? Yaya Farook wallahi inasonka." "Wai meyasa bazaki fahimci abinda nikeson fad'a miki bane? Fadwa inason ki amma haka nan zan hak'ura dake, hakuri kawai ya dace muyi baki d'aya." Ya na gama fad'in haka ya juya zai fita tayi saurin rik'e mishi hannu, "Please Yaya Farook ' meyasa baka sona? Amma shikenan naji kuma na hak'ura zan aure shi, amma Yaya Khaleel bazai tab'a jin dad'in aure ba wallahi. " jin haka yasa shi juyowa ya kalleta cike da b'acin rai sannan ya fizge hannun shi ya fice, ya na fita suka had'e da su Umma a bakin k'ofar Ward d'in. "Ina kuma zaka je? Cewar Umma, Komawa ciki yayi sannan suka bi bayanshi, Umma na shiga taje ta zauna gefen Fadwa cike da fara'a. "Ina wuni Umma? " "Lafiya kalau Fadwa yaya jikin naki?" "Umma kada ku damu naji sauk'i ina Abba? Murmushi Umma tayi ' zatayi magana Ilham ta tari numfashin ta da cewa, "Haba wa ai Abba ya ce yayi fushi dake ' shiyasa ma baizo ba," "lalala Umma dagaske ne?" Cewar Fadwa, "A'a k'arya take miki Abban ku yana cen tare da Doctor suna magana." To kawai Fadwa ta ce sannan ta ballawa Ilham harara, Yaya Khaleel kuwa yana gefe a tsaye rik'e da waya a hannun. Abba ya shigo tare da doctor ' ya cirewa Fadwa canulla d'in hannun ta sannan aka sallame su sannan suka koma gida. *** *** *** *** ** *Around* *8:00pm* Suka koma gida ' basu wani zauna yin hira ba kowa ya tafi d'akin shi domin yin bacci. *_babu_* *_yawa_* *_kuyi_* *_hak'uri_* *_da_* *_wannan_* *Dedicated* *To* *My* *Fan's* [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *33-34* *pages*🌹 Bayan shigarsu Fadwa d'aki ne Ilham ta sanya key a d'akin ta kulle tare da ajiyan zuciya sannan taje ta sami waje ta zauna a gefen gado, Fadwa kuwa tana tsaye tana k'ok'arin sanya rigar bacci, "Alhamdulillah Fadwa watan mu ya tsaya! " Fadwa tsayawa tayi cak ita bata sanya rigar ba ' ita kuma ba cire ba, "Wane irin wata ne kuma ya tsaya? "Eh mana kinga yanzu ' ni anbani damar in tsaya da duk wanda nikeso, ke kuma an zab'a miki Yaya Khaleel ' kuma wallahi Fadwa ba k'aramin dacewa kukayi ba." Ya tsine baki tayi sannan ta sanya rigar baccin ta ' ba tare da tace mata komai ba ta haye gado ta kwanta gami da jan bargo, "Ha'a Fadwa meye haka? Magana fa ni keyi kika shareni! Wai ma tsaya ko dai bakyason Yaya Khaleel ne? " Nan take Fadwa ta matso murmushi a fuskarta ' tare da tashi zaune, "Haba Ilham wace irin magana ce wannan? Aini su Umma sun gama min komai ' to donme zance banason Yaya Khaleel? " Murmushi Ilham tayi har saida fararen hak'oran ta biyu suka bayya, "Naji dad'in jin haka Fadwa," Kwanta wa sukayi a tare ' sukayi shuru nad'an lokaci sannan Fadwa tayi zambur ta tashi zaune, "Ilham?" Ilham ta amsa da "Na'am," "Ilham amma sai nake ganin kamar zansha wuya a hannun Yaya Khaleel ' saboda baya sona kuma kinga bawani sabawa mukayi dashi ba." Ilham dafata tayi tare da cewa, "Hmm Fadwa kenan ' karki bani kunya mana kamar ba'a *BABBAN* *GIDA* kike ba? Ai wannan lokacinki ne da zakiyi amfani da damarki ' ki tsigilgila mashi rashin kunya dole yayi hak'uri saboda ke zai aura! Kuma dole ki rik'ayin abubuwan da zai rik'a jawo hankalin shi gareki although dama ya riga yace ke bakida kunya ' so saiki nuna mishi haka." Sakin baki tayi ta na kallon yadda Ilham keta zuba zance, "Niko Ilham wai ina kikasan wad'an nan abubuwan?" Cewar Fadwa, "To ki zauna nan ' don wallahi Yaya Khaleel yana da y'an mata da yawa saikinyi dagaske am telling you this! " Murmushi kawai Fadwa tayi mata sannan suka koma suka kwanta ' A zuciyar ta tace, "Nifa Ilham ba son Yaya Khaleel nakeyi ba, amma da wannan shawarar taki zanyi amfani in nunawa Yaya Farook kuskuren daya tafka." Tana gama ayyana haka a zuciyar ta ne bacci yayi awon gaba da ita. *** *** *** *** *** *Around* *6:30am* Alam d'in wayar Ilham ya fara k'ara haka yasa Fadwa tashi a firgice, "Haba don Allah wane irin abu ne wannan? Kinsama mutane Alam kamar wasu yara!" Cikin magagin bacci Ilham ta tashi ' tare da yin mik'a, "Ke dai kika sani!! " Cewar Ilham, Ilham shigewa Bathroom tayi tayi wankan ta tare dayin Alwala ' sannan ta fito ta iske Fadwa sai sharar bacci takeyi, "Oh Fadwa wato bacci kika koma ko? To tashi zakiyi wallahi yanzun nan!" K'ara sawa wajen gadon tayi ta yaye blanket d'in sannan tahau bubbuga ta, "Ke dalla ki tashi ' kinsan ko k'arfe nawa yanzu," Ba arzik'i Fadwa ta tashi cikin b'acin rai sannan ta shige bathroom itama. Ko da ta gama wanka ta fito ' ta iske Ilham harta idar da Salla, sannan itama tayi Sallar a gurguje suka shirya don ganin kada lokaci ya k'ure masu. *Around* *7:00am* Suka gama kammala had'a breakfast, Fadwa ta shirya komai a saman dinning table ' sannan suka zauna ita da Ilham, haka yayi daidai da isowar Yaya Farook da Yaya Khaleel cikin parlon ' hakan yasa Ilham kashewa Fadwa ido d'aya (Wink😉) alaman tayi wani abu. Bayan sun zauna a wajen ne Fadwa tayi wuff ta mik'e tsaye gami da cewa, "Let me serve! " Zubawa ko wanen su tea tayi a cikin cup ' suka fara sha, sannan ta dafa hannun Yaya Khaleel tare da cewa, "Dear? A k'wai wani abunda kake buk'ata ne bayan wannan?" Yaya Khaleel zaro ido yayi ' cike da mamaki tare da sakin baki ' hakan yasa Yaya Farook sark'ewa, "A'a babu abinda nike buk'ata!" "Oh i see ' ai kamar Yaya Farook ne ma ke buk'atar ruwa a kusa dashi!" Cewar Fadwa, Nan take ta zuba mashi ruwa a cup ta mik'a mashi tare da cewa, "Sannu," Ko kallon ta beyi ba ya karb'a ruwan tare da balla mata harara, sannan ta koma ta zauna. Bayan sun gama karya wane Umma da Abba suka shigo parlon ' tukunna su kuma su Ilham suka tashi da niyya wuce wa School, "Har kun gama karya wanne?" Inji Umma, zukunna wa sukayi ' dukkansu suka gaishe su sannan suka mik'e tsaye, "Umma zamu tafi School yanzu." Cewar Fadwa, "To Allah ya kaiku lafiya ' ya kuma baku sa'a!" Ameen suka ce sannan suka nufi d'aki domin d'aukar handbag d'in su. Bayan shigarsu d'aki ne Ilham ta ce, "Fadwa ki cewa Yaya Khaleel shi zai kaiki School yau!" Zaro ido tayi ' ta tsaya tana k'arewa Ilham kallo cikin tsoro, "kinsan me kike fad'i kuwa?" Ta d'aga mata kai alaman Eh ' sannan Fadwa ta girgiza mata kai gami da cewa, "A'a wallahi bakisan me kike fad'iba, so kike ranmu ya b'aci da sassafen nan ko Ilham?" "Ko kad'an kawai k'ok'ari nike inga ya fara sabawa dake, kafin Aure!" Girgiza mata kai kawai tayi ' sannan ta jawo handbag d'inta zata fita ' Ilham tayi saurin rik'eta, "Please ki gwada don Allah, " To kawai ta ce sannan ta fice itama ta bi bayanta, saida suka kai tsakiyar parlor sannan Fadwa ta tsaya. "Ammm... Mhm Yaya Khaleel please zaka d'an kaimu School yau?" Cikin bacin rai ya juyo ya kalleta ' sannan ya kalli su Abba dake karyawa, "What!!?" Ya fad'a a tsawa ce ' hakan yasa k'afafun ta suka fara rawa, Ilham tayi saurin tab'ota tare da cewa, "dalla ki dake!" Fadwa kallon Yaya Farook tayi ' ta ga idon shi nakan wayar shi, haka yasa ta saki murmushi sannan ta maida kallon ta kan Yaya Khaleel ' wanda ya had'e rai kai kace mutuwar shi ya gani, "Yes! Cewa nayi kad'an zo ka kaini School, " "Driver d'in aikin uban me yakeyi?" Sunkuyar da kanta tayi ' cikin shagwab'a tace, "Nidai kai nikeso ka kaimu yau ' please Swe..." Yaya Farook ne yayi gyarar murya ' tukunna Yaya Khaleel ya ce , "To shikenan muje!" Ya fad'a cikin sanyin jiki ' sannan suka fita ya bi bayansu. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *35-36* *pages*🌹 Bayan fitarsu ne daidai bakin k'ofa ya finciko ta cikin zafin nama ' Ganin haka yasa Ilham yin sand'o ta shige mota, "Don't you think kin cika zak'ewa da yawa? Ko cemiki akai ina..." Nan yayi shuru ba tare da ya k'arasa ba ' ita kuwa tsoro ya gama cika idon ta ' Nan tayi k'arfin hali ta fizge hannunta tare da cewa, "Yes ainasan cewa baka so na ' haka zalika nima bana sonka don baka tab'a shiga raina ba Yaya Khaleel..." Ta na rufe baki ya d'auke ta da mari tasss ' nan ta dafe wajen wasu zafafan hawaye ke zuba mata a fuska, "Kamar kin manta wanene a gaban ki ko?! To bara in tuna miki ' kina magana da Khaleel ne, bana d'aukar raini Fadwa harni zaki kalla kice bakya sona?" Nan ya ja hannun ta zuwa gaban mota ' ya bude seat d'in gaba cikin b'acin rai ta shiga sannan ya rufe bamm, ya shiga ya ja motar. Fadwa kuwa tunda ta shiga babu abinda take in banda kuka ' kukan ne ya ishe shi yasa shiyin packing a gefen titi tare da cewa, "Zaki min shuru ko saina k'ara miki? Idan kuma bazaki yi shurun ba to ki fitarmun a mota," Aiba arzik'i tayi shuru don tasan halin shi babu abinda ba zai iya ba. Bayan sun kai School d'in ne yayi packing Ilham ta fita ' Fadwa bud'e mota tayi zata fita ya tsaida ita, sai da yayi shuru nad'an lokaci sannan ya ce, "idan kuma kika sake ' kika fad'awa Umma ko Abba cewa na dakeki ' to wanda zan miki sai yafi haka!," Sunkuyar da kai tayi ta had'e rai ba tare da tace Uffan ba, "And ' anjima ni zan dawo na d'auke ku," Yayi maganar cikin sanyin rai ' ya na kallon ta, "A'a ka barshi zan kira driver sai yazo ya d'auke mu, "What!! Ina magana kina magana? To idan na dawo d'aukar ku ' kice bazaki shiga ba! Fita ki bani waje, " Da sauri ta fita tare da rufe mashi k'ofa sannan ya ja motar shi ya koma gida. Ko da ya koma gida ' Umma kawai ya iske a parlor, Abba da Yaya Farook duk sun wuce Office ' samun waje yayi ya zauna, "Ina kaje ne?" Cewar Umma, "Umma na kai su Ilham School ne," Umma murmushi tayi sannan ta cigaba da kallon ta ' suna cikin hakan ne wayar shi tayi k'ara Alaman kira, cikin hanzari ya d'auka. "Ok to gani nan zuwa ' just give me some minutes Ok?" Abunda ya fad'a kenan sannan ya kashe wayar gami da mik'ewa tsaye, "Umma zan fita ' amma bazan dad'e ba zan dawo!" To kawai Umma ta ce sannan Yaya Khaleel fita , wajen motar shi yayi ' ya bud'e ya shiga sannan mai gadi ya bud'e gate tukunna ya fita. kai tsaye ya wuce wajen wani k'aya taccen restaurant, sannan ya d'aga wayar shi yayi kira tukunna ya k'arasa ciki. Wata kyakkyawar mace ce zaune a kujera ' daka ganta kasan cewa kud'i sun zauna mata kuma ba y'ar k'ana nan mutane bace. Ganin shi yasa tayi saurin mik'ewa tsaye ta tare shi cikin murna ta rungume shi, "i missed you so much ' my Love, " Ta fad'a tare da k'ank'ame shi sosai, "I missed you more baby," Rabata yayi da jikin shi ' sannan suka koma suka zauna , "jiya na sauka Nigeria ' na biyo kane akan wannan maganar," Nan ya had'e rai tare da cewa , "wace magana kenan?" "Ha'a don't tell me cewa dawo warka Nigeria ' harka manta maganar dake tsakanin mu !" "To basai ki tuna min ba! Ko aibune don kin tunamin?" Sunkuyar da kai tayi cikin takaici ' tukunna ta d'ago idanun ta ta kalle shi, "Khaleel ' maganar Auren da ke tsakanin mu mana, ka fad'amun cewa dazarar na gama school na dawo gida zaka turo!" Shuru yayi nad'an lokaci sannan yayi gyaran murya, "Lubna, ba zan Aure ki ba!" Nan take gabanta ya fad'a, cikin tashin hankali ta mik'e tsaye, "What? Me kake nufi? Bayan ka riga ' ka gama lalata mun rayuwa ta sannan ka ce bazaka Aure ne niba, impossible wallahi ba ka isa ba Khaleel..." komawa tayi ta zauna ' cikin b'acin rai take kallon shi, "Baby ba laifina bane ' su Umma ne zasu Aura mun wacce bana So, amma kema kin san inason ki " "Kar kayimun wani dad'in baki Khaleel , kuma ka sani bazaka tab'a samun kwanciyar hankali ba inhar baka Aure ni ba." Hannu yasa ya tallabo fuskarta, "Haba Baby! Ki kwantar da hankalin ki, kinga wannan Auren da zanyi ' zanyi shine kawai don faran'tawa Umma da Abba, Amma i can assure you that bayan na Aureta da wata d'aya ke kuma zan Aure ki." Murmushi tayi har saida dimples d'inta suka fito sannan ta ce, "Da gaske kake?" "Kwarai kuwa baby na!" Kallon wristwatch d'in hannun shi yayi yaga *1:56pm* ,ya tuna da zaije d'auko su Fadwa daga School sannan ya maida kallon shi akan Lubna. "Lubna zakiyi mun rakiya ' zuwa wani waje?" Kai ta d'aga mashi sannan suka tashi ' suka bar wajen, wajen mota suka nufa ' ta zagaya ta bud'e ta shiga tukunna shima ya shiga. Kai tsaye suka nufi School d'in , bayan isar shi cikin makarantar ne *2:00pm* ya cika daidai, Nan Fadwa da Ilham suka fito ' Ilham ce ta fara hango Yaya Khaleel tare da wata, "Ha'a to wacece ita?" Ta fad'a cike da mamaki, haka yasa Fadwa saurin tambayarta. "Ita wa? Ilham nuni tayi mata da yatsa ' sanin Fadwa ta fahimci abunda take nufi, "Kin gani ko? Daman na fad'a miki sai kinyi da gaske!" Girgiza kai kawai tayi sannan suka k'arasa wajen motar, Ilham sauri tayi ta shige mota ' nan Yaya Khaleel ya tsaida Fadwa, "Baby , wannan itace Fadwa ' wacce Abba da Umma suka zab'amin don na aura, " Nan Lubna ta tsaya ta na k'arewa Fadwa kallo, tamkar zata had'iye ta. "Gashi kamar bata iya gaisuwa ba ma!" Fadwa girgiza kai kawai tayi gami dayin Murmushi, "Sannu!" Abinda ta ce kenan ta shige mota ' cike da takaici a zuciyar ta, nan shima Yaya Khaleel yai ma Lubna izni data shiga su tafi ' seat d'in gaba ta bud'e ta shiga. Tunda suka fara tafiya babu wanda ya ce Uffan ' kowa sak'e sak'e kawai ya keyi a ranshi. A bakin gate d'in gida ya tsaya shi bai kaiga shiga ba, "My love, restaurant d'in nan zaka mai dani, don mota ta tana cen." Cewar Lubna, "Ku kuma ku k'arasa ciki bara in maida ta," Ilham ce mai k'arfin halin cewa to, sannan suka fito suka shige gida ' shi kuma ya juya domin maidata restaurant d'in. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *_I_* *_dedicated_* *_this_* *_page_* *_to_* *_all_* *_members_* *_of_* *SEEMALUV'S* *NOVELS* *GROUP* *37-38* *pages*🌹 Suna shiga ciki ' suka iske Umma a zaune saman kujera tana kallo, bayan sun gaishe tane suka juya da niyyar wuce wa d'aki Umma ta tsaida su, "Ina Khaleel d'in? " Ilham ce ta kalli Fadwa ' wacce kanta yake a sunkuye, "Ha'a wai baku nake tambaya ba?" "Umma yaje maida budurwar sa gida, " Cewar Fadwa, "Wace irin budurwa kuma ' babu dad'in ji, " Nan Ilham tayi saurin shiga maganar , "Eh Umma budurwa! Umma wallahi ba kiga yadda ya wulak'anta Fadwa ba, harda cewa wai zab'in kune amma bashi ya ce yana sonta ba...." Nan Umma ta dakatar da ita cikin fushi , "Naji, ya kuma isheni haka nan ' kuma shi Khaleel d'in zai dawo ya same ni, ku tashi ku shiga ciki." Mik'ewa sukayi a tare suka wuce d'aki, bayan shigar su ne Fadwa ta sami waje ta zauna ' sannan ta maida kallon ta kan Ilham, "Ilham dama akwai maganar da nakeso in fad'a miki, amma please kada kid'auke ta da wani fuska daban." Cikin zumud'i Ilham ta ce, "No wait! bari in fara fad'a miki wani albishir tukunna," To kawai Fadwa ta ce , "Fadwa yau zanyi bak'o na musamman, " "Wow! Kardai kicemin dashi za'ayi," "Kwarai kuwa , Insha Allah shine mijin Aure na." Girgiza kai Fadwa tayi cike da dariya , "Ameen, to meye sunan sa?" Wara idanu Ilham tayi gami da juya su ' tukunna ta ce, "Sunan shi Al'ameen." Nan Fadwa ta buga uban ihu ' cike da jin dad'in sunan , "Insha Allah ' sunan d'a na kenan na fari, " Murmushi kawai Ilham tayi tace, "To fad'amin abunda zaki fad'amin yanzu, " Nan Fadwa ta d'anji jikin ta yayi sanyi, sannan ta rufe ido ta fad'a mata duk abinda ke tsakanin ta da Yaya Farook. Ajiyar zuciya Ilham tayi ' cike da tausayawa soyayyar su, "Fadwa ba laifinki bane ' laifin Yaya Farook ne da baiyi saurin sanarwa ba, kuma inaso kiyi hak'uri ki cire shi amatsayin masoyi ' don na tabbata bazai aure kiba, kuma yanzu dole zaki jajirce don ganin kinsamo kan Yaya Khaleel ' don kuwa shine mijin auren ki.!" Ajiyan zuciya tayi nad'an lokaci, "Ilham , Insha Allah zan k'ok'arta duk da nasan zansha wahala a wajen shi," "A'a kar kice haka ' Fadwa ni zan taimaka miki wajen yak'ar wannan budurwar tasa dayake ik'irari, " Nan sukayi smilling ' sannan suka tashi suka nufi kitchen, shirye shiryen abunda za'a ci na lunch sukeyi cikin hanzari, nan Diary d'in Yaya Khaleel ya fad'owa Fadwa a rai. "Amm Ilham , ki bani 5minutes zanje indawo yanzu ' and please karki tsaya jirana, " Ok kawai Ilham ta ce sannan Fadwa ta nufi d'akin Yaya Khaleel kai tsaye, bud'e k'ofar tayi a hankali ta shige cike da sand'o. Ta na shiga tahau yin bincike ' gami da bud'e drowers d'in d'akin, ganin bata sami komai bane yasa ta koma gefe tare da cije yatsa ' tukunna ta haye saman gadon shi, tana d'aga pillow taga Diary d'in, nan tayi ajiyar zuciya sannan ta d'auka cikin sauri ta diro daga saman gadon ' ta baro d'akin. D'akinsu ta nufa direct ta bud'e handbag d'inta ta saka ciki, sannan ta koma kitchen ' tana shiga ta iske har Ilham ta gama d'aura sanwa, "Har kin d'aura sanwan kenan?" "Eh na gama ' yanzu kuma kece da zarya cikin kitchen, don na gama nawa. " Ya tsine baki tayi ' gami da cewa, "To naji dai ' aini ba raguwa bace ' balle kice bazan jure ba !" A tare suka bar kitchen d'in suka nufi parlor ' Umma suka iske a zaune ita kad'ai tana kallo, sannan suka sami waje ' suka zauna, "Fadwa kun d'aura sanwan ne?" "Eh Umma mun d'aura," Tana gama fad'in haka Yaya Farook ya shigo cikin parlon cike dayin sallama ' suka amsa, sannan ya sami waje ya zauna gami da sauke ajiyar zuciya. "Ke Ilham kawomin ruwan sanyi, " Cikin hanzari Ilham ta tashi ' ta nufi kitchen, ta d'auko mashi robar ruwan sanyi da cup ' ta kawo mashi. Bayan ya shane yayi gyarar murya, "Umma ' na sami transfer daga wajen aiki na, " "Farook transfer kuma?" "Eh Umma yanzu haka ma tare da transfer letter d'in nake, " Hankalin Fadwa in yayi dubu ya b'aci, cikin damuwa taketa k'ok'arin had'a ido dashi, shi kuwa yak'i yarda don kuwa yasan tabbas tana cikin damuwa, "Yaya Farook ' ina ne suka maida ka yanzu?" Cikin rawar muryar tayi maganar ' hakan yasa Ilham tayi sauri ta rik'e mata hannu, "Bangladesh suka tura ni, sun bani nan da 3days ' infara shirye shirye, " Nan ta rafka salata ' salatin da batasan ya fito fili ba, "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un," Da sauri Umma ta kalli Fadwa ' hawaye ne kawai ke fitowa daga idanun ta, "Fadwa lafiya? Bafa tafiya zaiyi gaba d'aya ba! zai rik'a zuwa yana ganin mu," Girgiza kai kawai takeyi cikin kuka ' ganin haka yasa Umma cewa, "Ilham jata ku tafi d'aki ki lallashe ta, " Kwallane cike a idon Yaya Farook ' kasa danne zuciyar shi yayi yasa yayi saurin tashi ' ya wuce d'akin shi. "Ohh ikon Allah ' shak'uwa kenan, Allah dai yak'ara sanya shak'uwa a zuciyoyin ku. " Cewar Umma, Nan itama ta tashi ta wuce kitchen don duba ' girki. Ilham lallashin Fadwa kawai takeyi ' amma sam tak'i daina kukan, "Fadwa hak'uri fa zakiyi ' Yaya Farook ko ya tafi na tabbata zai rik'a dawowa yana dubamu, " "Ilham wallahi inason shi sosai ' zuciyata ta kasa hak'ura kibarni kawai inyi kukan ko zansami sauk'i, " Sake fashewa da kuka tayi ' cike da tausayawa, "Fadwa, amma dai kinsan kukan nan bazai ammafana miki komai ba ko? Yes nasan kina son shi sosai ' amma kinsan dai bazai aure ki ba yanzu!" "Ilham, please ki daina tunatar min da haka ' its hurting me, i have a stronge feelings that Yaya Farook shiya nemi wannan transfer d'in da kansa. " Rik'e hannun Ilham tayi ' tare da cewa, "Ilham, am pretty sure Yaya Farook ya na sona haryanzu a cikin zuciyarsa ' Ilham kawai bayason ganin biki nane dawani shiyasa ya nemi Transfer, " Ilham d'aura kan Fadwa tayi a kafad'an ta gami da bubbuga mata bayanta, "Kiyi shuru ki bar kukan nan ' and zuwa anjima idan zaki kwanta ki tabbatar kinyi *istik'ara* domin neman zab'in Allah," Ajiyan zuciya tayi ' sannan tace to tukunna Ilham ta tashi ta tafi kitchen. *Around* *3:00pm* Yaya Khaleel ya dawo gida, Ilham ce d'auke da plates a hannun ta nufi dinning table da shi, haka yayi daidai da shigowar Yaya Khaleel cikin parlon ' ganin har an gama abinci ne yasa ya doshi wajen dinning table d'in kai tsaye. Samun waje yayi ya zauna sannan ya tsayaya ruwan sanyi a cup yasha, itadai Ilham tana tsaye ta jera abubuwa. Umma ce ta shigo cikin parlon ' ta Umar ceta dataje ta kira Yaya Farook ya zo ya ci abinci, Bayan Wucewar Ilham ne Yaya Khaleel ya gaida Umma da cewa, "Sannu Umma!" Umma ko kallon shi batayi ba ' balle ta amsa sallamar shi, ta sami waje ta zauna , hakan yasa hankalin shi ya tashi ' Yaya Farook ne ya shigo parlon Ilham na biye da shi , sannan suka sami waje suka zauna Tayi sarving d'insu. Bayan sun fara cin abincin ne ' Umma ta umarce Ilham taje ta kira Fadwa , "Umma tund'azu naimata magana, tace batajin yunwa ' inbanda kuka babu abinda takeyi, " Yaya Khaleel ne ' ya d'ago kai ya kalleta, "kuka kuma? Me akayi mata take kuka, " Yunk'urawa yayi zaije d'akin Umma tayi saurin dakatar da shi, "ina zakaje? D'akin nasu zakaje domin kasake k'unsa mata wani bak'in cikin kokuwa me?" Komawa yayi ya zauna ' tare da girgiza kai Alaman A'a, "Umma zanje induba ta ne!" Tsaki taja ' ba tare da tace komai ba, sannan Yaya Farook ya tashi ya wuce d'akin nasu domin duba halin da take ciki. *Dedicated* *To* *My* *Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_PERFECT_* *_WRITERS_* *_FORUM_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *39-40pages*🌹 Yana shiga, ya iske ta a kwance ' duk'unk'une cikin blanket, sautin kukan ta kawai ke yi mashi zarya a kunnuwan shi. Samun waje yayi ' ya zauna a bakin gado ' dai dai Fuskarta, sannan ya yaye bargon ' nan ne Fadwa tasan da mutum a cikin d'akin, hakan yasa tayi saurin d'aga kanta ' ta kalle shi, "Meyasa kikeso ' kiyiwa kanki horo da yunwa? ko kinaso ' wani ciwon ya kamaki ne?..." Yayi maganar cikin sanyin murya ' Fadwa tashi tayi ta zauna, tare da had'e kanta da gwiwa, "Yaya Farook, zan cigaba da hora kaina da yunwa ' kuma zanyi k'ok'arin ganin ciwo ya kamani, ciwon ma na zuciya ' saboda na tabbata haka kake buk'atar gani, " Ta fad'a tare da d'ago kanta, tana kallon cikin kwayar idon shi , "Fadwa, hak'uri shine abinda ya dace damu ' bayan wannan babu wani abunda zamu iyayi, kuma inaso daga yau ' ki d'aukeni a matsayin Yaya Farook d'in da kika sani ," Yana gama fad'in haka ya juya ' ya share hawayen da ke shirin zubo mashi a fuska, bai ankara ba ' yaji ta rik'o mashi hannu, a hankali ya juyo ' ya kalleta, "Please Yaya na, promise me that ' bazaka tafi ka barni ba, zaka tsaya tare da ni ' a cikin *BABBAN GIDA*, " Nan take ' yaji wani mugun tausayin ta ' ya kamashi, zuciyar shi rugugi kawai take mashi ' hakan yasa yayi saurin tallabo fuskarta. "I promise you that ' k'anwa ta, insha Allah bazan tab'a barin ki ba." Nan yasa hannu ' ya share hawayen da ke fuskarta, "yanzu ' inaso ki tashi muje parlor, ki ci abinci kuma kiyi walwala kamar kowa." To kawai ta ce mashi ' sannan ta hanzarta ' ta sauko daga saman gadon, suka fito d'akin a tare. Kai tsaye ' suka zarce wajen dinning table, Fadwa ta zauna kusa da Ilham ' tukunna shima Yaya Farook ya sami waje ' ya zauna, sannan Ilham ta mik'e ta zuba mata abinci. Tunda Fadwa, ta zauna ' Yaya Khaleel keta satar kallon ta, yana son tambayar ta dililin da yasa take kuka ' ita kuwa ko a jikinta, abin cin ta kawai takeci ' kasan cewar Yaya Farook ya tausasa mata zuciya. Bayan sun gama ' cin abincin ne , ta tashi ta wuce d'akin su, Ganin haka ' yasa Yaya Khaleel shima ya tashi zaibi bayan ta, "Ina zakaje?" Cewar Umma, Tsayawa yayi ' yana kallon plate d'inda ke gaban shi, "Umma d'akina zanje fa!" "Allah ya baka sa'a , kuma ka cigaba dayin abinda kaga dama Khaleel ' shigowar Abban ku kawai nake jira." Had'iye miyau yayi dak'er, har ya juya ' zai tafi sai kuma ya tsaya, "Umma, ko wani laifin akace nayi?" "Khaleel, tambaya ta kakeyi?" Nan ya sunkuyar da kai ' gami da sosa kanshi, "A'a Umma kawai dai..." "To ka bari ' sai Abban ku ya dawo, sannan kaji laifin da ka aikata ' kuma ka wuce ka bani waje," Tana gama fad'in haka, Yaya Khaleel ya nufi d'akin su Fadwa kai tsaye, Yaya Farook kuwa fita yayi ' ya shiga mota yayi tafiyar shi. Jin gidan babu dad'i ne yasa ' Ilham kunna TV donyin kallo. Bayan shigan ' Yaya Khaleel d'akin ne ya iske Fadwa tsaye, wajen window ta na kallon waje ' daka ganta zaka fahimci cewa lallai tana cikin damuwa, "Meyasa meki Fadwa?" Maganar ce tazo mata ' zuwan bazata, haka yasa tad'an razana kad'an, sannan ta juyo ' ganin Yaya Khaleel ne yasa ta b'ata rai, ta juya ta cigaba da fuskantar window. Murmushin gefe yayi ' sannan ya tako har inda take, tare da tallabo fuskarta ' da hannu biyu, suna fuskantar juna. "Why are you ignoring me? Ko nayi wani laifin ne ' ban saniba Fadwa," Harara ta watso mashi tare da kauda ' fuskarta daga hannun shi, sannan ta ja tsaki ' ta juya zata wuce, yayi saurin janyo ta cikin zafin nama ' tare da had'a ta da bango, nan ta saki wani k'ara. "Ahhhggh," Matse ta yayi sosai ' ga irin rik'on da yayi mata a hannu, nan da nan ' idanun ta suka ciko da hawaye, "Yaya Khaleel, you're hurting me.." "Ni zakiyiwa tsaki? Cikin kuka ' tace, "A'a.." Nan ya saketa ' suka koma suna maida numfashi, daga bisani ya juyo ' ya kalleta. "idan kin gama kukan ' kizo d'akina ki sameni," Fita yayi ' ba tare da yajira abinda zata fad'a ba, Fadwa komawa tayi ' ta zauna gefen gado, ta share hawayen ta ' sannan ta tashi ta d'aura towel, ta fad'a bathroom donyin wanka. *** *** *** *** *** *Around 5:30pm* Fadwa ta fito parlor ' cikin doguwar riga, english wears ' gown ce a jikin ta, ta zauna a jikinta sosai ' don shape d'in jikin ta gaba d'aya ya fito. Ganin babu kowane a parlon ' yasa ta nufi kitchen kai tsaye, tare da kwala wa Ilham kira. "Ilham!!!" "Na'am Fadwa, ina kitchen." Haka yasata k'arasawa cikin kitchen d'in cikin sauri, "Me kike girka mana ' don nasan dai akwai abincin dare." "Kin manta ' nace miki yau zanyi bak'o Fadwa?" "Ayya! sam na manta ' to k'arfe nawa yace miki zaizo? " "Zaizo around ' 8pm," OK kawai Fadwa tace ' sannan ta bar kitchen d'in, ta nufi d'akin Yaya Khaleel ' knocking k'ofar tayi taji shiru, kawai ta bud'e ta shiga . Shigarta yayi daidai ' da fitowar shi, daga bathroom d'aure da towel a jikinsa ' da alama wanka yayi, ganin haka yasa tayi saurin juya mashi baya. "Am sorry ' I didn't know that you were naked!" Ta fad'a, haka yasa shi juyowa ' a 360 cike da mamaki, sakin baki yayi yana kallon ta ' sannan ya maida kallon shi ga jikinshi, "Naked???" Nan ya b'ata rai, a zuciyar shi yace, "lallai ' wannan yarinyar y'ar rainin wayo ce, wato tsirara ma nake ' a haka kenan, Lallai zan koya miki hankali." Ya fad'a a zuciyar shi tare da jan tsaki ' sannan ya kalleta, "Sai yanzu kikaga damar zuwa?" "wanka nayi shiyasa..." Nan ya tsaye yana k'arewa halittar ta kallo, sun b'ata minti 5 a haka sannan yayi gyarar murya.'' "Ke! Wane irin iskanci ne ' wannan? Bayanki nakeson gani kokuwa gabanki?" Maganar ce tayi mata wani ' ga tsaitsai, "Yaya Khaleel, nifa ba y'ar iska bace ' taya kakeso in kalle ka, bayan babu riga a jikin ka?" K'arasowa yayi kusa da ita, sannan ya juyo da ita ' da k'arfin tsiya, take ta runtse idon ta gam gam. "Zaki bud'e idonki kokuwa saina miki abinda zaki dad'e kina tuna shi, acikin ranki!" Banza tayi ta kyaleshi ' ba tare da ta bud'e idon ba, "Kinaso kicemin ' kwalliyar dama ba donni kikayi ba, ko kuwa mene?" "Yaya khaleel, nidai kayi hak'uri but i can't..." Bata k'arasa maganar ba ' taji saukar lips d'inshi a kan bakin ta, hakan yasa ta bud'e idanun ta cike da tsoro, k'ok'arin kwace wa takeyi ' amma ya riga yaci k'arfin ta. Jin jikin ta na rawa ne ' yasa shi kyaleta, amma sam bai yarda ya rabu da jikinta ba ' ninshi kawai takeyi sama sama, "what? Don't you love me? Didn't you feel me? Fadwa ' nasan kina sona ai ko, but ni bana....." Jin haka yasa ta dawowa hayyaci ta ' cikin d'an k'ank'anin lokaci, "Yaya Khaleel, abinda kaimun ' Allah ne kawai zai sakamin, kuma inaso ka sani cewa ' wannan maganar ' da kayi Insha Allah saikayi dana sani, " Nan ya ture ta ' ta zube a k'asa. "Wai don nayi kissing d'inki, shine kike fad'amin wannan magan ganun ' to bari kiji in fad'a miki, nayi kissing d'in y'am mata da dama, wad'an da suka fiki, kuma daga k'arshe sukemin godiya ' why not kema kiyi godiya , and stop pretending!" Nan ta tashi ' cikin sauri ' ta bar d'akin, kai tsaye ta wuce d'akin ta fad'a saman gado, wani wahalallan kukane yazo mata mai sauti ' cike da tausayawa kanta. *Dedicated To My Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluvv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me @*_I want to use this opportunity ' to thanks everyone of you, for the birthday wishes ' gaskiya naji dad'i sosai, kuma na gode ' Thank you so much guys, you really make my day...thank U once more.😘😘😘_* *41-42pages*🌹 Jin tafiyar Ilham ne ' yasa tayi saurin share hawayen ta, tare da saukowa daga saman gadon. Bayan shigowar Ilham ' cikin d'akin ne, ta fahimci cewa akwai abinda yake damun Fadwa. "Fadwa? " Juyowa tayi ta kalleta ' cike da sosa idanun ta. "Na'am Ilham." "Kamar kinyi kuka ' Fadwa, da abinda ke damun kine?" Nan ta matso murmushin k'arfin hali. "Laa! Wane irin kuka kuma? A'a babu abinda ke damuna, kawai kwaro ne ya shigar mun ido." Ok kawai Ilham tace ' sannan ta d'auki towel ta d'aura a jikin ta, ta shiga wanka. Ilham komawa tayi a kwanta ' abunda Yaya Khaleel, yayi mata ne ' yaketa fad'o mata a rai. *Around 8:00pm* Bayan Ilham tayi wanka ' harta gama shiryawa, cikin Riga da skirt ' atamfa, sannan ta zauna a gaban mirrow ' ta fara cab'a ado. Fadwa wacce ke kwance ' a saman gado ne tace, "Waike, wannan wace irin make-up kikeyi haka?" Ilham tsayawa tayi cak ' tana kallon ta cikin mirrow, "Ha'a to ina ruwanki? Nifa banason sa ido ' in kinji haushi kema kiyiwa Yaya Khaleel." Tsaki taja ' tare da saukowa daga saman gadon, cikin b'acin rai. "Ke dai kika sani!!" Ta fad'a gami da ficewa daga d'akin, ta nufi parlor kai tsaye. zaman ta keda wuya ' Yaya Farook ya dawo, sallama yayi ta amsa ' tukunna ya sami waje ya zauna. "ke kad'ai ce a parlon, ina Ilham tace?" "Ilham, tana d'aki." Ta fad'a ba tare da ta kalleshi ba. Yaya Farook ' zaiyi magana kenan yaji sallamar Abba, a cikin parlon ' cikin hanzari ta tashi, ta tunkari Abba. "Abba, sannu da dawowa." Fadwa ta fad'a gami da karb'ar jakkar shi , sannan ta kai mashi sashen d'in shi. Bayan ya zauna ne ' Yaya Farook yayi ma Abba sannu da isowa, tukunna ya koma k'asa ya zauna. "Ina Umman taku take?" Cewar Abba, "Nima shigowa ta ' kenan Abba, amma ina tunanin tana d'akin ta." "Alright! Naga sak'on ka ta Email d'ina, game da transfer d'inda akayi maka ' hope dai ka gama shiryawa?" Hakan yayi dai dai ' da dawo war Fadwa cikin parlon. "Eh Abba , na kammala shirina ' nan da next week Insha Allah flight d'ina zai tashi." Raras Fadwa taji ' gaban ta ya fad'i , a hakanli take saukowa ' daga saman steps tare da cewa, "Abba, nakai jakkar d'aki." Muryar ta na rawa ta fad'i haka, jin haka yasa Yaya Farook juyowa ' ya kalleta a tsorace. Ganin ta nufi b'angaren su ne ' yasa shi mik'ewa tsaye tare da cewa, "Abba , ina zuwa." Uhm-hum, kawai Abba ya ce ' sannan Yaya Farook yabi bayan Fadwa cikin sauri, hartasa hannu zata bud'e k'ofar d'akin su yayi saurin tsayar da ita. "Fadwa, Please.." A fusace ta juyo ' ta kalle shi, idon ta cike da hawaye. "Bana son ji! Yaya Farook, babu abinda zaka fad'amin, kamin k'arya kuma ka b'oyemin, and Insha Allah ' na hak'ura dakai for good, and if am where you ' zan had'a kaya na ne gobe gobe intaf...." Bata kaiga k'arasawa ba ' ya falla mata mari, jikake tasss ' nan take ta zuk'unna gami sakin k'ara. "Ahhhhgggh," "Fadwa, kinsan me kike fad'i kuwa? Kinsan wanene a gabanki kuwa?" Cikin kuka ta mik'e tsaye ' tare da cewa, "Kwarai kuwa, nasani ' kuma nagode!!!" Tana fad'in haka ta bud'e k'ofar d'akinsu ta shige, nan sukayi kicib'us da Ilham ' tana k'ok'arin fitowa. "Ke! Fadwa, harya iso." Fadwa banza tayi ' ta kyaleta tashige d'aki, Ilham lura tayi da Yaya Farook a bakin k'ofar ' ranshi a bace , a zuciyar ta tace. "Topha! Ashe takuce ' ta had'o ku!!" Saida ta tsaya ' ya wuce tukunna, itama ta wuce parlor ' gudun karya huce kanta. Ilham wacce ta fita ' ta shigo da bak'on ta mai suna Al'ameen, cike da fara'a ta zarce dashi ' parlon da bak'i ke zama. Bayan sun gaisa ne ' ya yaba da irin Kwalliyar da taimashi, "My baby, gaskiya kinyi kyau ' nawa za'a siyarmun da wannan kwalliyar?" Murmushi tayi ' sannan ta tashi, tare da cewa. "uhm ' bara in kawo maka ruwa!," Tana fad'in haka ta wuce ciki ' ta nufi kitchen kai tsaye, ta had'o mashi drinks da abubuwan da ta shirya mashi. Ilham, dawo wa tayi ' ta aje mashi a gaban shi, sannan ta bud'e drinks d'in ta zuba mashi a cup ' ta mik'a mashi cike da ladabi, ta koma ta zauna. Al'ameen, sau d'aya yasha ' sannan ya aje a k'asa, "My baby na gode ' da tarba mai kyau, But nace nawa ' zanbiya kwalliyar nan?" "Sweetheart, ai bazaka iya biya ba ' so kawai kabarshi." Nan suka cigaba da hirarsu ' ta soyayya, Fadwa kuwa na kwance a d'aki tana danna wayarta, taga an bud'o k'ofa ' ga dubanta saitaga Umma ce , "Fadwa! " "Na'am Umma?" Umma k'arasawa ciki tayi ' ta zauna a bakin gado, itama Fadwa ta ' tashi ta zauna. "Ki tashi ' kije Abban ku nason magana daku," To kawai Fadwa ' ta cewa Umma, sannan ta sauko daga kan gadon ' da niyyar fita, "Ina Ilham take?" Cewar Umma, "Amm, Umma ' tayi bak'one, suna k'aramin parlor." To Umma tace ' sannan Fadwa ta fita zuwa parlor, ita kuma Umma ' zarcewa tayi d'akin Yaya Khaleel ' da Yaya Farook. Bayan Fadwa ' ta isa harabar parlon ne, ta iske Abba a zaune d'auke da laptop a saman cinyar shi ' sai da ta gaishe shi tukunna, ta sami waje a k'asa ta zauna. "Fadwa, ke kad'ai ce ' ina sauran suke?" "Umma taje kiran su ne ' but ita Ilham, tana da b'ako ne shiyasa." Ok kawai Abba ya fad'a, sannan ya maida kanshi ' ga laptop. Ana a hakan ne ' Umma ta shigo cikin parlon ' su Yaya Farook ' da Yaya Khaleel, suna biye da ita. Umma zama tayi ' gefen Abba, tukunna suma suka zazzauna a k'asa cike da ladabi, Abbane ya ajiye ' laptop d'in nashi, saman hannun kujera ' sannan yayi gyarar murya. "uhm Uhm! Ammm... dalilin ' taraku anan wajen shine, Magana ce akanka ' kai Khaleeel." Nan Yaya Khaleel ' yaji rasras a zuciyar shi. Sannan Abba ya cigaba da cewa, "Tabbas ' duk naji abubuwan da kakeyi, a cikin gidan nan ' da kuma waje, da irin wulak'ancin da kake nunawa ' ita wannan yarinyar Fadwa, to inaso ka bud'e kunnuwanka sosai ' ka saurare ni, Fadwa ce ' zab'in mu a cikin gidan nan ba wataba ' kuma Aure tamkar an d'aurashi ne ' harkai ka isa kayi jayayya ' da zab'in mu?" Cikin tashin ' hankali Yaya Khaleel ke girgiza kai. "Kuma bari ' kaji in gaya maka, wani abinda baka sani ba ' aure kamar anyishi angama ne, domin nida Umman ku ' mun yanke shawaran Next week za'ayi auren ku, in Allah ya yarda." Maganar ce, taiwa Fadwa tsawa a kai ' da k'arfi ta d'ago kai ta kalli Abba, sannan ta maida kallon ta ' akan Yaya Khaleel, wanda shima ita yake kallo ' ranshi a b'ace, tukunna ta maida kallon ta ' zuwa k'asa.. "To amma Abba, bikin nan fa kamar yayi kusa ' da yawa...." Bai kaiga ' gama rufe baki ba, Umma ta daka mashi tsawa ' da cewa, "Rufe mana baki, ja'iri kawai ' wato kai har wuyarka tayi kwarin da zaka iya ' fad'a in fad'a da Abban naku? Lallai bakada kunya Khaleel." "Umma, don Allah kuyi hak'uri." Abinda ya iya fad'i kenan, sannan ya sunkuyar da kanshi k'asa. Fadwa kuwa ' mamakin kanta ' ta rik'ayi ganin yadda idonta ' ya k'enk'eshe sam babu hawaye a cikin sa. Shi kuwa Yaya Farook ' komai baice ba game da maganar, sannan Abba ya ce. "Ku tashi ' ku tafi." Fadwa yunk'urawa tayi zata wuce, Abba ya tsaida ita. "idan Ilham ta gama ' ki sanar da ita, ina neman ta." To kawai ta ce ' sannan ta wuce d'akin su, ta haye gado ' a cigaba da danna wayarta. *Dedicated To My Fan's* 👄👄👄😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *43-44* Yaya Farook kuwa ' yana shiga d'akin shi, ya hau shirya kayan shi ' cikin trolley, daga bisani ya tsaya ' don kuwa yarasa meyasa yake sanya kayan shi aciki. Komawa yayi ' ya zauna tare da goge zufar goshin shi, sannan ya tashi ' ya shiga bathroom yayo alwala, yayi sallah raka'a biyu(Nafila) ' gami da rokon Allah yazab'a mashi mafi alkairi. B'angaren Yaya Khaleel kuwa, gaba d'aya ranshi ya riga ' ya gama b'aci. Nan ya d'auki wayar shi ' da take kan mirrow d'in d'akin, cikin sauri yayi dailing number d'in Lubna, harta shiga ' yayi saurin yanke call d'in gami da dafe kanshi, "Oh my God, what the hell ' is wrong with me!, meyasa su Abba zasuyi min haka? Yes inason Fadwa ' but is just that ita ba ajita bace, and besides she's not my choice." Ita kuwa Lubna ' cike take da mamaki, yadda taga flashing d'in Yaya Khaleel a cikin wayar ta ' girgiza kai kawai tayi, sannan tayi dailing number d'in shi itama. Yaya Khaleel ' yana cikin wannan tunanin ne, yaga shigowar kiran Lubna ' cikin hanzari yayi recieving. "My love!" "Yes baby ' ya kike?" "Lafiya kalau my love!' I was surprised dana ga missed call d'inka." Nan ya tuna cewa ' eh tabbas yayi dailing numbar ta, "Oh yes baby, it was a mistake ' bansan na kiraki ba ma. " Yana yin ' yadda yake magana ne, ta fahimci cewa ' akwai abinda yake damun shi. "but my love ' is everything alright? " "Of cause, baby zamuyi magana ' anjima Okay?" Bai jira ' yaji abinda zata fad'a ba ' ya kashe wayar, sannan ya koma ya zauna a Sofa. Yaya Khaleel ' cike yake da tunani iri ' iri, a cikin zuciyar shi ' jinginar da kanshi yayi a jikin kujera, zuciyarsa na maimaita mashi ' maganar da Abba yayi. "Subhanallah!" Abinda ya iya furtawa kenan ' ya tashi ya shiga bathroom, domin watsa ruwa. Ita kuwa Fadwa ' pictures taketa kallo cikin wayarta, don kuwa duniya taimata dadi ' tana cikin haka ne Ilham ta shigo cikin d'akin. Zambur Fadwa tayi ta zauna ' fuskarta d'auke da murmushi. "Har Al'ameen d'in ya tafi?" "Eh ya tafi ' kuma yayi fushi, tunda bakizo kun gaisa na." Uhm ' kawai Fadwa tace wa Ilham, Ilham lura tayi ' Fadwa ta sauya ba kamar yadda ' ta barta ba. "Fadwa akwai labari ne mai dad'i?" "Uhm ' ai dama abinda naketa jira ki tambaya kenan." Nan ta fad'a mata duk abinda ke faruwa, da kuma hukuncin da Abba ya yanke ' sannan kuma ta sanar da ita cewa Abba yana nemanta. Miyau Ilham ta had'iye dak'er, gaban ta na dukan uku uku. "Shikenan ' nima za'a badani, Allah dai yasa nawa ba kusa ' kusa bane haka." Ta fad'a tare da dafe k'irjinta, abinne ya bawa Fadwa dariya matuk'a. "Haha! Lallaima Ilham ' to ba gwara kawai a had'a mu ' mu biyu ba?" Girgiza kai kawai Ilham tayi ' daka kalli idon ta ' zaka gane cewa akwai fargaba a cikin su, Ilham juyawa tayi ta nufi sashen ' Abba. Bayan Yaya Khaleel ' ya fito wanka ne, d'aure da towel a jikin shi ' ya zauna a bakin gado, ya hankad'a pillow ' don d'aukan diarry d'inshi, Hankalin shine yayi matuk'ar tashi ' don ganin babu diarry babu alamar sa. Nan yayi zambur ' ya tashi tsaye, gami da bud'e drowers d'in wajen ' duk da yasan bai aje a wajen ba. "Ha'a to a ina na aje shi?" Yaya Khaleel ' saida yabi ko'ina ya bincike, amma kwatakwata ' bai gani ba. Fadwa ce ta fad'o mashi a rai ' don kuwa yasan babu wacce zata iya d'aukar mashi diarry ' sai ita. "Oh my God ' this gurl is so stubborn, ni bansan yadda zanyi ' da yarinyar nan ba wallahy, mtswww." Ita kuwa Fadwa tashi tayi ' tayi shirin bacci cikin rigar bacci transparent ' iyakarta gwiwa, sannan ta haye gado ' gami da janyo handbag d'inta, tana k'ok'arin cire diarry d'in Yaya Khaleel ' domin karan tawa. Yaya Khaleel ' abin duniya ne ya isheshi, ya ga bazai iya hak'uri ba ' hakan yasa yafito daga d'akin shi ' daga shi sai towel a jikin shi, ya nufi d'akin su Fadwa. Yaya Khaleel ' bankad'o k'ofar yayi ' haka yayi daidai, da cirowar Diarry d'in nashi ' daga hannun Fadwa. A tsorace ta d'ago kai ' ta kalleshi, tsoro ne yasa tayi saurin yin wurgi da diarry d'in k'asa ' cikin rawar baki tace. "Yaya Khaleel ' are you looking for something?" Ta fad'a tare da yin saurin rufe jikinta ' da blanket ma'ana bargo. Cikin fushi ya k'arasa cikin d'akin cike dayin huci tamkar zaki, finciko ta yayi ' har sai da hannun ta ya ansa, a tsiyace ya fizgota zuwa k'asa. "Ke!! Where is my diary?" Had'iye miyau tayi dak'er , sannan tace. "Yaya Khaleel ' babu diary d'inka a wajena!" Yaya Khaleel ' maida kallon shi yayi zuwa k'asa, sannan ya tuna lokacin da ' take wurgi dashi zuwa k'asa, Fadwa cikin tsoro ta kalli diary d'in ' sannan ta maida kallon ta kan Yaya Khaleel suka had'a ido. "Well ' am so sorry Yaya Khaleel, am just trying to..." "trying to do what!!!" Ya daka mata tsawa ' sannan ya duk'a ya d'auki diary d'in. "For Goodness sake ' why are you so stubborn? Fadwa!" Sunkuyar dakai tayi ' ita dai tsoron ta shine, kada ya tab'a lafiyan jikin ta. Fadwa jitayi yayi shiru ' yasa tayi saurin d'aga kai ta kalleshi, ga duban ta sai taga ' ashe k'irjin ta yake k'arewa kallo, kasan cewar rigar jikinta shara shara ce. Da sauri tasa hannu d'aya ' ta kare wajen ' don kuwa yana rik'e da d'ayan hannun, ganin haka yasa Yaya Khaleel dawo wa cikin senses d'in shi. Ganin yadda tsoro ya kamata ne ' yasa shi yin murmushi tare da tallabo hab'arta. "What? Meye kike karewa? Aren't you stubborn enough? And besides ' kin kusa zama matata duk da bakida mu halli a zuciyata." Nan ya fara k'ok'arin kissing d'inta ' tak'i yarda, jin tafiyar Ilham ne ' yasa yayi saurin wulli da ita ' ta fad'a saman gado, sannan ya juya ya fice ' suka had'e da Ilham a hanya, saida ta jira ya wuce sannan ' ta k'araso cikin d'akin. "Fadwa ' meyafaru ne?" "Me kika gani?" Ilham K'arasawa ciki tayi ' ta nemi waje ta zauna. "gani nayi ' daga ke har shi ' kunyi wani iri." "hmm ke kuwa ' akwai ki da sonjin kwakwaf, babu komai fa kawai zuwa yayi ' yayi abinda ya saba." Ya tsine baki Ilham tayi ' sannan ta shiga cire kayan jikinta, donyin shirin bacci. "Baki bani labarin yadda kukayi da Abba ba." "Ke nifa wallahi ' yanzu bacci nakeji, ki bari sai munje school." Ok kawai Fadwa tace mata sannan ' ta maida kallon ta kan wayarta. *Dedicated To My Fan's* *_Seemaluv👄 ' the brave!!💪_* [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 & *_Sumeeluv_* www.Seemaluv.wapka.me *_@Assalamu Alaikum, ina mai mik'a godiya ta agareki RUFAIDA YUSUF. Naji dad'i sosai matuk'a da yadda kika nuna soyayyarki ga JAMEESHA ' bama JAMEESHA kad'ai ba hardani, gaskiya munji dad'i sosai JAMEESHA tana godiya sosai..._* *45-46* A haka bacci yayi awon gaba dasu. *Washe gari* Da sassafe ' su Fadwa suka tashi, sai da sukayi sallah tukunna sukayi wanka ' Fadwa ce ta fara shiryawa sannan ta shiga kitchen domin had'a breakfast, Ta na cikin had'a tea ne Yaya Khaleel ya shigo . Cikin muryar rashin lafiya ' yayi mata magana, "Fadwa ' please ki had'a mun Coffee yanzu, ki kawomin d'akin...." Bai kaga k'arasawa ba ' amai ya taso mashi, cikin sauri ya k'arasa wajen sink d'in kitchen ' yaita kakarin amai. Cikin hanzari ' Fadwa ta d'ibi ruwa a cup, ta tsiyaya ruwan a tafin hannun ta, ta fara shafa mashi asaman kanshi. "Sannu Yaya Khaleel." Yawwa kawai yace ' sannan yabar kitchen d'in ya wuce d'akin shi. Nan tayi sauri ta had'a mashi Coffee d'in ba tare data k'arasa had'a masu kayan breakfast d'inba. Fadwa barin kitchen d'in tayi ' ta nufi d'akin Yaya Khaleel rik'e da cup a hannun ta, ciki ta shiga ta iske shi kwance saman gado ' rik'e da cikin shi, sannan ta sami waje ta zauna a bakin gadon. "Yaya Khaleel ' gashi na kawo." Tashi yayi ya zauna ' tukunna ya karb'a Coffee d'in ya rik'e a hannun shi. "Ki bud'e wancen drower d'in, zakiga Cimetadine ki d'auko min." Yayi mata nuni da yatsar shi ' haka yasa ta doshi wajen kai tsaye, ta d'auko maganin sannan ta dawo ta mik'a mashi. Harta juya zata wuce ya tsaida ta cewa, "Ina kuma zakije Fadwa?" Yanayin yadda yayi maganar ne ' yasa tajin tausayin shi sosai, hakan yasa ta juyo ta kalleshi tare da cewa. "Na'am?" "Baki bani ruwa ba ' zaki wuce kuma." "Bari in kawo ma." Juyawa tayi zata fita ' da niyyar wucewa kitchen, ya tsaida ita. "Ina zakije kuma? Bayan ga robar ruwa anan," Babu musu ta dawo ' ta d'auki robar ruwan ta mik'a mashi, sannan shi kuma ya b'alli maganin yasa a baku ta zuba mashi ruwan ya kora, Fadwa wani yarrrr takeji ' tsigar jikin sai tashi takeyi, don kuwa batason magani a rayuwar ta kokad'an. Yaya Khaleel ' sai a wannan lokacin ya kalli kwalliyar da ke fuskar Fadwa, a wannan lokacin ne yaji kishinta ya fara shiga cikin zuciyar shi 'Fadwa kam harta juya zata wuce yasake tsaidata, sai da ta yatsine fuska sannan ta juyo. "Dama a haka kike tafiya school d'in," Nan ta tsaya tana duba jikinta. "A'a zan sanya gele ai." "Nup! Ba dressing d'inki nake nufi ba, kwalliyar da kika cab'a nakeso ki gogeta yanzun nan." Sunkuyar da kai tayi ' tare da turo k'aramin bakin ta. "Ga tissue cen ' ki d'auka ki share wannan janbakin dake kan lips d'inki." Kallon wajen da tissue d'in yake tayi, sannan ta sake sunkuyar da kanta. "Yaya Khaleel plea..." Bata k'arasa ba ya daka mata tsawa. "Bakiji abinda nace maki bane?" Cikin tsoro ' ta d'auki tissue d'in ta zara ta goggoge bakin ta. "Na share." "Ke am not joking ' ko sokike in tashi maki?" Ta girgiza mashi kai ' sannan ta matsa gaban mirrow d'in tana gogewa, ganin yak'i goguwa ne ta gane cewa lallai 24hrs ta shafa a bakin ta ' cikin fargaba ta juyo ta kalleshi suka had'a ido. "Yaya Khaleel ' yak'i fita amma don Allah kayi hak'uri bazan sake sawa ba." Nan take ya diro daga gadon ' gami da cewa. "No ai saiya fita yau d'in nan." A hankali yakeyo kanta ' tanaja da baya, Sai da yaji ya k'ureta a bango tukunna ya kamo k'ugunta. Ganin haka yasa Fadwa tsorata sosai ' k'ok'arin k'wacewa takeyi amma ta kasa ' Yaya Khaleel kuwa k'ok'arin kissing d'inta yakeyi amma tak'i bashi had'in kai. "Ke!" Ya daka mata tsawa ' cikin tsoro ta d'ago kai ta kalleshi. "Bazaki daina wannan fizge fizgen ba?" Hawaye kawai ke tsiyaya a fuskarta. " Ya Khaleel ' kayi hak'uri don Allah, ka barni in wuce ' bazan sake sawa ba i promise." Jikinta rawa kawai yakeyi ' hakan yasashi sakin ta cikin sauri, gami da juya mata baya. "Get out!" ya fad'a cikin tsawa, Fadwa sauri tayi ta fita cikin rawar jiki ' ta koma kitchen tana maida numfashi. Sunan ta taji ankira ' haka yasa tayi saurin juyowa, don ta duba waye. "Are you Okay?" ganin Yaya Farook ne yasa tayi saurin share hawayen ta ' tare da cigaba da had'a tea d'in. "Of cause." Ta fad'a a tak'aice sannan ta cigaba da abinda takeyi. Abin ne yabawa Yaya Farook haushi ' yasashi k'arasowa kitchen d'in cikin fushi. "Bazaki fad'amin abinda ke damunki ba!" Fadwa banza tayi ta kyaleshi ' ta zuba tea d'in cikin plast, sannan ta d'auka zata wuce ya rik'eta. "Ki fad'amun abinda ke damunki mana Fadwa.!" Nan ta d'aga kai ta kalleshi ' tare da ajiyar zuciya. "Ya Farook ' ni babu abinda ke damuna, kuka kuma da kaga inayi wannan tsakani nane da wanda zan aura." Tana gama fad'in haka ta fizge hannun ta ta wuce, ba tare da ta tsaya ko inaba ta wuce parlor ' ta ajiye plast d'in, sannan ta koma d'akin su don sanarwa Ilham. Tana shiga suka cikaro da Ilham tana k'ok'arin fitowa. "Thought ko baki gama shiryawan bane," Cewar Fadwa. Juyawa Fadwa tayi suka tafi parlon a tare, suka zauna a dinning table. Zaman su keda wuya ' su Umma da Abba suka shigo parlon, sai da suka zauna sannan Fadwa da Ilham suka gaishesu. "Yawwa Fadwa idan kin tafi School ' ki nemi permission subaki hutu, don yau nakeson a fara shirye-shiryen bikin nan." To kawai Fadwa ta iya cewa ' don kuwa sai yanzu ne takejin damuwa a cikin zuciyarta. A gaban idonta Umma ta d'aga waya ta fara kiran dangi tana sanar dasu bikina ' wata kunya ce tazo mata had'e da bak'in ciki, yasa tayi zambur ta tashi tsaye. "Ilham tashi haka nan ' wallahi lokaci ya k'ure mana yau." Tashi Ilham tayi ta d'auki cups d'inda sukayi amfani dashi sannan ta zarce kitchen ita kuma Fadwa ta wuce d'aki don d'aukar handbag d'inta da gele. Su Fadwa basu wani b'ata lokaci ba suka fita driver ya d'aukesu suka bar gidan zuwa school. Bayan driver ya sauke su a school ne ' suka shige class cikin sauri, duk d'aukan su akwai lecturer a cikin. Saida suka shiga suka iske aji kowa sharholiyar shi yakeyi, tukunna suka sami waje suka zauna. "Ilham kince zaki fad'amin yadda kukayi da Abba jiya." "Hm aikedai bari kawai ' Abba cewa yayi in fad'awa Al'ameen cewa yanason ganin shi, don idan akayi bikin ki da one-week za'ayi nawa." "Toh Allah ya kaimu ' but ninaso ace tare za'a aurar damu wallahi." Wata uwar harara Ilham ta watsama Fadwa ' haka yasa Fadwa darawa kad'an, sannan tad'an bigi kafad'anta. Suka cigaba da surutun su ' kafin wani malamin ya shigo. *** *** *** *** *Around 1:54pm* Fadwa ta mik'e tsaye daga seat d'inta ganin lecturer na ciki ne yasa ta d'auki permission d'in fita. Kai tsaye ta wuce Office d'i shugaban school d'in ta sanar da ita komai, sannan akayi signing wata takarda ' aka bawa Fadwa. Koda ta fito daga Office d'in ta iske antashi duk an watse, sai Ilham ne kawai dake tsaye a k'ofar class take jiranta. Cikin sauri ta k'arasa wajen ' ta karb'i handbag d'inta sannan suka nufi inda driver ke tsaye yana jiransu. Shiga motar sukayi a gajiye ' tukunna yajasu ya maidasu gida, saida sukaji yayi packing ' sannan suka fito daga motar suka nufi cikin gida. Fadwa na bud'e k'ofar parlon taji wani shock a jikinta cak ta tsaya a wajen ' don ganin yadda mutane suka cika parlon , Ilham abinne ya bata mamaki ganin yadda Fadwa ta tsaya awajen. "Ke don Allah meye haka ' ji yadda kikasa mutane sunata kallon mu," Ilham gaishe su tayi da hanya ' sannan itama Fadwa ta gaishesu, Ilham ganin Fadwa tak'i tafiyane yasa ta kama hannunta ta jata suka wuce d'akin su. Bayan shigarsu d'akine Fadwa ta fad'a saman gado cike da gajiya. "ai kwanciya bai gankiba tukunna." "Kamarya?" Fadwa tayi tambayar ta k'ok'arin gyara kwanciya. "eh tashi zakiyi muje mu gyara d'akin saukan bak'i , don nasan ba wani datti yayyi ba k'urace kawai, don wallahi bazan iya sharing toilet ba ' kina gani harda mutane k'auye akazo, yoo koma mutanen birnin nefa?!" Fadwa ajiyar zuciya ta sauke ' tare da cewa. "To nidai yanzu ki daure kije ki farayi ' don wallahi agajiye nake." "to naji." Har Ilham ta tashi zata bar d'akin, sai kuma ta tsaya gamida juyowa. "Yawwa Fadwa ya kamata fa ' muyi arranging yadda za'ayi KAMU." "Eh jeki dawo dai ' koma menene saimuyi magana akai koh." Ilham ficewa tayi daga d'akin don zuwa gyarawa bak'i inda zasuyita kara kainan su, Fadwa kuwa nan bacci mai dad'i ya d'beta. *Dedicated To My Fan's* *_Seemaluv the brave💪_*😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *47-48* *Around 4:00pm* Fadwa ta farka daga bacci ' tashi tayi cike da mik'a da hamma, a zaune taga Ilham tana karanta english novel. "Ilham bak'in nan sun tafi ne? Naji banji hayaniya ba." "Eh basu dad'e da wucewa ba amma zasu dawo gobe." Fadwa saukowa tayi daga saman gado ta nufi bathroom da niyyar yin alwala ' Ilham ta tsaida ita da cewa. "Fadwa guess what?" Juyowa tayi ta kalleta cike da tambaya a idonta. "Meye?" "Anan zaku tare!" "Kamarya?" "Yes ' Abba yasa a gyara muku d'ayan part d'in nan." Nan Fadwa tayi shuru nad'an lokaci sannan tace. "Koshh!" "Kosh kamarya ' ke wallahi don dai bakije kin duba bane, yafi wannan part d'in kyau." "Zan duba." Abinda Fadwa ta iya cewa kenan ta shige bathroom, Ilham ta cigaba da karatun ta. Umma ce ta shigo cikin d'akin nasu ta sami waje ta zauna sannan tace. "Ina Fadwa?" "Ta shiga bathroom." "To dama Yayan kune Farook ' yace kuyi masa addua jirgin shi zai d'aga yau." "Laaa Umma ' tun yau ya wuce d'in? Allah sarki Yaya Farook, aikam zamuyi ta yimashi addu'a. "Idan Fadwa ta fito ki sanar ita." To kawai Ilham tace cike da murmushi ' sannan Umma ta bar d'akin. Cikin d'an lokaci k'alilan Fadwa ta fito daga bathroom, Saida Ilham ta jira ta idar da sallah tukunna. "Fadwa kinsan kuwa Yaya Farook ya tafi?" Wani abune ya cokari k'irjinta ta rasa ko menene, Cike da mamaki ta juyo ta kalli Ilham. "Ya tafifa kikace! Zuwa ina?" "Bangladesh mana." Nan gabanta ya sake fad'uwa, nan take hawaye suka fara yimata zarya a fuska. "He left without even calling me! He left without telling me!! Ilham ki fad'amin wasa kikeyi please." Ilham tashi tayi tare da kamo hannunta suka zauna, Sannan Fadwa ta yaye hijab d'in jikinta. "Komai yai zafi ' to maganinsa Allah Fadwa, meyasa bazaki zama mai tawakkali ba?" "Ilham na yarda da k'addara kuma nina yarda cewa Yaya Farook ba mijina bane, amma Ilham meyasa zai tafi bai fad'amin ba? Meyasa?" Ilham sharewa Fadwa hawaye tayi ' cike da tausayawa." "Is okay Fadwa ' ni banga abin kuka ba anan, may be yanada reason d'in yin haka." Kai kawai Fadwa ta daga mata ' alaman Eh. "Hakane ' to yanzu kinsan me za'ayi Ilham? Mu tashi driver ya kaimu ' muje musa a fara buga mana invitation card d'in, hope dai akwai abinci?" "Eh akwai ' don naga bak'in nan sunyi kuma zaikai har dare." Yawwa Fadwa tace ' sannan suka tashi tare da rufe jikinsu da gele, suka fita wajen garage. Anan suka iske Yaya Khaleel a zaune yana shan iska da waya a hannu ' baima lura da suba, sannan suka nufi wajen driver kai tsaye. "Yawwa don Allah taso zaka kaimu wani waje." Cewar Ilham, Cikin hanzari ya tashi ' rik'e da car-key a hannun shi, ga bud'e motar suka shiga. Bayan shigar sune ' suka fad'a mashi inda zai kaisu. Basu suka dawo gida ba ' sai wajen *7:30pm*, sakamakon tsayawan da sukayi aka gama musu nan take. Bayan driver yayi packing ne suka fito, Ilham ta farajin fargaban shiga gida. "Wai don Allah miye haka kikeyi Ilham? Mun riga mun girma fa! Mu shiga kawai ninasan abinda zan fad'a tunda dai ga invitation cards a hannun mu." Haka nan dai Ilham ta yarda suka shiga cikin gida, shigar su parlor suka iske Umma da Yaya Khaleel ' a zaune ya wani had'e rai. Sallama sukayi a tare cike da ladabi. "Sannu da gida Umma." Cewar Fadwa, Yawwa Umma tace ' sannan suka d'auki hanya zuwa d'akin cike da fiskewa😎, Yaya Khaleel ya tsaida su. "Daga ina?" Fadwa ce ta juyo cike da tsoro ' sannan ta koma wajen Umma ta zauna gamida nuna mata invitation cards d'in. "Umma ' kinga abinda ya tsaida mu nan, inba haka ba wallahi da tuntuni mun dawo." Murmushi kawai Umma tayi ' cike da fara'a tace. "Amma ko kinyi dabara Fadwa ' za'aje a rabawa k'awaye kenan?" "Eh Umma' da yake muna so muyi wani event ne (*KAMU*), shiyasa." "To shikenan Allah ya kaimu." "Ameen.!" Abinne ya k'ufule Yaya Khaleel, cike da b'acin rai yace. "Babu wanda zai had'a wani party a gidan nan, Walima kawai za'ayi." Salati Fadwa ta shiga a cikin zuciyarta ' suka had'a ido da Ilham. "A'a bazaka hanasu yiba Khaleel, kaidai idan bakkada ra'ayi shikenan ' amma su zasuyi." Cewar Umma, Yaya Khaleel ' tashi yayi tare da cewa. "Umma ke kike goya masu baya ' suna raina mutum." Sannan yasa kai zai fita waje ' Umma ta tsaida shi. "Ina zakaje? Ko ina zakaje aikabari kaci abinci ko ' kafin ka fita." "A'a Umma ' akwai wacc..infact ma a restaurant zanci a binci." "Toh ai shikenan." Abinda Umma tace kenan ' sannan yasa kai ya fita, ita kuwa Fadwa a zuciyar ta cewa. "Ahab! Wajen wannan ballagazar zaije ' wai ita Lubna." Tana gama ayyana hakan ta mik'e tsaye da niyyar wucewa, Umma tace. "Fadwa ki kawomin abinci inci ' na farajin yinwa." To tace sannan sannan ' ta yaye gelenta ta mik'awa Ilham tare da Invitation cards d'in. "Don Allah wucemin dasu d'aki, ni bara inzarce kitchen kawai." Ehem ' Ilham tace sannan ta karb'a ta wuce dasu d'aki ita kuma ta shige kitchen. *** *** *** *** *** A kwana a tashi ' gashi yau saura kwana d'aya kacal, bikin *Fadwa&Yaya Khaleel*. Fadwa ce ke zaune a parlor ' tare da mai lallee, k'awaye zagaye da ita ' Ilhan kuwa tana gefe tana video Covering d'inta. K'awaye ko wacenta da shirinta tazo ' don kuwa *Around 4-5:00pm* za'a tafi KAMU. Haka aka gyara Fadwa ' tayi kyau sosai, sannan Ilham ta kira makeup artist ta zo taimasu kwalliya ta gani ta fad'a. *4:00pm* Lokacin tafiya wajen kamu yayi ' har wasu daga cikin k'awayen sun fara tafiya, Fadwa ta tashi ta nufi d'akin Yaya Khaleel. Bud'e k'ofar tayi without any tension, ta shiga tare da yin sallama ya amsa ba tare da ya kalleta ba ' ganin shi tayi daga shi sai singlet sai boxer. Fadwa tsayawa tayi daidai wajen k'ofa ' ita bata k'arasa cikin d'akin ba ta sunkuyar da kanta k'asa tana wasa da y'an yatsunta. Jin shurun yayi yawa ne yasa ya d'ago kai ya kalleta ' Wow ya furta a cikin ranshi don ba k'aramin kyau tayi. "Lafiya?" "Yaya Khaleel ' dama lokacin tafiya wajen kamu d'in ne yayi, ti shine...." Ya dakatar da ita cikin fad'a,. "Karma ki k'arasa, angaya miki banda aikin yine? Nan k'walla ta ciko mata cikin idanuwan ta. "Yaya Khaleel please!!" "Fitarmun daga d'aki please hutawa nakeson yi." Juyawa tayi ' ta fita ba tare da tace komai ba, turo mashi k'ofa tayi sannan ta share hawayen ta ' ta wuce d'aki. Yaya Khaleel murmushi yayi har saida hak'aran shi biyu suka fito. Sannan ya fad'a bathroom don yin wanka. *Dedicated To My Fan's* 😜😜😜💪 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 & *_Sumeeluv_* www.Seemaluv.wapka.me *_@Assalamu Alaikum, ina mai mik'a godiya ta agareki RUFAIDA YUSUF. Naji dad'i sosai matuk'a da yadda kika nuna soyayyarki ga JAMEESHA ' bama JAMEESHA kad'ai ba hardani, gaskiya munji dad'i sosai JAMEESHA tana godiya sosai..._* *45-46* A haka bacci yayi awon gaba dasu. *Washe gari* Da sassafe ' su Fadwa suka tashi, sai da sukayi sallah tukunna sukayi wanka ' Fadwa ce ta fara shiryawa sannan ta shiga kitchen domin had'a breakfast, Ta na cikin had'a tea ne Yaya Khaleel ya shigo . Cikin muryar rashin lafiya ' yayi mata magana, "Fadwa ' please ki had'a mun Coffee yanzu, ki kawomin d'akin...." Bai kaga k'arasawa ba ' amai ya taso mashi, cikin sauri ya k'arasa wajen sink d'in kitchen ' yaita kakarin amai. Cikin hanzari ' Fadwa ta d'ibi ruwa a cup, ta tsiyaya ruwan a tafin hannun ta, ta fara shafa mashi asaman kanshi. "Sannu Yaya Khaleel." Yawwa kawai yace ' sannan yabar kitchen d'in ya wuce d'akin shi. Nan tayi sauri ta had'a mashi Coffee d'in ba tare data k'arasa had'a masu kayan breakfast d'inba. Fadwa barin kitchen d'in tayi ' ta nufi d'akin Yaya Khaleel rik'e da cup a hannun ta, ciki ta shiga ta iske shi kwance saman gado ' rik'e da cikin shi, sannan ta sami waje ta zauna a bakin gadon. "Yaya Khaleel ' gashi na kawo." Tashi yayi ya zauna ' tukunna ya karb'a Coffee d'in ya rik'e a hannun shi. "Ki bud'e wancen drower d'in, zakiga Cimetadine ki d'auko min." Yayi mata nuni da yatsar shi ' haka yasa ta doshi wajen kai tsaye, ta d'auko maganin sannan ta dawo ta mik'a mashi. Harta juya zata wuce ya tsaida ta cewa, "Ina kuma zakije Fadwa?" Yanayin yadda yayi maganar ne ' yasa tajin tausayin shi sosai, hakan yasa ta juyo ta kalleshi tare da cewa. "Na'am?" "Baki bani ruwa ba ' zaki wuce kuma." "Bari in kawo ma." Juyawa tayi zata fita ' da niyyar wucewa kitchen, ya tsaida ita. "Ina zakije kuma? Bayan ga robar ruwa anan," Babu musu ta dawo ' ta d'auki robar ruwan ta mik'a mashi, sannan shi kuma ya b'alli maganin yasa a baku ta zuba mashi ruwan ya kora, Fadwa wani yarrrr takeji ' tsigar jikin sai tashi takeyi, don kuwa batason magani a rayuwar ta kokad'an. Yaya Khaleel ' sai a wannan lokacin ya kalli kwalliyar da ke fuskar Fadwa, a wannan lokacin ne yaji kishinta ya fara shiga cikin zuciyar shi 'Fadwa kam harta juya zata wuce yasake tsaidata, sai da ta yatsine fuska sannan ta juyo. "Dama a haka kike tafiya school d'in," Nan ta tsaya tana duba jikinta. "A'a zan sanya gele ai." "Nup! Ba dressing d'inki nake nufi ba, kwalliyar da kika cab'a nakeso ki gogeta yanzun nan." Sunkuyar da kai tayi ' tare da turo k'aramin bakin ta. "Ga tissue cen ' ki d'auka ki share wannan janbakin dake kan lips d'inki." Kallon wajen da tissue d'in yake tayi, sannan ta sake sunkuyar da kanta. "Yaya Khaleel plea..." Bata k'arasa ba ya daka mata tsawa. "Bakiji abinda nace maki bane?" Cikin tsoro ' ta d'auki tissue d'in ta zara ta goggoge bakin ta. "Na share." "Ke am not joking ' ko sokike in tashi maki?" Ta girgiza mashi kai ' sannan ta matsa gaban mirrow d'in tana gogewa, ganin yak'i goguwa ne ta gane cewa lallai 24hrs ta shafa a bakin ta ' cikin fargaba ta juyo ta kalleshi suka had'a ido. "Yaya Khaleel ' yak'i fita amma don Allah kayi hak'uri bazan sake sawa ba." Nan take ya diro daga gadon ' gami da cewa. "No ai saiya fita yau d'in nan." A hankali yakeyo kanta ' tanaja da baya, Sai da yaji ya k'ureta a bango tukunna ya kamo k'ugunta. Ganin haka yasa Fadwa tsorata sosai ' k'ok'arin k'wacewa takeyi amma ta kasa ' Yaya Khaleel kuwa k'ok'arin kissing d'inta yakeyi amma tak'i bashi had'in kai. "Ke!" Ya daka mata tsawa ' cikin tsoro ta d'ago kai ta kalleshi. "Bazaki daina wannan fizge fizgen ba?" Hawaye kawai ke tsiyaya a fuskarta. " Ya Khaleel ' kayi hak'uri don Allah, ka barni in wuce ' bazan sake sawa ba i promise." Jikinta rawa kawai yakeyi ' hakan yasashi sakin ta cikin sauri, gami da juya mata baya. "Get out!" ya fad'a cikin tsawa, Fadwa sauri tayi ta fita cikin rawar jiki ' ta koma kitchen tana maida numfashi. Sunan ta taji ankira ' haka yasa tayi saurin juyowa, don ta duba waye. "Are you Okay?" ganin Yaya Farook ne yasa tayi saurin share hawayen ta ' tare da cigaba da had'a tea d'in. "Of cause." Ta fad'a a tak'aice sannan ta cigaba da abinda takeyi. Abin ne yabawa Yaya Farook haushi ' yasashi k'arasowa kitchen d'in cikin fushi. "Bazaki fad'amin abinda ke damunki ba!" Fadwa banza tayi ta kyaleshi ' ta zuba tea d'in cikin plast, sannan ta d'auka zata wuce ya rik'eta. "Ki fad'amun abinda ke damunki mana Fadwa.!" Nan ta d'aga kai ta kalleshi ' tare da ajiyar zuciya. "Ya Farook ' ni babu abinda ke damuna, kuka kuma da kaga inayi wannan tsakani nane da wanda zan aura." Tana gama fad'in haka ta fizge hannun ta ta wuce, ba tare da ta tsaya ko inaba ta wuce parlor ' ta ajiye plast d'in, sannan ta koma d'akin su don sanarwa Ilham. Tana shiga suka cikaro da Ilham tana k'ok'arin fitowa. "Thought ko baki gama shiryawan bane," Cewar Fadwa. Juyawa Fadwa tayi suka tafi parlon a tare, suka zauna a dinning table. Zaman su keda wuya ' su Umma da Abba suka shigo parlon, sai da suka zauna sannan Fadwa da Ilham suka gaishesu. "Yawwa Fadwa idan kin tafi School ' ki nemi permission subaki hutu, don yau nakeson a fara shirye-shiryen bikin nan." To kawai Fadwa ta iya cewa ' don kuwa sai yanzu ne takejin damuwa a cikin zuciyarta. A gaban idonta Umma ta d'aga waya ta fara kiran dangi tana sanar dasu bikina ' wata kunya ce tazo mata had'e da bak'in ciki, yasa tayi zambur ta tashi tsaye. "Ilham tashi haka nan ' wallahi lokaci ya k'ure mana yau." Tashi Ilham tayi ta d'auki cups d'inda sukayi amfani dashi sannan ta zarce kitchen ita kuma Fadwa ta wuce d'aki don d'aukar handbag d'inta da gele. Su Fadwa basu wani b'ata lokaci ba suka fita driver ya d'aukesu suka bar gidan zuwa school. Bayan driver ya sauke su a school ne ' suka shige class cikin sauri, duk d'aukan su akwai lecturer a cikin. Saida suka shiga suka iske aji kowa sharholiyar shi yakeyi, tukunna suka sami waje suka zauna. "Ilham kince zaki fad'amin yadda kukayi da Abba jiya." "Hm aikedai bari kawai ' Abba cewa yayi in fad'awa Al'ameen cewa yanason ganin shi, don idan akayi bikin ki da one-week za'ayi nawa." "Toh Allah ya kaimu ' but ninaso ace tare za'a aurar damu wallahi." Wata uwar harara Ilham ta watsama Fadwa ' haka yasa Fadwa darawa kad'an, sannan tad'an bigi kafad'anta. Suka cigaba da surutun su ' kafin wani malamin ya shigo. *** *** *** *** *Around 1:54pm* Fadwa ta mik'e tsaye daga seat d'inta ganin lecturer na ciki ne yasa ta d'auki permission d'in fita. Kai tsaye ta wuce Office d'i shugaban school d'in ta sanar da ita komai, sannan akayi signing wata takarda ' aka bawa Fadwa. Koda ta fito daga Office d'in ta iske antashi duk an watse, sai Ilham ne kawai dake tsaye a k'ofar class take jiranta. Cikin sauri ta k'arasa wajen ' ta karb'i handbag d'inta sannan suka nufi inda driver ke tsaye yana jiransu. Shiga motar sukayi a gajiye ' tukunna yajasu ya maidasu gida, saida sukaji yayi packing ' sannan suka fito daga motar suka nufi cikin gida. Fadwa na bud'e k'ofar parlon taji wani shock a jikinta cak ta tsaya a wajen ' don ganin yadda mutane suka cika parlon , Ilham abinne ya bata mamaki ganin yadda Fadwa ta tsaya awajen. "Ke don Allah meye haka ' ji yadda kikasa mutane sunata kallon mu," Ilham gaishe su tayi da hanya ' sannan itama Fadwa ta gaishesu, Ilham ganin Fadwa tak'i tafiyane yasa ta kama hannunta ta jata suka wuce d'akin su. Bayan shigarsu d'akine Fadwa ta fad'a saman gado cike da gajiya. "ai kwanciya bai gankiba tukunna." "Kamarya?" Fadwa tayi tambayar ta k'ok'arin gyara kwanciya. "eh tashi zakiyi muje mu gyara d'akin saukan bak'i , don nasan ba wani datti yayyi ba k'urace kawai, don wallahi bazan iya sharing toilet ba ' kina gani harda mutane k'auye akazo, yoo koma mutanen birnin nefa?!" Fadwa ajiyar zuciya ta sauke ' tare da cewa. "To nidai yanzu ki daure kije ki farayi ' don wallahi agajiye nake." "to naji." Har Ilham ta tashi zata bar d'akin, sai kuma ta tsaya gamida juyowa. "Yawwa Fadwa ya kamata fa ' muyi arranging yadda za'ayi KAMU." "Eh jeki dawo dai ' koma menene saimuyi magana akai koh." Ilham ficewa tayi daga d'akin don zuwa gyarawa bak'i inda zasuyita kara kainan su, Fadwa kuwa nan bacci mai dad'i ya d'beta. *Dedicated To My Fan's* *_Seemaluv the brave💪_*😜 [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *53-54* *AROUND 4:00PM* Yaya Khaleel ya dawo gida ya iske duk mutane sun watse ' sai wata y'ar tsohuwa wacce ta manyan ta zaune a parlor. kai tsaye ya wuce sashen shi ya cire babban rigarshi, sannan ya fito parlor suka had'e da Umma wacce dama shi take jira. "Khaleel daga ina?" "Amm Umma yanzu nake dawo wa ' daga wajen abokai na, zanje sashe na.." Ya fad'a yana sosa k'eya. "Ai indai da kunya to anjita. Cewar tsohuwar da ke zaune a wajen, Yaya Khaleel juyawa yayi ya kalleta ' sannan ya maida kallon shi kan Umma. "Umma wannan wacece kuma?" "Sunan ta Ige ' akwai wasa a tsakanin ku, zata cigaba da zama damu ne anan ' tana d'an taya Ilham aikin da ba'a rasa ba." Ok kawai Yaya Khaleel ya ce ' sannan yasa kai zai fita Umma ta dakatar dashi. "Ina kuma zakaje? Bata tare da mun gama magana ba? Duk zumud'in ne haka?" Murmushi kawai yayi. "To kaje sashen Abban ku yana nemanka yanzun nan." Kai tsaye Yaya Khaleel ya nufi sashen Abba ' a zaune ya hange shi saman kujera, Yaya Khaleel sallama yayi sannan ya shiga. Abban ya amsa cike da fara'a. "Sami waje ka zauna!" Yaya Khaleel k'asa ya zaune cike da ladabi. "Khaleel ' Alhamdulillah yau aka d'aura auren ku da Fadwa kuma ina fatan zaka rik'ayin adalci a tsakanin ku." "Insha Allah Abba." "Kuma inayi maka albishir da cewa ' na bud'e maka company naka na kanka, domin ka rik'a sarrafawa." Yaya Khaleel bud'e baki yayi yana kallon Abba ' cike da mamaki. "Kuma na sama maka ma aikata ' wad'an da zasu rik'a aiki a k'ark'ashin ka yanzu kana zuwa sai dai ka hau aiki, Amma gobe insha Allah zan kaika domin ka ga wajen." Wani ihu Yaya Khaleel ya saki mai kama da kuka ' ya tashi ya rungume Abba cike da jin dad'i. "Abba na gode ' na gode sosai Abba ban tab'a jin dad'i irin na yau ba Abba." "To sakeni mana Khaleel ' so kake ka k'arasa ni?" Cikin sanyin jiki Yaya Khaleel ya koma ya zauna. "Yanzu ka tashi kaje ' dama kiran kenan!" "To shikenan Abba na gode ' Allah ya kaimu goben." Ameen Abba ya ce ' sannan Yaya Khaleel ya tashi ya fita, Parlor ya shigo d'auke da fara'a a fuskar shi zai wuce Umma ta tsaida shi. "Ina zakaje?" "Umma zanyi packing kaya na ne ' zuwa gidana!" "Yayi kyau masu gida!!!" Harya juya zai wuce Ige ta tsaida shi da cewa. "D'an samari naga kana ta fara'a ne! D'an fesa mun inji me aka samo mana." "Company Abba na ya bud'emun." "Ohh shi dama kanunfarin bud'e shi akeyi?" "Hahaha! Kinga illar zama a k'auye kenan, ki tambayi Umma ta fad'a miki ' ni inada abunyi." Wuce wa yayi ya kyaleta ita da Umma ' tana ta k'ok'arin fahimtar da ita. Bayan ya d'auko trolley d'in shi da duk wani abu nashine ya nufi part d'inshi. Karo yaci da k'awayen Amarya zasu koma gida. "Haba kardai har zaku koma!" Dariya sukayi dukkansu sannan d'aya daga ciki tace. "Ango kenan kasha mai ' to ai mun dad'e anan kuma kai kawai Amarya take jira." Murmushi kawai yayi sannan ya kira driver d'in gidan ya umarce shi ya kaisu gida. Godiya sukayi mashi sannan ya shige cikin gidan shi, D'akin shi ya fara shiga ' ya ajiye kayan shi sannan ya nufi d'akin da Fadwa take. Suna cikin hira ne da Ilham sukaji anyi gyaran murya ' hakan yasa Fadwa tayi saurin maida gelenta ya rufe mata fuskar ta. Yaya Khaleel k'araso wa yayi cikin d'akin fuska a d'aure sannan Ilham ta tashi ' ta fita cikin sauri ta wuce sashen su. Ita kuwa Fadwa gabanta dukan uku uku kawai ya keyi ' saboda tsabar fargaba. Yaya Khaleel gefen gadon ya zauna ' ya na kallon irin kyan da tayi cikin gele, Hannu yasa ya yaye gelen ya cigaba da k'are mata kallon. K'ara matsowa yayi kusa da ita yana k'ok'arin sunsunar wuyan ta, tayi saurin matsawa. "Me hakan ke nufi?" Banza tayi ta kyaleshi ' abun yayi matuk'ar b'ata mashi rai sosai, tashi yayi fita daga d'akin ta bishi da kallo. Parlor ya je ya zauna ' ya kunna TV ya na kallo, Haka Fadwa ta k'araci zaman ta a d'aki ita kad'ai har aka kira sallar magrib ta tashi ta cire mayafin ta ' ta shiga bathroom. D'auro alwalar ta tayi ' ta shinfid'a dadduma ta fara sallah, Yaya Khaleel shima tashi yayi ya shiga d'akin shi don yin sallah. Bayan Fadwa ta idar da sallah ne ' ta koma ta zauna a kujerar d'akin Sofa, ji tayi gaba d'aya batajin dad'in zama ita kad'ai hakan yasa ta tashi ta nufi parlor da niyyar fita zuwa sashen su Umma. Suka had'e da Yaya Khaleel zai shigo cikin d'akin, tsayawa cak yayi yana kallon ta yadda surar jikinta suka bayya. "Ina zakije?" "Ammm Yaya Khaleel dama inaso ne inje wajen Ilham in karb'a phone d'ina." "What!? Phone? Saboda ke dama kunya bata ishe ki ba ko? Yau yau da tarewar ki ' zaki kama hanyar yawo ko?" Nan ta sunkuyar da kai ' ba tare da tace komai ba, Sannan ya matso kusa da ita. "Bazaki fita ko nan da cen ba ' har sai nan da 2weeks, kuma babu mai shigowa ya katse mun jin dad'i." D'ago kai tayi ta kalle shi ' da y'ar kwallar ta a cikin ido. "Yaya Khaleel please ' wallahi bazan iya zama ni kad'ai ba shiyasa." "Nidai kinji abinda na fad'a miki." Nan ya juya ya wuce parlor ' yayi zaman shi. Koma wa cikin d'akin tayi zata cire kayan jikinta ta shiga wanka ' taji sallamar Ilham, Abinci ta kawo musu cikin plask Yaya Khaleel ya ansa sannan ya umarce ta data koma inda ta fito ' da gudu Fadwa ta nufo parlon. Ta na isa taja burki ta tsaya ' ganin babu Ilham a wajen sai Yaya Khaleel wanda ke rik'e da plask d'in abincin ya na kallon ta. "Yaya kamar naji muryar Ilham ko?" "Na ce ta koma inda ta fito! Wata matsala ce?" Tsayawa kawai tayi tana mashi kallon mugu ' sannan ta ce. "A'a." Ta juya ta koma d'aki, ta hau cire kayan jikin ta sannan ta d'aura towel ta shiga wanka. Tana cikin wanka ne ' taji an bangad'o k'ofar bathroom d'in, cikin tashin hankali da tsoro Fadwa ta rarumi towel ta rufe k'irjinta k'ok'ari take ta d'aura amma jikinta rawa kawai yake yi. Yaya Khaleel cak ya tsaya a bakin k'ofar yana k'arema jikinta kallo ' ita kuwa babu abin jikin ta keyi sai rawa. Sai da suka kwashe 5minutes a haka ' sannan ya juya ya rufo mata k'ofa ya koma gefen gado ya zauna ' yana sauke ajiyar zuciya. Ji yayi tana shek'a ruwa a jikinta alaman tana gab da fitowa ' haka yasa yayi saurin bud'e wardrope d'inta ya ciro mata wasu fitinan nun sleeping gown shara shara ya ajiye mata su saman gado sannan ya bar d'akin. *Dedicated To Seemaluv's Novel Group*👌👌 *_Love you Gurls So Much_* [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: ....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *_@My Dedication Goes To Tambuwal's Family, How Amazing This Family Iss 😍😍May Allah Guide This Family ' In Any Way.Thank You , Thank You For Your Supports._* *Yours Ever!!! SEEMALUV👄* *By Seemaluv* [4/18, 3:55 PM] Maman Ussey😘: .....🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹 *BABBAN...GIDA*🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_Pure Moment Of Life writers_* © ```Written```       By *_Seemaluv_*👄 www.Seemaluv.wapka.me *57-58* Yaya Khaleel binta yayi da kallo har ta b'ulle zuwa d'aki, Bayan Fadwa ta shiga d'aki ne ta fad'a bathroom tayo wanka tare da yin alwala ' sannan ta fito tayi sallah , Mik'ewa tayi nufi gaban mirror ta zauna ta fara gyara jikin ta. Bayan ta gama ne ta tashi ' ta bud'e wardrope d'in ta ta ciro riga da skirt d'inki mai kyau ta saka a jikin ta gamida kashe d'auri, Tana cikin hakan ne taji ana k'wank'awasa k'ofa ' cikin hanzari ta bar d'akin ta nufi parlor ta bud'e k'ofar. Ilham ce rik'e da kayan breakfast a hannun ta, Shigowa tayi cikin parlon cike da sababi. "Kinyi aure amma mutum bazai huta ba?" Murmushi kawai Fadwa ta bita da shi ' sannan suka zauna Ilham ta mik'a mata ledar da ke hannun ta. "Gashi ' Milk ne da bread da sauran su aciki, inji Umma." Mik'ewa Ilham tayi zata wuce Fadwa ta tsaida ita da cewa. "Tsaya! Mu tafi tare ' ingaida Umma da Abba." To kawai Ilham ta ce sannan suka fita zuwa sashen su Umma ' Ilham a parlor tayi zaman ita da Ige sannan Fadwa ta haura wajen su Umma ta gaishe su. Bayan ta gaishe su ne ' ta dawo parlor ta zauna sannan suka gaisa da Ige. "Y'an nan harkin gama cin amarcin naki ne?" Cewar Ige, "Hmm me kika gani?" "Gani nayi harkin fara fitowa!" Nan ta sunkuyar da kai ' Ilham tashi tayi ta matsa kusa da Ige. "Ai Ige ' daga gani babu wani amarcin da sukaci, Ige Yaya Khaleel fa bak'in rai ne dashi wallahi." Nan Ige tayi zuk'u tana kallon Fadwa. "Y'an nan abinda Ilham ta fad'i gaskiya ne?" Fadwa d'aga kai tayi alaman Eh, Sannan Ige ta sauke ajiyar zuciya. "Lallai wannan shine daidai lokacin da ya dace tsarabar da nai miki ' ki fara aiki da ita." Nan Fadwa da Ilham suka had'a ido, A tare su kace. "Kamarya?" Ige ta bud'e baki kenan zatayi magana Abba ya shigo parlon ' cikin hanzari. "Fadwa tashi kije ki cema Khaleel ' ko ya manta akwai inda zamuje yau ne!" To tace ' sannan ta tashi ta bar sashen cikin sauri, Ta na shiga sashen su ta iske shi a zaune a parlor cikin shadda blue yayi kyau sosai ' waje ta samu ta zauna ba tare da ya d'aga kai ya kalle ta. "Ina kwana Yaya Khaleel?" "Lafiya!" "Amm... sorry na d'anje sashen su Umma ne na gaishe su ' so shine Ige ta tsareni." Banza yayi ya kyale ta ' ya cigaba da kallon shi. "Yaya Khaleel ' Abba ya ce na fad'a maka wai ko ka manta akwai inda zakuje ne?" Jan tsaki yayi kad'an sannan ya mik'e tsaye ya fice, Fadwa bin shi tayi da kallo. Tashi tayi ta d'auki kayan tea d'in ta nufi dinning table da su, Sannan ta wuce kitchen ta d'ebo ruwan zafi a plask ta ajiye ' nan ta zauna ta had'a nata tea d'in ta na sha kafin ya dawo ta had'a mashi nashi. Fadwa ta na cikin haka ne ' Ilham ta shigo rik'e da y'ar k'aramar kwalba a hannun ta, Zama tayi tukunna Fadwa ta aje cup d'in tea d'in ta zo harabar parlor kusa da Ilham ta zauna. "Yaya Khaleel ya fita ko?" Cewar Ilham. "Eh." "To ga wannan ' inji Ige." Ta mik'a mata kwalbar turare ' Fadwa ta karb'a. "Ta ce duk idan lokacin kwanciya bacci yayi ne ' zaki shafa shi kad'an a saman k'irjin ki." "To meye amfanin shi?" "Oh my God! Nikam aida kin bari na gama bayani na ko?" "Uhm! Shikenan ina jinki!" "Yawwa, Bayan kin shafa shi ' to muddin yaji k'amshi turaren zaiji babu wacce yake sha'awa saike, Gaba d'aya zaiyi sanyi ' zaiji babu wacce yake so kamar ki!" Ajiyar zuciya Fadwa tayi ' tare da juya kwalbar turaren cike da tsoro. "Amma Ilham ' ni gaskiya inajin tsoro fa!, Kinga ance ba k'aramar wuya mutum ke sha ba ' kema kanki kinsani." Wata harara Ilham ta watso wa Fadwa. "Ke wai meye haka? Anaso a taimake ki ' kina wani butsarewa haba Fadwa." "A'a nidai bana so ' karb'a ki maida mata abunta, A hakan nina son Yaya Khaleel yana sona." "Oh Allah? A hakan ko? Amma karki manta fa ' yana da budurwa a waje, Saboda haka anan zan aje shi ' idan kinga dama kiyi amfani dashi ' idan kuma kinso ki yar." Nan Ilham ta tashi ta kama haryat fita ' har ta kai bakin k'ofa ta juyo ta kalle Fadwa wacce ke ta nazari. "Kuma banma sake shigowa sashen shi." Fadwa murmushi kawai tayi ' sannan Ilham tayi wuce warta. "Inma baki shigo ba ' aini zaki ganni ne ai." Fadwa tashi tayi ta bar turaren anan wajen ta koma dinning table ta cigaba da shan tea d'in ta. *AROUND 12:00PM* Yaya Khaleel suka dawo gida ' shi da Abba, Abba ya wuce ciki ' shi kuma ya shige sashen shi, A zaune ya iske Fadwa ta na kallo TV. Ganin shigowar shi ne ' yasa tayi saurin mik'ewa tare da yi mashi sannu da dawo wa, Yaya Khaleel bayan ya zauna ne ' Fadwa ta je ta had'o mashi tea don tasan yau kam ya wuni da yunwa. "Yaya Khaleel ga tea d'inka ' kayi hak'uri ban had'a da wuri ba sabo..." Bata kaiga k'arasawa ba ya katse ta da cewa. "Banason dogon surutu plaese." Karb'a yayi ' Fadwa ta koma ta zauna ' sama sama ya sha tea d'in tukunna ya aje a k'asa, Sannan ya jingina da jikin kujera. "Amm... Fadwa Abba ya bud'e mun Company, Kuma Alhamdulillah yau ya kaini wajen na gani ' Amma sai nan da 1week zan fara aiki." "Wow! Alhamdulillah! Yaya Khaleel gaskiya naji dad'i sosai kuma Allah yasa rai a kaiwa." Amin ya furta ' sannan ya tashi zai wuce d'aki tayi saurin tsaida dashi. "Yaya Khaleel to yaushe zaka kaini inga wajen?" Tayi maganar a shagwab'e cikin sanyin murya. "Bazaki je ba!" Nan ta tashi ido cike da k'walla. "Yaya Khaleel ' inaso inga wajen ne please!" "To shikenan naji ' kar kuma ki dameni!" Ya na fad'in haka ya wucewar shi d'aki. Fadwa koma wa tayi zauna ta cigaba da kallon ta. A ranar haka Fadwa ta k'arashi wunin ta ' bata sashin su Umma bata sashen ta. *** *** *** *** *** *** *** *WAJEN K'ARFE 6:30 NA YAMMA* Bayan Yaya Khaleel ya dawo daga masallaci ne ' ya zauna parlor tare da ciro wayar shi yayi dialing number d'in Lubna, Yayi sa'a ringing d'aya tayi ta d'ago tamkar ta na da k'ishin shi. "Baby!." "Hm i was shock and surprise!" "Well...don't be, Lubna you know that i missed you so much right?" "Bawani nan! Bayan kanata cin angon cin ka ' ko zaka cemin baka kwanta da ita ba?" Fadwa da ke bedroom d'in taji kamar motsin mutum a parlor ' haka yasa ta fitowa daga d'akin nata zuwa parlor don ta duba waye. "Haba meyasa zaki rik'a fad'amun haka? Kema kinsan Lubna ba zab'ina bace and she's not my class really..." Haka yayi dai dai ' da isowar ta parlor, Cak ta tsaya jin abinda yake fad'a haka yasa ta fahimci da Lubna yake waya. Sai da ta jira ya gama wayar ' tukunna tayi gyaran murya, Da sauri ya juyo ya kalle ta. "Dama kina ciki ne?" "Eh." Juyawa tayi ta koma d'akin ta ' ta zauna a bakin gado. "Ni nasan dama ba sona kakeyi ba Yaya Khaleel ' amma insha Allah komai ya kusa zuwa k'arshe." Turaren nan ne ya fad'o mata a rai ' haka tayi zambur ta tashi ta nufi parlor, Sam ta manta da akwai Yaya Khaleel zaune a wajen ' kai tsaye ta nufi wajen inda ta san cewa nan ta saki turaren. Ta na ganin shi tayi ajiyar zuciya ' tukunna ta d'auka ta juya ta zata koma d'aki ya tsaida ' haka yasa ga banta yayi mugun fad'uwa ta juyo ta kalle shi a sanyaye. "Meye ne wannan? ' kika zo zaki wuce kamar baki ga mutum ba?" "Babu komai ' fitsari nakeji shiyasa na ke sauri." Tana fad'in haka ta juya ' ta wuce cikin sauri harda k'arawa da gudu, Tana shiga d'aki ta sa key ta kulle ' nan ta cire kayan jikin ta ta fad'a bathroom don yin wanka. B'angaren Yaya Khaleel ' text yayiwa Lubna da Address d'in Company d'in shi don anan zasu koma suna had'uwa. Bayan ya gama ne ' zai tashi ya wuce Ilham ta bud'o k'ofa rik'e da cooler d'in abinci. "Yaya Khaleel Fadwa fa?" "Tana d'akin ta." Ok kawai ta ce ' sannan taje ta ajiye abincin saman dinning table ta zarce d'akin Fadwa. Murd'a handle d'in tayi taji a kwulle. "Kome takeyi oho!" Ilham juyawa tayi ta koma sashen su. *Dedicated To Seemaluv Novel Group 2* 👄👄👄

Share this


Author: verified_user

0 Comments: