Friday, 8 June 2018




hadin Allah complete

Home hadin Allah complete

[4/30, 5:26 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) 1_5 Bismillahir rahmanirrahim Sanye take da wata kodaddiyar atamfa koriya xanin ta kasa arage yake an dinke da zare da allura,ga tiren tallar gyada akai tana ta faman taunar cingam, a haka har ta karasa dai dai wasu yammata saan nun ta, ajiye tiran gyadar tayi gefe tare da janyo takalminta Dan ta kara daure shi da leda, Dan taga ledar ta fara kwancewa, ba Wanda ta kula a cikin wanda ta tadda a wajan ba ta fi minti biyarba gyadar ta tafara karewa sosai mutane suke san gyadar ta, duk da kasancewar ta bata da tsafta hakan baya hana mutane siyan kayanta, musamman gyada da suka san ba ita take soyawa ba kuma a bawo take sannan a leda A hankali take magana wanda in ba kana kusa da ita ba baza ka taba jin me take cewa, mutum sai bakin jini tinda kika zo naga alama ko Biyar baki ba wlh in nice mai gyadar bazan kara samiki ba, a fusace yarinyar da take kusa da ita wuyan ta ta shakuma suka fara dambe, mutanan wajan ne suka taso da gudu dan su rabasu, " ke asabe me ta miki kawai dan neman masifa ki shakumi wuyan ta, wani dattijo ta ya rike hannun ta ke tambayqr ta, Wlh tsokanata take yi" Babu wani nan tin da *NUR* tazo wajan nan babu wanda ta kula taya zakice ta tsokaneki, wata yarinya dake talla a gefe ta fda, duk yadda asabe taso su fahimta suka ki fahimta amma suka ki fahimta saima rashin gaskiya da suke bata, suna hada ido da Nur tai mata gwalo, sannan ta cigaba da matsar kwallah, Cikin fushi asabe ta dau farantin gyadar ta tai gaba, bayan ta saida gyadar ta dau farantin ta tai hanyar gida Garin panisau gari ne mai rahama, ga kuma gonaki, sosai jamaar garin ke da sannar su Allah kuma ya azurta garin da mahauta, duk inda kika zaga zakiga ana saana, musamman wajan kofa sannan kuma da fada duk wuraran sanaa ne, kuma a wajan yammata garin ke zama dan saida abinci ko kuma wata sanaa tasu ta hannu, Mutanan panisau akwai zuciyar neman na kansu ko yaro karami ne zaka gansa da sanaarsa, sosai garin yake da niima Tana tafe tana waka har ta karasa gdan su, ko sallama Nur ba tayi ba ta shigo gda direct kitchen ta nufa wata roba ta dakko zama tayi a kasa ta fara cin abinci a nutse kadan taci abinci ta maida kwanon kitchen ta goge hannun da taci abinci dashi akanta, sannan ta shiga cikin dakin su Ku kasance da mu dan jin abinda labarin ya kunsa By Shamsia salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:27 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Page 6-10 Umma Umma Umma kina Ina ne, Nur ta fda tana daga labulan dakinsu, " ban sani ba ke wai baza kiyi hankali ba ne , kullum girma fa kike karayi, dan iskanci uban me ya hana ki yi sallama kawai zaki hau kwallan kira kamar baki san inda nake ba, wlh Nur ki fita idona na rufe duk sanda na danke ki baza ki ji da dadi ba, turo baki Nur tayi ta dauke kanta kamar ba ita akewawa maganaba, au dan wulakanci ina miki magana kina turan baki sbda kin raina mutane koh, umma ta fada tana janyo ta " wayyo umma kiyi hakuri bazan kara ba dan Allah kar ki dake ni, tureta umma tayi ta mike dan fita " haka kawai dan an tsani mutum sai ana dukanshi, wlh ba dan nasan umma ce ta haifqn ba Allah sai nace kishiyar uwa ce, dan dai kawai muna kamane, dariya ta kusa subucewa umma amma ta dake ta juyo, Nur me kikace, hanjin cikin nur ne suka mada ummana ba magana fa nayiba haka nace ki soya gyada da yawa gobe dan yau ana ta nema sosai, Kuma ki kace baki magana ba, mantawa nai ummana Dariya kawai umma tai tayi waje tana rokon Allah ya shirya mata yarta Malam habu ne ya turo kekensa har cikin gda da sallama ya shigo gdan, umma sake zaune akan tabarma ta amsa masa sallamarsa, bayan ya jingine keken ya zauna kusa da umma, " sannu da zuwa malam" yauwa dije, ina nur ne, na aiketa gdan atine ta karbo mun kudi tin kan ai kiran mangariba kaga yanxu har kusan 8:30 amma bata dawo ba, umma ta fda tana daga labule dan ganin ko karfe nawa, " Allah dawo da ita lpya" Amin malam, umma ta fda tana mikewa dan dakkowa malam habu abincin sa Idan na zagayo idan na zagayo idan na zagayo ace tafi kanwar maza ni kanwar maza bazan ki maza ba ko yanxu ma daga gun mazan na........ Dukan da umma tai wa nur a bayane yasa kin karasa wakar, nur sau nawa zance ki daina shigo min gda da waka gashinan ko kallon gabanki ba kyayi kin zubar min da miya, Ganin abba a zaune yasa ta karasa da gudu ta fda kansa tana kuka, rarashinta dady ya fara yi hkri nur amma daga yau kar na kara ganin kin shigo gda bbu sallama, toh Abba, Yauwa yar gdan Abba tashi ki wanko hannun ki muci abinci, ba musu ta wanko hannunta suka fara cin abinci, baifi loma hudu nur tayi ba ta dauke hannunta daga abinci, " me zan gani yar gdan abba naga kin dauke hannunki" eh abba na koshi ne" dije ya kamata a nemowa nur maganin cin abinci bnsan meye masalar yarinyar nan ba kwata kwata bata san cin abinci, zan tqmbayi atine ko tasan India zaa samu maganin dan nima rashin cin abincin yarinyar nan na damuna, Honey pls ka hakura da tafiyar nan kaga fa yanxu kusan karfe uku gwanda ka bari sai gobe, sweat heart kiyi hakuri nan da panisau ai ba nisa bane dashi, kawai yau zuwa zanyi na ga kaka, insha Allahu gobe zan dawo da wuri, cikin shagwaba ta kara shigewa jikinsa, toh honey ka kula da kanka bnda kallon mata a hanya, kar ki damu sweat heart ai ke kadaice a raina bbu na biyun ki, dariyar jin dadi tayi ta rakoshi har mota tana daga masa hannu har ya tafi By Shamsia salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:27 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Page 11_15 'Cikin mintuna da basufi arba'in ba ya isa garin panisau, daidai bakin tasha yaxo zai wuce kenan wata yarinya ta taho aguje tabi gabansa ba shiri yaja burki ya tsaya, ita kuwa batama san tayi ba, tasha damara da wani dukukkunannan hijab, cikin zafin rai Nura ya fito ya bi yarinyar nan, shakota yayi ya riko gashin kanta, ta waigo ta sauri zata mai rashin kunya, ya dau hanu zai kwada mata mari ina yaji sam bazai iyaba yarinyar tamai kwarjini dayawa. Sakinta yayi tayi gefe tana huci, budar bakinta tace Allah ya isa mugu kawai, cak Nura ya tsaya yakasa aiwatar da komai, haka yayi ta binta da kallo har taje gidin wata bishiya ta dauki tiren gyadarta tayi gaba, sai da ta bace masa sannan ya shiga mota ya karasa gida. Salama alaikun kaka"a'a wanakeji kamar Nura badai kaine tafe da yamman nan ba, "Wlh nine kaka ta shimfida mai tabarma ya zauna, ruwa taje ta kawo mai mai sanyi cikin kwanon sha, ya karba yasha sannan suka gaisa, " ina kuma kishiyar tawa"tana lfy tace agaisheki"ina amsawa Aishatulle, kai kaka kidena batamun sunan mata, "toh mai mata sukayi dariya duka. Suna zaune sunata hira da kakartasa Nur tayi sallama ta shigo tasha damara a kugu, ga wata kwalliya data chaba adole wai tayi wanka kenan, ta gaishe da kaka, ta dinga hararar Nura dake zaune bai ma dago yaga ko wayeba yana ta danna wayarsa, kakata tace Nur me zaa baki?" kaka muka da daddawa da magi, sai lokacin ya dago suna hada ido ta gaa mai harara, kaka ta mike taje dakin ta daukowa Nur aikenta, Nur kuwa kaka na shiga daki tafara zagin Nura shi muma yarasa me yasa yakasa yiwa yarinyar komai kasancewarsa mutum ne wanda bayason raini, tace mugu kawai azzalumi Allah ya isana, dai dai nan kaka ta iso, "ke Nur menaji kina cewa, " a'a kaka waka nakeyi, ta amshi aikanta tayi waje. Sai jinjina sunan yake aransa Nur, tunda yani kaka ta fada shikenan ya ji sunan ya masa dadi kamar yadda yarinyar ta masa kwarnini, da tunani kalakala ya karasa hirarsa da kaka. Da magriba Alh Abubakar kakan Nura ya dawo daga kasuwa, sosai yaji dadiin ganin Nura saboda ya kwana biyu bai zoba, tare sukaci abincin dare sannan sukayi ta hira, karfe tara na dare Nura ya tafi dakinsa dake zaure ya kwanta don hutawa amma me tunanin Nur yaki barin zuciyarsa, dakyar bacci barawo ya sace shi. Misalin karfe sha biyu Nur ta fito sanye da wata bakar doguwar riga duk tasha faci, tana dauke da tiren gyadarta, dai dai kan dakalin gidan Kaka ta hango wannan bakon birnin aikuwa da hanzari ta karasa ta sake yimai tsiwa kamar yadda tamai jiya sannan ta fara tafiya, sai yace Nur taja ta tsaya amma bata juyo ba, cike da mamaki tace to ina yaji sunana"can sai ta tuna niya datane gun kaka, yace bani gyadar ta dari biyu, ta juyo ta aniye tiran tace mai ya diba goma goma ce, ya kwasshi kulli ashirin yabata mudinta ta dau tiranta tayi gaba. Misalin karfe biyar ya shirya sukayi sallama da kaka ya tafi, kafin ya wuce sai dayabi ta tasha ya sayi gyada gun Nur har yace tabar canjin dubu dayace dama, ta dari biyu kuma yasaya. Wlh sai naci ubanki uban waye ya baki kudi, nan ummanta tafara dukanta sai ga abbanta ya shigo, nan Nur ta nufi gunshi tana kuka, lfy dai ko, ina fa lfy malam yarinyar nan ta fara juyen gyada, nan abban ya tambayeta yadda akayi ta fada mai dake ita duk rashin kunyarta da rashin tsabtar ta bata karya. Wannan kenan muje zuwa By shamsiya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:27 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Page 16_20 A gajiye ya shiga gida, tun yana parking mota, Aisha ta fito tasha kwalliya sanye da wani less pink da stoch baki, yayi mata kyau sosai, da hanzari ta karasa gunsa"sannu da zuwa honey, ya dago habarta ya sumbaci goshinta sannu swt heart, nasameki lfy, "lfy lau sweet heart, yasu kaka?" Suna lfy sunce ma agaishe ki"ina amsawa, yana rungume da ita suka karasa falo, dakinsa ya nufa direct toilet ya shiga ya sakarwa kansa shower, tana hada mai abinci akan dinning. Daure da towel ya fito, daya kuma yana goge sumarsa ya zauna ya shafe jikinsa da mai, wadrobe ya bude zai dauki kayan sawa Aisha ta rungumesa ta baya, ya juyo da ita, suna kallon juna, sakarwa junansu murmushi sukayi, ya dauko kayan ta taimaka mai yasa kayan suka nufi dinning, ta zuba mai yadda zai ishe sa. Suna zaune a falo suna hira, Nura na zaune akan capet, inda Aisha take kan kujera, ya juyo yace af na manta, ashe nazo da gyada, da hanzari ya mike ya dauko key motarsa ya nufi waje, jim kadan sai gashi yadawo dauke da daurin gyada, da sauri Aisha ta karba, la!, tasoyu ce ashe sweetheart, kai kawai ya daga mata alamar eh, nan suka fara cin gyadar. Honey a ina kasamo gyada haka mai dadi?, "hmm kodai kaka ce ta baka, " a'a saya nayi gun wata yarinya NUR, Aisha najin sunan taji gabanta ya fadi, amma ta rasa dalili duk da tasan Nura bazai taba son yar kauye ba bare yar talla. Yanaji kinyi shiru?"a'a babu gyadar ce akwai dadi, nan yaji dadi anyaba gyadar Nur, anan ta tashi ta yi daki don tafara hamma.ai kuwa tana tafiya Nura ya fara tuna haduwarsu da Nur, kusan sai karfe sha biyu ya shiga daki, lokacin har tayi bacccinta. Nur kizo maza kije ki kaiwa kaka aikan nan sannan ki siyo mun kubewa, kai dan Allah badama mutun ya huta, dawa kikeyi Nur inace nikike zagi?, nifa badake nake ba tana tura baki ta amshi aikan. Nura ne ya fito sanye cikin kananan kaya, Aisha na zaune afalo misalin karfe tara na safe, da hanxari ta mike don taga alamar fita zaiyi, "Honey sai ina kuma?, ta tambaya atakaice, ba kalli inda take ba yace" panisau zani amma da yamma xan dawo, cikin rashin kuzari tace to baka karya ba, "hanu ya daga mata alamar baya bukata, shan gabansa tayi lfy kuwa honey?ba yadda nasa ba ganinka bane kodai na maka laifine, yayi murmushi ya rungumeta jikinsa, no sweet heart ba abinda kika mun yau koko da kosai nake shaawar sha shiyasa sainaje panisau xan karya, ta gamsu da jawabinsa tare sukaje parking space har ya tada mota tana daga mai hanu. Isar sa keda wuya ya samu kaka ta sauke kokon kuwa, dama yasan daidai lokacin da take karyawa, bayan sun gaigaisa da kakannin nasa ne, ya dubi kaka, " nikam akwai wata yarinya dana sayi gyada gunta ranar ko kin santa, gyadar me dadi, "kodai gyadar Nur ce domin duk garin nan gyadarsu tafi ta kowa dadi, inaga itace domin gyadar tana da dadi, kana sone?, " eh asayaomun ta dubu daya saboda Aisha ma tanaso. Kuyi hakuri abiyo mu anjima By Shamsia salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:28 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Page 26-30 Cikin mota nura ya Shiga ya dakko mata chocolate kwali uku, da murmushi ya karaso inda take " kanwata ga tsarabarko, 😳 zaro ido nur tayi kai yaya nura so kake ummana ta Zane ni tace waya bani, murmushi yayi kanwata Umman mu baza ta dake ki ba kinji, naki wayyan, sanda zaa dakeni ai baka sani ba, nur ta fda tana turo baki, sosai nur ta burge nura, zuwa yanxu dai ya tabbatarwa da zuciyarsa yana san nur san da bai taba yiwa wata mace ba " yaya kana ji ina ma magana kai shiru, jin shirun yayi yawa nur ta tabashi yaya magana nake, Sai da nur ta tabashi ya dawo daga duniyar tina nin da ya tafi, yi hakuri kanwata wani tina nin na tafi da ban, " ni dai na tafi kar ummana taga na dade, toh kanwata ki dauki chocolate din ko daya ce, ba musu ta dauka tai gaba ba tare da tajira taji me zai ce ba , tana tafiya ya Shiva gidan kaka " kaka akwai maganar da zamuyi da ke dan Allah" toh miji na ina jinka cikin nutsuwa nura ya fara magana , " kaka wata yarinya nake so a garin kuma wallahi da gaske auranta zanyi, kuma bansan abin ya dau lokaci sbda makaranta zan sata, Toh wace yarinya ce mai saa a garin nan da har ta rikita tina nin mijina, ta sashi zuwa garin nan duk sati" murmushi nura yayi ya fara magana " Nur nake so tin lokacin dana sata a idona naji ta shiga raina da farko na zaci tausayi take bani sai naga kuma ashe harda kaunarta, Sosai kaka taji dadin zancen nura, farin ciki ta nuna sosai, domin tana san nur sosai kuma zata so su hada zuria da gidan su malam habu sbda mutuncin su Nura da namiji tilo wajan mahaifansa Alhaji Abdullahi, da kuma mahaifiyarsa hajiya memunatu, yana da yaya mace guda daya Ummul kairi sai kuma kannansa biyu mata Fiddausi sai kanwarsu karama fatima itace wadda shekarunta basu wuce goma ba, asalin Alhaji Abdullahi haifafan panisau ne su Biyar ne wajan babarsu da babansu, Alhaji Abdullahi Dan kasuwa ne ya fara daga dako a kurmi had Allah ya daukakashi, har uban gidanshi ya bashi auran yarsa memuna sbda yadda yake da amana, ba yadda Alhaji Abdullahi baiyi da mahaifansa su dawo hotoro inda yake amma suka ki Malam habu asalin Dan garin panisau ne yana da mata data khadija amma dije ake ce mata, tin da sukai aure basu haihuba, har sun shire rai da haihuwa, Allah ya basu ya mace suka sa mata suna Nur sosai suke santa amma kuma hakan bai hana sun bata tarbiyya ba sai dai bata makarantar boko tana zuwa islamiyya har yanxu da take da shekara tara da haihuwa *cigaban labari* Nura bai ba ranar sai da ta tabbatar masa da cewa insha Allahu Zara shawo kan iyqyan Nur su yadda, sosai nura yaji dadi, Karfe tara na dare nura ya dawo gidansa da sallama ya shiga falon, Aisha sake zaune a kujera tana kallo ta amsa masa sallamarsa ciki ciki, kusa da ita ya zauna tare da janyota jikinsa, ture hannayansa tai ta canxa kujera, kusa da ita ya kara zama, zata tashi ya janyota ya matseta a jikinsa tare da tura bakinsa cikin NATA, saida sukai kusan minti goma a haka sannan ya dagota, sweat heart kiyi hakuri wallahi aiki ne yake min yawa yanxu vai kamata kina fushi Dani ba sbda kefa nake aikin nan, nura bai kyale Aisha va sai da ya tsarata sosai, ranar baccin farin ciki sukai sosai By shamsiyya & Haima ( mmn abul) [4/30, 5:28 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) 36_40 Jikin Nur yayi zafi sosai, kaka ta jika maganin data karbo tabawa nur maganin sai shegen daci, dakyar ta iya hadiyewa. Nura yana fitowa yaga wani dan matashin yaro, "zo dan Allah in tambayeka, cikin ladabi yaron ya karaso kusa da Nura ya gaidasa, Nura ya amsa ya kuma ji dadin hakan, dan Allah ina ne gidansu Nur?ya tambaya yana kallon yaron, yaron yace bayan layine muje in kaika, godiya Nura ya dinga yiwa yaron, tare suka nufi bayan layi, adaidai kofar gidansu Nur yaron yace " ga gidan nan, Hanu Nura yasa a aljihu ya cire kudi ya mikawa yaron yace gashi ko nagode, yaron ya girgiza kai alamar bazai karba ba, dakyar Nura yasa yaron nan ya karbi kudin nan, yace dan Allah ka shiga kacewa kaka Nura ne yazo. Da sallama yaron ya shiga gidansu Nur bayan sun gaisa da ummanta, yace an aiko sane gun kaka, kaka dake daki tace zo gani nan, yace wai Nura yaxo, tace to kace ina zuwa yaron ya fita. Nura yana tsaye sai ga mahaifin Nur ya dawo, ganin bakuwar fuska yasa shi yayi turus, cikin ladabi Nura ya gaida abban Nur sannan, yace lfy dai malam dai dai lokacin kaka ta fito, a'a sannu da dawowa malam, a'a kece agidan namu h nazo duba jikin Nur ne, toh, wannan Nura sunansa jikana ne, abban Nur ya fadada murmushinsa yace a"a bismilla shigo. Tare suka shiga gidan, tabarma umman Nur t shimfida mai, ya xauna ya gaida iyayen Nur cikin girmamawa sannan kaka ta shiga ta taso Nur wacce jikin yanxu da dan dama dama, tana ganin Yayan nata ta sake mai murmushi, wanda hakan shi kadai yasan abinda yaji. Kusa dashi ta zauna, tace ina wuni yayana, lfy lau kanwata ya jikin ki?, jiki da sauki yayana ina Aunty Aisha, tana lfy tace na gaida kanwata, ina amsawa, yaya ina alawa ta, yace tana nan dayawa ma nakawo miki, yanxu nazo ne in kaiki asibiti, iyayen Nur kuwa ttsayawa sukayi suna kallon ikon Allah, kaka kuwa hakan ya mata dadi, Abbab Nur yace dama Nur kin san shi ne?, kai ta daga alamar eh, shine yaban kudi ranar har umma ta dakeni, kuma shiyake sayan gyada sannan yake kawomun alewar birni, sosai ta burge Nura ya sunkuyar dakai, abba ya shiga godiya, kaka tace ba komai malam ai wannan ba komai bane. Da kaka da Nurane suka kai Nur asibiti, nan aka mata allurai aka bata magunguna, ya shiga da ita shoprite ya mata sayayya sosai harda kayan sawa sannan sukaje parks tadanyi wasa kadan kasancewar jikin da dan sauki. Sai magriba suka koma panisau, sosai iyayen Nur sun yaba da hankalin Nura kuma sun samai albark, Nura bai bar gidansu Nur ba sai kusan karfe goma na dare, haka dayazo da safe sai azahar ya tafi, yanxu kusan kullum gidan yake wuni, har sun saba da umma. Muje zuwa anjima Naky yar mutan jos&ta dabo By shamsiya salis & Haima(mmn Abul) [4/30, 5:28 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) 46-50 Fuskar nan ta ta a daure ta fito kamar wadda bata taba dariya ba, kusa da umma ta zauna, " umma gani ta fda tana turo baki, ni nace ina kiranki, kuma bakiga yayanki ba ne baki gaidashi ba, " ina wuni" nur ta fda tana murguda baki, " lpya lau" nura ya fda fuskarshi dauke da murmushi, Umma ta mike ta shiga daki, kusa da ita nura ya dawo, nur me ya faru kike fushi dani, idan laifi nayi kiyi hakuri, " au bakasan ma kayi laifin ba bayan ka gani a fada har Zan taho shine ka juya ka canxa hanya, sai a lokacin nura ya gane nur ta ganshi, rausayar da kansa yayi, kiyi hakuri kanwata, kinga da auntyn ki muke tare kuma tana da fda sosai in taga ina miki magana zata fara miki masifa, ni kuma ban san bacin ranki, turo baki nur tayi ba tare da tace komai ba, Baki hakura ba, ba dole na hakura ba, da kyar nur ta sakko suka fara hira sosai, ya dade a gidan sannan sukai sallama ya tafi, Kullum sai nura ya zo gaidasu su danyi hira ba sosai ba sannan ya taxi sbda gudun kar Aisha ta masa korafi Yau ta kama lahadi kuma yaune zasu koma gida Aisha ta azzazaleshi su tafi ita ta gaji ba yadda ya iya dole ya tafi ba dan ransa ya so ba ko sallama baima nur ba ya tafi, tinda nur ya tafi bai kara waiwaiyar panisau ba sbda ba yaso Aisha ta zargeshi ya fiso sai an tambayar masa auran ta sannan kowa ya sani, Yau satin nura biyu baizo panisau ba tin nur na damuwa har ta shire shi aranta, "Nur wai bazaki zo ki dau tallarba sai ranki ya baci koh, " umma yanxu zanxo so nake na dauraye jikina, au baki wanka ba, " umma ana wannan sanyi na yamma zanyi wanka, sbda kwaliyar jumaar ma da zanyi ne kawai yasa zan wanke jiki na, cikin bacin rai umma ta fito daman ta dora tukunyar sanwa, kwashe ruwan tayi sanan ta sirka, nur na kuka umma ta janyo ta yi mata wanka, sosai nur ta shiga rera kuka kamar wadda ake mata azaba, sanda aka gama mata wanka ta shige daki rai a bace, Jin kukan nur ya sashi saurin karasowa cikin gidan, cikin girmamawa ya gaidata ta amsa, " umma me ya sami nur nake jiyo kukan tin a waje" bari kawai nura yarinya sai shegiyar kazanta kullum a na nuna mata bata ganewa, Allah sa umma baki dakar min kanwa ba, a'a ban dake taba wanka kawai na mata shine take ta rero kukan nan, Bari na shiryata kar tamin ba dai dai ba toh umma bari naje na dawo, Ya fda yana mikewa, sosai umma ta gyara yarta ta tamata kwaliya, sannan ta dora mata talla tai waje Bayan sallar isha'i nura da kaka suka zo gidan su nur sun kwa ci saa Abba na nan tabarma umma ta shimfida musu suka zauna Daman malam habu jika nane yaga nur yace yana so shine yake so a tambayar masa izini idan ba wanda ya rigashi, yana santa kuma baya so abu yay tsayi sbda yana san sata makatanta, da kyar Abba da umma suka yarda sai da nura yay musu kuka sosai ba karamin tausayi ya basu ba hakan yasa suka yarda akan ya turo mahaifinsa ai zancen auran, washe gari tin safe ya tafi gida wannan karan ko haduwa basuyi ba " mlm kaga *hadin Allah* koh jibi yadda yaron nan yake san nur fatan mu dai Allah yasa tayi alfahari da auran da za a mata Daga Shamsiyya salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:29 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.cocom 51-55 " da daddare nura yaje ya sami mahaifinsa a daki, cikin girmama ya gaidashi, bayan ya gaida shi, sai yace ahm baba daman sai yafara Sosa k'eya, daman me mahaifin yace, "um daman baba wata yarinya ce nagani danaje gidan kaka shine... Sai mahaifin nasa yayi murmushi yace, nura daman na dade ina jiran wannan ranar sai gashi allah yakawo ta, Allah yasa yar gidan mutunci ka samo, akwai wani abokina ma da naso ka auri yarsa amma tinda ka samo da kanka ba matsala fatana dai Allah yasa ka iya adalci tsakanin matan naka, Cikin jin dadi yace insha Allahu dady zan iya Allah yasa dady ya fda yana fadada dariyarsa " yanxu ya kukayi da iyayen yarinyar, dady ya fda yana kallon Dan nasa, dady munje ni da kaka neman ixini mahaifin nata yace na turo manya na, kuma dady ban san abin da tsayi sbda yarinya ce ina so ta fara makaranta sbda bata yi, " kar ka damu nura insha Allahu zuwa ranar lahadi tinda bani da aiki sai naje, idan naje zan nemi amini na a garin muje ya rakani neman auran nata, " toh dady na gode Allah ya kara girma, nura ya fda yana ficewa daga dakin " nura meke damunka ne naganka fuskarka cikin farin ciki kamar anma bushara da aljannah, wata mata datijuwa ta fda wadda ga dukkan alamu mahaifiyarsa ce " mumy bbu komai kawai dai aure nakesan karawa ne, " kai Alhamdulilah amma nura kayi tinani mai kyau, ai gwanda ka kara auran yau shekarar ku kusan biyar da Aisha ko watan bata bata tabayi ba bare musa ran jika, " mumy ni ba sbda haka zan kara aure ba kawai dan dai ina san yarinyar ne, kuma na fdawa dady yace lahadi zaije neman auren ta " kai amma naji dady, ai bnyi tinani dady zai yarda ba haka, a ina ka samo mana yarinyar yar gidan wace, mumy ta fda cikin jin dadi " mumy ba yar kowa bace hasalima yar kauye ce kuma karamace sanda naje panisau na ganta da fari na zaci tausayi take bani sai daga baya na gane ashe santa nake kuma..... Maganar da mahaifiyarsa ta fara ne yasa shi saurin dago kansa, Wallahi Allah nura baka isa ba dan wulakanci duk matan garin nan karasa wadda zaka so sai wata yar kauye jahila kaskantacjya, wadda da ita da kare basu da maraba a wajena, " haba mumy dan Allah mutum ce fah bai kamata kina mata haka ba, kar ki manta itama mutumce kamar kowa haba mumy, nura ya fda cikin Bacon rai, " inalilahi wainailaihir rajiuna na shiga uku ni Hindatu, nura tin kafin kayi auran har ka fara min rashin kunya😭 mumy ta karashe maganar cikin kuka, Gaba daya jikin nura yay sanyi, ruko hanunta yay ya zaunar da ita a kujera, " haba mumy dan Allah ya kike so nayi so kike azabar Allah ta hauni, yaza ki dinga zubda hawaye sbda ni, Dan Allah ki duba girman Allah ki daina kuka" " nura tashi ka tafi gida dare yayi" dady ya fda ransa a bace, " dady mumy fa fushi takeyi dani, nura ya fda kamar zai yi kuka, " nace ka tashi ka tafi kafin ranka ya baci koh' Ba yadda nura ya iya dole ya tashi ya tafi " wallahi wallahi wallahi kinji na rantse sau uku ko hindatu mudum kika ziga yaron nan ya fasa auranta wallahi kema sai na sakeki, kuma ko nura baiyi tina nin auro yar asalinsa ba, ni zan aura masa" dady ya fda ransa a bace, mumy zatai magana ya daga mata hannu, bnsan jayayya, ya fda yana shigewa ciki, ba yadda ta iya dole ta hakura amma a ranta ita kadai tasan muguntar da ta shiryawa yarinyar Kamar yadda dady yayi alkawari haka kuwa ya cika, tin safe nura da dady suka kama hanyar panisau karfe tara suka isa garin panisau, Da sallama suka shiga gidan kaka, suka kwa ci saa kaka na tsakar gida, cikin girmama suka gaidata bayan tayi musu shimfida " baba gidan malam habu zani ko yana nan sai ya rakani nemowa nura auran yarinyar da ya gani, cikin mamaki kaka ta kallesa wane malam habu din bayan wajansa zaka neman auran , zaro ido dady yayi, 😳 baba kina nufin aminina malam habu yarsa nura yake so, eh, "Alhamdulilah amma naji dadi sosai nura dama ita ce yarinyar da nake fda ma zan aura maka, sosai yaji dadin lalai wannan shi ake kira *hadin Allah* Kuyi hakuri naso page din yafi haka amma kasancewar ina busy shiyasa banyi da yawa ba amma insha Allahu za muyi muku wanda yafi wannan insha Allah Daga taskar Yan mutan *dabo da jos* [4/30, 5:29 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 56_60 Malam habu na zaune tsakar gida kan tabarma Nura yayi sallam, Nur dake wanke wanke ta amsa sallamar itama, guri yasamu kusa da baban ya zauna cike da girmamawa ya gaida abban Nur, Nura yace"abba dama da daddyna muke tafe yana waje ma, Malam habu yace a'a jeka ce su shigo mana. Mikewa Nura yayi daidai lokacin umma ta fito ya gaisheta sannan yayi waje, tare suka shigo da daddynsa gefe dasu ya zauna, cikin mamaki Malam habu ya kasa magana, daddyn Nura shiya katse mai mamakinsa yace"kaga hadin Allah ko?, daga kai malam habu yayi alamar eh sai lokacin ya bude baki" badai ince Nura shine yaronka ba"kwarai shine kuma dama ya mun bayanin komai game da Nur shine yasa ma nacewa kaka xanxo gurinka muje gun uban yarinya, toh shine kaka take shaidamun ai yarka ce ma, naji dadin hakan sosai saboda dama niyyata na umarcesa akan yaxo ya nemi yarka, dayaxo mun da bayanin yasamu wata sai ban matsa ba ashe Allah ya riga ya hadasu wannan shine HADIN ALLAH. sun sha hira sosai ta yaushe gamo sannan daga karshe suka tsaida lokacin bikin nan da wata biyu, Daddyn Nura ya dubi aminin nasa yace "bana bukatar komai daga gareka domin Nur ya'tace, sosai malam habu yaji dadi haka ma umma tayi godiya sosai. Nura ne xaune kan dakalin kofar gidansu Nur yana jujjuya mukulin motarsa, Nur ta isa gurin fuskarnan tasha adon su na yan kauye wai ita adole tayi ado gyalen tasha damara dashi, da sallama ta isa gurinsa, ya dago yana mata murmushi ya amsa sallamar, guri tasamu ta zauna, ta dubeshi sosai sama zuwa kasa tace" yayana kayi kyau sosai, da mai hoto ya fito da munje an dauke ka, yayi murmushi sosai har kumatunsa ya loba yace "kanwata nagode kema ai kinyi kyau har kin fini, ya ciro wayarsa yace" zo ki gani ta matso ya nuna mata yadda zatayi ta daukeshi a hoto, hakan kuwa akayi ta daukesa sannan itama ya dauketa. Nura bai bar gidan ba sai da yaci turon umma na dare, washegari suka koma kano, Da sallama Nura ya shiga gidansa amma Aisha na zaune a falon bata ko san ya nayi ba bare ta amsa mai, ransa yayi masifar baci ya wuce dakinsa, wanka ya fada bayan ya fitone ya shirya cikin kananan kaya ya sake fitowa tana zaune inda ya barta, yaxo zai fita nan ne tasha gabansa, sannan taci kwalarsa wlh baka isa ba munafiki, duk abinda kake shiryawa ina sane toh wlh sai dai kasan insa xata xauna don wlh baxan xauna da kishiya ba, kai bari ma kaji baka isa ayi auren nan ba, cikin zafin rai da irin kalaman Aisha bai san lokacin daya dauketa da wani wawan mari ba, sai da taga taurari cikin hanxari ta sake shi ya juya ya fice abinsa. Durkushewa tayi agurin tana ta rusgar kuka, shikuwa tunda ya fice sai karfe sha daya ya dawo lokacin har ta gaji da kukan tayi bacci, afalo ya sameta tana bacci akan kafet kallon ya kashe ya dauketa ya kaita daki, ya kashe mata wuta ya rufe dakin ya nufi nasa. Ku kasance damu anjima zamu cigaba amma sai ankawo wuta. By Haima(mmn Abul? & Shamsiya salis [4/30, 5:29 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 61_65 Washegari, Nura na fitowa daga dakin, dakin Aisha ya nufa ganin kofar a kulle yasa yayi turus ya murda amma a kulle, hakan ya tabbatar mai bata gidan, kitchen ya nufa ya hada tea yazo yasha, ya kishigide akan doguwar kujera. Misalin karfe tara na safe wayarsa dake gefensa tayi ringing jawo wayar yayi ganin sunan hajiyar Aisha yasa yayi saurin daga wayar tare da karawa a kunnen sa, ko sallama batai ba ta fara masifa " wallahi nura ba isa ba dan wulakanci karasa wadda zakaima kishiya sai yar tawa kuma duk matan garin nan ba ka auri kowa ba sai ka tafi kauye ka dakko mata bagidajiya, jahila kaskantaciya, tin da mumyn Aisha ta fara zagin nur ya rintse idonsa dan har cikin ransa yake jin zafin abin ba yadda zaiyi da mumyn ne kawai, " nura kanaji ina magana kamin shiru wato ka maidani yar iska ko, maganar da ta katsemasa tunanin da yake, " mumy wlh ba haka bane kawai dai ina san yarinyar ne kuma bata da aibu" ka ga dalla malam ba ca nai ka min wannan shashancin ba sai dai ka zaba ko Aisha ko yar kauyan da zaka dakko, bata jira cewar sa ba ta kashe wayarta Dafe kasa yayi yana ta karanto adduo'i ya rasa yadda zaiyi mutane su fahimci san da yake ma yarinyar, yasan yana san Aisha amma san da yake ma nur bai taba jin yanayi ma Aisha shi ba da wannan tinanin bacci mai nauyi ya dauke sa *Bayan kwana uku* Mumy dan Allah kiyi hakuri ki bani matata wallahi ina santa, kuma ina san nur gaba dayan su bbu wadda zan iya rabuwa da ita, ki min addua Allah ya bani ikon rike su da amana, nura dake durkushe gaban mumyn Aisha yake fda cikin girmamawa " wai nura sau nawa zan fda maka kar ka kara zuwa gidan nan da nufin tafiya da Aisha har sai ka janye batun auran wannan dabbar da kake ikirarun aura" rintse idon sa nura yayi jin zagin da mumyn Aisha ke wa nura ya sashi mikewa a fusace ya kalli mumy " indai yarki ce ki riketa ba zan kara zuwa neman dawo da ita ba kuma duk duniyar nan bbu mahalukin da ya isa ya hanani auran nur tin da mahaifina ya yarje min " iyeeee nura ni zaka zaga sbda waccan jakar yarinyar wlh ba ka isa ka aure ta ba" ganin yana batawa kansa lokaci yay ficewar sa Yana fita ya ja motarsa yay panisau cikin mintinan da ba su wuce arba'in nura yaje garin Gidan kaka ya fara zuwa bayan sun gaisa ya tafi gidan su nur akan dakalin gidan su ya hangota suna ta zuba tar carafke ita da kawayanta, sanda ta ganshi ta dauke kanta kamar bata gansa ba ta cigaba da yin yar carafeken, ganin bata taso ya sa yay tinanin wasa ya dauke mata hankali bata lura dashi ba cikin nutsuwa ya fito daga motar ya nufi inda suke " sannun ku wasa ake yi, nura ya fda fuskarsa dauke da murmushi sanda ya karasa kusa dasu, " eh wasa muke yaran suka fda suma suna dariya, nur ba magana, nura ya fda yana maida kallonsa gare ta, turo baki tayi ta ki ko kallon inda yake ganin bata da niyyar kulasa ya sashi dole ya kyaleta ya nufi cikin gidan, Da sallama ya Shiga lokacin Umma na tsakar gida tana bare gyada zatayi dambu, fuskarta dauke da murmushi ta amsa masa, kusa da ita ya zauna a gefen tabarma bacin ya gaidata cikin girmamawa Hannu yasa ya dibi gyadar ya fara barewa " umma daman karatu nake san fara koyawa nur kafin ayi auran mu koma can, kinga in ta fara makarantar karatun zai zo mata da sauki, " ba komai nura kullum adduata Allah ya biyaka domin mu kan bamu da abinda zamu biyaka, hayaniyar da suka jiyo a waje ne ana kuka yasa nura kin magana, umma kamar fda yaran nan suke kan tai magana wata yarinya ta shigo da gudu " umma nur ta fasawa ladidi kanta da dutse, kafin yarinyar ta karasa nura yay saurin fita, ganin yadda jini ke fita akan yarinyar ya sashi saurin sata a mota ya nufi karamin asibitin dake cikin ungwago, cikin sauri suka karbeta suka mata taimakon gagawa sannan suka hada masa magun guna suka bashi ya kamo hanyar panisau " ladidi me ya hada ku da nur,nura ya fda yana kallon ladidi, wai dan ina cinyeta a yar charafke yau, kuma kullum in anayi itace ke cinyewa yau ne kawai na cinyeta fa, " kiyi hakuri kinji ladidi zan zane ta, toh ladidi ta ce Har gida ya kaita aka masa iso ya shiga ciki ya basu hakuri tare da mika musu kudi Umma ba karamin duka tayima nur ba wanda yasata ficewa daga gidan ita a dole tayi fishi, bayan nura ya dawo yaje ya dakko umma da kaka suka je suka duba jikkn ladidi Muna barar addua son bashi da lpya Allah ya baka lpya my abul kair Daga taskar Auntyn abul & Mmn abul [4/30, 5:29 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 66- 70 Nur bata dawo gida ba sai bayan sallar isha'i har lokacin nura na gidan umma, sanda ta shigo gidan umma ta zubawa nura abinci ta shiga daki dan tayi sallah Cikin sanda take tafiya har ta shigo tsakiyar gidan kwata kwata bata ma lura da nura dake tsakar gida ba, " gwanda ma kiyi tafiyar ki yadda kowa zai san kin shigo kuma sandarki bazai hana a dake ki ba ko" umma ta fda tana karasowa wajan ta, " umma dan girman Allah kiyi hakuri wallahi vazan kara ba ki yqfe mun, Janyota umma tai kin iya munafurci mana da siffar salahai in kinyi laifi amma wallahi sai na dake ki, umma ta fda lkcn da ta fara dukan nur, " umma kiyi hakuri tin da tace bazata kara ba, nura ya fda yana riko hannun nur sosai ta makale a jikin sa sbda kar umma ta daketa, da kyar nura ya lalashi umma ta kyale nur sannan ya tafi Kwanci tashi ba wuya wajan Allah bikin nur da nura ya rage saura sati biyu, nur an fara iya turanci, dan sosai nura yake mamakin yadda nur take da saurin daukar duk abinda akayi mata Aisha kuwa tin tana sa ran zuwan nura har ta fara cire ransa, tin bata damuwa har ta fara damuwa duk ta rame sbda ko waya baya yi mata, suna zaune a falo ita da mumy ta kalli mumyn ta tace, mumy kinga nura sbda baya sona yaki dawo wa kuma gashi har ya kusa auro yarinyar da na tsana, " kar ki damu Aisha zanje na sami mumyn nashi muyi magana, toh mumy na Da daddare dady da nura suna daki suna tsara yadda za a yi bikin, " yauwa nura ina Aisha ne ka siya mata nata kayan nata, " dady ai ta dade bata gida ta kusa sati shida da komawa gida sosai dady yayi masa fda kuma yace yaje ya dawo da ita a yau, ba dan ya so ba dole yana barin gidan ya wuce gidan mumyn Aisha Da sallama ya shigo falon sosai Aisha taji dadin ganin sa amma ta dake, mumy ce ta amsa masa sallamar ciki ciki, " mumy ina wuni, lpya lau ta fda a takaice, "ai na zaci nura baza ka dawo ba, " ayi hakuri mumy yanxuma zuwa nayi mu tafi, bari nai sai kun huce tukunna, sai da suka gama ja mashi rai sannan Aisha ta shirya suka tafi, da kansa ya bude mata gaban motar ta shiga ya ja suka tafi " sweat heart ya kamta ki ajiye fishin nan nasan na miki laifi amma ki yafe mun kinji, nura ya fda yana dora hannunsa akan hannunta, dauke hannunta tayi tana turo baki, haba sweat heart kila ma ko missing dina bakiyi ba, ganin bata da niyyar tanka masa yasa a dole yay shiru har suka karasa gida, dakinta ta wuce tai wanka, shima haka, nura dai sai da ya tabbatar matarsa ta hakura a ranar dan saida suka lula duniyar masoya a ranar Sosai nura yake gyaran gidan dady ne yayima nur kayan daki na gani na fda komai sai da yayi mata guda biyu, ganin yadda bangaran nur ya tsaru, yasa nura gyarawa Aisha bangaranta ko zata ji dadi, dan sosai yake san Aishar tasa dan ko a mafarki baiyi tinanin yi mata kishiya ba, Ana saura sati daya biki yan uwan dady suka kawo lefe gidan su nur akwati goma sha biyu ko wanne cike yake da kaya, sosai muta nan garin ke zuwa ganin kayan nur kowa da abinda yqke fada, nur kuwa sai murna take ganin lodin kayan da aka kawo wai kuma duk nata ne a haka aka shiga hidin dumun biki Sosai bikin yayi dadi yadda ake tsara bikin kauye haka akayi shi anyi kamu da sauran aladun gagarin an raba kaya na gani na fda duk Wanda ke garin panisau ya san da bikin nur haka ma yan gefen garin su *Jaba* *Rimaye* da dai sauran gefen garin Allah ya baka lpya my cwt abul Daga taskar yan mutan Dabo da jos [4/30, 5:29 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 71-75 Yau takama jumaa yaune dubban jamaa suka shaida daurin auran Nura da amaryarsa Nur Alan sadaki dubu Dari a babban masalacin sarki na fada aka daura auren, wayyo zo kuga yadda mutane suka dinga mamakin sadakin nur, kasancewar garin akanta ne aka fara sadaki dubu dari a can na hango cikin wata dakakiyar shada sai faman sheki takeyi, hakoransa kwa duk ya washe su kana ganinsa kasan yana cikin farin ciki wanda bazai misaltu ba, Amarya kuwa umma ce ta mata wanka da kanta sannan ta shafa mata mai da hoda jambaki kadan umma ta shafa mata sannan ta dakko mata atamfa sharaton green abinka da farar fata nan da nan fuskarta ta fara haskawa, tsayawa fadar yadda nur tayi kyau, bayan an daura aure angwaye suka zo gaida iyayen amarya, sosai nura yay mamakin yadda nur tayi kyau, ansha hotuna sannan angwaye suka tafi Washe gari ta kama asabar ranar akayi yini anci an sha Alhamdulilah, bikin nur sosai ya kafa tarihi a garin panisau, wasu na murna wasu kuma na bakin ciki kasan cewar ba yayansu aka aura ba, Karfe biyar motoci suka fara layi a unguwar su nur sai da aka kawo motoci guda goma sha biyu ko wacce mota sadadiyar gaske ce, Anya hasantu dije ba sai da yarsu sukayi ba jibi yadda ake ta faman bidiri da kudi kamar baa san yau ba, haba fatsima ai wannan hassada ce da dai ba a san asalin sa bane sai ace an saida ta amma ba wanda bai san mahaifin yaron nan ba hasali ma kakar sa da ta haifj mahaifinshi har yanzu tana cikin garin nan ki daina wa mutum bakin ciki bbu inda zai kaiki, insha Allah hasantj na daina kuma na gode da waazinki gare ni, Bayan sallar mangariba Abba ya kira nur ya mata fda akan ta nutsu ta daina kazanta dan a shekarunta bazai mata fdan aure ba kuma yasan nura ma bazai bari wani abu ya shiga tsakaninsu sai tayi ilimi, umma na kuka nur na kuka aka sata a mota suka kama hanyar hotoro, gaba daya sauran amaran gidan amarya aka wuce dasu a tarauni, motar amarya da iyayenta ke ciki a ka wuce hotoro dan gaida iyayen ango Yan panisau ba karamin rudewa sukai ba sanda suka ga irin saruwar gidan ni kaina da nake gefe saida biro na ya fdi dan bn taba tsayawa nayiwa gidan kallon kullura irin na yauba,sister haima ce ta dunguran kai bayan ta mikon bison maza bisu ki gano mana falon, Da Sauri nai bi bayansu Masha Allah abinda duk mutanan dakin ke fda kenan, nima abinda na fara fada kenan sbda tsayawa fadar yadda falon ya hadu bata lokaci ne Sanda aka kai nur gaida mumy fuskarta ba yabo ba fallasa ta karbe su jiki bbu kwari suka dau yarsu suka nufi gidanta Karfe tara gida ya watse aka tafi mai dash panisau yan kai amarya na watsewa Aisha da kawayanta suka nufi part din nur Cikin tswa Aysher ta kalli nur da take zaune tana ta faman wasa da remote a gaban tv ta taba wancan ta taba wancan " ke ina wadda kuka kawo gidan nan take yayar ki, nur ta kalleta cikin rashin fahimta, Aysher ta zaro mata ido nace miki ina Nur din da kuka kawo, nur ta mata bnza kamar ba da ita take ba dan uwarki ba magana nake miki ba, Aysher ta fda cikin tsawa, rai a bace nur ta mike ba dai uwata ba wallahi sai dai uwarki kuma nice nur din da kike nemar uwar me zan miki da kike nemana, nur ta fda tana rike da kugu, zaro ido Aisha tayi kadai nura wannan mara kunyar mara tarbiyar ya auro aiko ya kawowa kansh jaraba, Aisha taja hannun kawayenta suka yafi, nur kuwa komawa tai ta cigaba da wasanta, Aisha tin da ta shiga daki take zagaye zagayen dan kawayenta ma kin shigowa sukai suka tafi wai ta basu kunya yarinya yar cikinta na mata rashin kunya amma taki tabuka komai, Nura ne yay sallama tare da shigowa dakin cikin bacin rai Aisha ta juyo ta kalleshi,wallahi nura kaji kunya ka rasa wadda zaka aura sai wadda a haihuwar kaji kayi jika da ita, haba sweat heart bai kamata kina fdan haka ba nifa mijin ki ne yanxu dai ki kintsa zan kawo ta ku sasanta Allah ya min tsari tsatsan tawa da yar ciki na kai dai da ka zubar da girmanka da kimarka sai kaje wajenta, mtswww Aisha ta gallama nura harara ta shige dakinta tare da saka key ta rufe girgiza kansa kawai nura yayi ya nufi part din nur By Shamsiyyah salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:29 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 76_80 Murda kofar dakin yayi ya shiga side din nur, a zaune ya sameta tana wasa yadda ya barta karasawa yayi ya durkusa gaban Nur ya riko hannunta, ta dago tana harararsa ya yi dariya domin dariyar ta bashi, kanwata lfy kike hararata?, ya tambaya ta turo baki ya mike tsaye itama ta tashi ya na rike da hanunta suka shiga bedroom dinta, wanka yaje yayi sannan ya fito ya umarceta da taje tayi wankan itama, amma fir taki sanin halinta ne tana iya taramai jama'a yasa ya rabu da ita ya hau gado ya kwanta, ta xo ta tsaya mai akai kerere tace yayana ni a ina zan kwanta?, ya yi kamar baiji ta ba, ta sake tambayarsa nan ne yaga zata dameshi yace ki hau gadon mana, tace tab ya zaayi mu kwana gado daya aradu baxai yiwu ba ta rike kugu kamar wacce zata yi dambe dashi, ya ce toh shikenan tunda bazaki hau ba ki kyaleni kinga bacci nakeji, ya juya mata baya ya kashe wutar dakin, ihu tasa tayiwo gadon da gudu, yayana dan Allah ka kunna wutar dakin, yayi banxa da ita ta saka mai kuka tana kiran ummanta. Ganin taki saurarawa da kukan yasa ya kunna wutar dakin, ya hango ta can kuryar gado ta rakube tana ta kuka, ya matsa kusa da ita yana bata hakuri, riko hanunta yayi aikuwa kamar jira take sai ta bige hannun ta runkura zata bar gadon yayi saurin riko ta. Ina zakije tace bansani ba cike da tsiwa, ta bashi dariya amma ya gimtse dariyarsa, ya fara lallashi dakyar yasamu ta hakura amma tace sai dai yabar mata dakin ta, mikewa yayi ya nufi kofa tana zaune tsakiyar dagon yace sai da safe ya bude kofa zai fita kamar an korota ta taho da gudu tace yayana wlh tsoro nakeji, yace ba kince na bar miki dakin ki ba, tace toh dawa xan kwana wlb inajin tsoro, juyawa yayi ya fara tafiya, ai maza ta biyo sa, dakinsa ya nufa tana biye dashi. Kan gadon taje ta rakube, nan dai har bacci barawo ya sace ta, ya lullube ta da bargo ya kwanta agefenta. Washegari shiya hada musu breakfast don yasan Aisha ba girki take ba bare tana jin haushin aurensa ya gama hadawa kenan driver gidan mumny ya kawo musu kayan kari, sai da ya tabbata ya hada komai sannan yaje ya tashi Nur dake bacci tun bayan tayi salla yasa tayi wanka dakyar hakan ma don yace xai mata ne, kaya ya bata riga da wando, rigar yello da bakin wando sai hula itama yello, ya tayata sukayi kwalliya tare sannan suka fito, har kan dinnig ya ajiyeta sannan ya nufi sashen Aisha. Tana zaune ta zuba uban tagumi ya zare hanun, cikin bacin rai tace lfy malam?"lfyr kenan ya fada ataikaice sannan yace swt hrt bako gaisuwa ne?ta galla mai harara ta juya mai baya, yayi lallashi amma taki kulasa haka ya mike ya tafi. Zama yayi yana zubawa Nur abinci sai ta kallesa tace"yayana naga kamar kana fushi dani don Allah kayi hakuri ka yafe mun, dagowa yayi ya kalleta ta sake mai murmushi ya mayar mata yace"ba abinda kika mun kanwata auntynku ce ta bata mun rai, nan take sai Nur ta hade fuska "yace lfy kanwata me kuma ta faru tace wlh wannan auntyn akwaita da masifa da jaraba ai na dauka kai babbane baza ta maka ba sai yara, tab halinta bayi da kyau, hanu yasa ya rufewa Nur baki yace tanada kirki fa Nur kuma tana sinki jiyan ma ranta abace yake, Nur ta jinjina kai aranta tace shegiya taji dashi azarihi kuma cewa tayi Allah yasa, " amin kanwata. Amun afuwa Abul ba lfy amma xamu cigaba anjima. By Shamsiya salis & Haima(mmn Abul) [4/30, 5:29 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 81-85 " kanwata ranar monday zaki fara zuwa makaranta hpe dai zaki maida hankali kiyi karatu, insha Allahu zanyi yayana, " yauwa my yar kanwa, dariya sukayi gaba daya, ganin mutum akan su yasa su tsagaita dariyar, Wallahi nura kaji kunya anyi asara ka zauna kana shashanci kai da yar cikin ka wai kai baka yadda soyayya kake ba, mtswww Aisha ta karashe maganar tana tsaki, "Haba swt hrt bai kamata kina min irin haka ba, wannan in kikai hakuri zaku zauna lpya yar kanwar tawa bata da matsala ai ya fda yana ruko hannunta, " mtswww dalla malam ni ka sakeni wallahi anyi asara ta fda tana fuzge hanunta tayi waje " Allah ya kyauta abinda nur ta fda kenan tai waje, *Bayan kwana3* Nur ce kwance tana sharar baccin ta hankali kwance, nura na gefenta yana ta tashinta amma taki tashi ganin taki tashi kuma bata da niyyar tashi yasa nura daukarta cak ya dire ta a bandaki, kuka ta saki tana bubuga kafa ni wallahi kadaina tashi na in ina bacci, Allah sai na fdawa umma, duk abinda take idonta a rufe yake taki budewa, sosai ta burgeshi, ruwa ya diba ya watsa mata a fuska, ihu ta Saki tare da kankamesa, " sorry my kanwa , kuka ta dinga masa da kyar ya lalabata yayi mata wanka sannan suka fito, cikin wata doguwar riga milk ya shirya ta sosai ta yi kyau duk da ba abinda ta shafa a fuskarta, bnda mai da farar hoda sannan suka fito sukai break fast har lokacin Nur bata rai take batayi dariyaba, a haka suka nufi makaranta, " kanwata har yanxu fishi akeyi dani ne dan Allah ki danyi min dariya mana kinga makaranta fa zan kaiki ko ba kyaso ki iya turanci da karatu ki zama babar likita,ya fda yana ruko hannunta, Fuskarta dauke da murmushi ta juyo ta kalleshi, yaya da gaske zan iya turanci, "sosai ma kanwata ni dai fatana ki dage da karatu kinji" toh yaya zanyi, a haka suka karasa makaranta bayan an gwada ta aka sata a pri 1 nura ya tafi ya barta a makaranta, Sanda auntyn su ta shigo tqji yaran suna turanci sosai suka burgeta, ranar dai Nur anyi abin arziki dan har aka tashi bbu wanda ta tsokana, Karfe biyu dai dai nura ya zo daukarta, kasancewar bai tashi daga office ba ya sa ya wuce da ita office dinsa "Yayana gaskiya makarantar da dadi sosai, kaji yadda suke turanci, nur ta fda fuskarta dauke da murmushi, toh kema ki dage ki iya turanci kinji kanwata, toh yayana amma zaka koyan koh, daga mata kai yayi sanda ya isa office dinsa kamal abokinsa ya tadda a bakin kofa, "Nura ina kaje ne tin dazu nazo fa" " Ayya am sorry naje dakko kanwata ne yaushe kazo kano din, wlh jiya nazo shine nace bari nazo mu gaisa, Wow gaskiya kanwar nan taka tayi kyau sosai ina kamu" harara nura ya wulla masa, kaga bansan iskanci kamal, wlh da gaske nake indai zaka bani ita, ya fda yana kallon nur, baby ya sunanki, Nur sunana, ta fda tana washe bakinta, " kina da kyau, kaima kana da kyau ina m....... Tsawar da nura ya daka mata ne yasata kin karasawa, sosai nur take hargitsewa duk sanda aka mata tsawa, hannun kamal yaja suka bar wajan, " kaga malam ban san iskanci malam mata tace fah, itace amaryar danj" Ayya yi hakuri nura wallahi ban sani ba amma fa kayi saa, dariya nura yayi ya koma office dinsa inda ya bar Nur nan ya tadda Hannunta ya rike suka Shiga office, kan kujera ya zaunar da ita ya cigaba da aikin sa, " yaya kayi hakuri Dan Allah kaji" harara ya wulla mata haka nace kin mun laifi da zaki bn hakuri Ranar sai shida suka koma gida Suna zuwa gida part din nur suka nufa yayi mata wanka shima yayi wanka sannan ya nufi part din Aisha By shamsiyya & Haima (mmn abul) [4/30, 5:30 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.comcom 86-90 Tana zaune akan kujera tana chrtn da alama kuma tana jin dadin chrtn din sallama yayi tare da shigowa dakin, ciki ciki ta amsa masa, kusa da ita ya zauna tare da dora kansa a kafadarta swt hrt ya gida, " gashi muna ciki" nayi missing dinki alot, tin da na fita ko ki kirani kiji yadda naje office koh, cikin bacin rai ya ta kalleshi tace wadda ka fita da ita din bata debe maka kewar ba, sbda tsabar rashin adalci tin da nake da kai ko sau daya ba ka taba zuwa dani office ba shine yau har da daukar yar cikinka kuma dan abin kunya a tambayeka wace kace matarka Allah kaji kunya Nura, murmushi kawai yayi mata yay waje ya tabbata kishi ke damun matar tasa Kwanci tashi ba wuya wajan Allah su Nur an shiga wata daya da aure sosai ta dage da karatunta bata wasa hakan yasa aka maidata pr 2 tinda aka maida ta pri 2 takara dagewa da karatu ba laifi yanxu ta fara iya turanci duk da ba kwarewa tayi ba rashin kunyarta kwa na nan bbu inda taje kazanta ce dai aka rageta kadan kamar kullum tana zaune a daki tana yin assihnment din da aka bata Akayi sallama tare da turo kofar dakin, ba tare da ta dago kai ba ta amsa sallamar " ke dan uwarki kina jin mutane shine zaki musu shiru kamar wata saarki, Fuskarta a hade ta dago tana kallon Aisha tace, " toh aunty me kike so na miki sallama ki kai kuma na amsa ta fda tana murguda baki, " kut lalai yarinyar nan ni kike murgudawa baki, " eh din an murguda ina ruwanki dani kawai dan kinga ina kyale ki koh an fda miki tsoron ki nake ji da zaki dinga zuwa kullum kina zagina, Cikin bacin rai Aisha ta kai mata mari, " Allah ya isa muguwa azzaluma kuma wallahi sai na rama shegiya kawai dai dai lokacin da nura ya turo kofar da zai shigo yaji nur na zagin Aisha ita kuwa Aisha najin alamun nura yasa tayi shiru sbda ta kullamata sharri ita kuwa nur ido ya rufe ta dage sai zagin Aisha take, nur ni kike zagi " eh din an zageki kuma wallahi...... Marin da nura yay ma nur ne ya sata kin karasa maganar, nan ta durkushe tana kuka Nura kuwa hannun Aisha ya ja suka bar dakin, wallahi nura sai na koyawa yarinyar nan hankali jibi yadda kasa ta raina ni tana ta faman zagina, ta zage ki din da kin rike girmanki ai bazata zage ki ba kuma ai ke kikaje inda take, wallahi Aisha kar na kara ganin kinje dakinta kina jina ya fda yana tafiya ba tare da ya jira me zata ce ba yay waje dakin nur ya nufa har lokacin tana durkushe Inda ya barta, jikinsa a sanyaye ya karasa inda take, dagota yqyi ta kwace ni ka sakeni, haba kanwata kiyi hakuri bazan hakura ba din ni ka maida ni inda ka dakko ni jibi yadda fuskata ta kumbura ita ta maran anan nai mata Allah ya isa, sbda na zageta kaima kara mari na jibi fa yadda fuskata tayi, nur ta karashe maganar tana kuka, Sai a lokacin ya lura da inda Aisha ta mareta, duk sai yqji ba dadi, am sorry kanwata bazan karaba kinji, da kyar nur ta hakura sai da yace zai kaita wajan wasan yara sannan ta hakura, Washe gari ya kama asabar tin safe ya shirya nur tsaf cikin wata atamfa riga da skrt sosai nur tayi kyau cikin kayan, yana rike da hanunta har suka isa gaban mota, " iyeeeee nura kana san gamawa da duniya lpya kuwa kasan hukuncin wanda basa a ladalci kuwa tsakanin matansu, me yasa zaka dau matarka daya ka bar daya, mumyn Aisha ta fda tana karasawa wajan su Cikin girmamawa nura ya gaidata, mumy yanxu xamu dawo ai, kuma ai ba rashin adalci bane wannan dan na fita da Ita, sbda itama Aysher ai na fita da ita tana amarya " yayana wace wannan din, kan nura yay magana mumy tayi magana cikin bacin rai " uwarki ce dan ubanki shegiyar yarinya yar karama dake kin iya kisisina ai dole Aisha ta samo mafita kan ki girma munafuka kawai, " wallahi ni ba munafuka bace sai dai in ke....... Kallon da nura yayi mata ne yasa ba shiri tai shiru, Nura yanxu wannan tsinaniyar yarinyar ka auro wadda bata da tarbiyya batasan girman manya ba, Mumy kiyi hakuri in Allah ya yarda zan mata fda, bai jira cewar mumy ba yasa nur a mota suka fice Mumy kuwa masifa ta dingayi da kyar Aisha ta rarasheta tai shiru " kanwata bbu kyau yiwa babba rashin kunya ki daina kinji, " toh yaya bazan karaba amma wacece ita, mumyn Aisha ce, Ashe gadar masifar tayi, abinda nur ta fda a zuciyarta kenan, a fili kuma tace ai bn sani ba bazan karaba a haka suka karasa wajan wasan yara suna hirarsu By shamsiyah & Haima ( mmn abul) [4/30, 5:30 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 91-95 nura da nur sukaje wajan shakatawa da dama daga nan ya kaita shpn basu baro wajan ba sai kusan laasar direct gidan mumynsa ya wuce lokaci na farko da zai kaita gidan mumynsa tin bayan auransu, da sallama suka shiga falon lokacin ba kowa a falon hakan yasa nura yay mata izini da ta zauna a daya daga cikin kujerun falon yaje ya dawo, yana wata kofa ya shiga da zata sadashi da dakin mumy ya bi, tana zaune a daki ta idar da sallar laasar da sallama ya shiga ta amsa masa fuskarta ba yabo ba fallasa, bayan ya gaidata ta amsa yace mumy daban nur na kawo miki ku gaisa, Hararsa tayi, " uban me zan mata da kakawo min ita, kuma kana tinanin wannan karamar yarinyar zanje na samu a falo ba ita zata zo ta sameni ba, mumy kiyi hakuri bari na kurawo ta, bai jira amsarta ba ya fice tana zaune inda ya barta, kusa da ita ya zauna " kanwata kinga mumy na yanxu zaki gaida dan Allah ki nutsu bnda rashin kunya kinji kin ga bna wa umma rashin kunya koh, " Allah yayana na daina rashin kunya kuma ko zaa dakeni bazan rama, " yauwa kanwata ta kaina taso muje, nura ya fda yana rike hanunta, " ga dakib mumyn nan ki shiga ku gaisa ni kuma zan tafi wajan aiki ana jirana da daddare zan xo na dauke ki, toh yaya Allah ya tsare, sosai nura ya ji dadin adduar da ta masa, yay mata murmushi ya tafi Cikin nutsuwa nur ta tura kofar dakin mumy da sallama ta shiga mumy na zaune a gefen gadonta, ta amsa mata sallamar fuskarta ba yabo ba fallasa, Har kasa nur ta tsugunna ta gaida mumy sosai mumy ta yaba da hankalinta domin tin da take da Aisha bata taba gaidata cikin girmamawa ba, Duk tsanar da mumy ta mata a kaso dari yanxu bbu kaso sabain, " nur ya gida lpya lau mumy, mumy yau yaya ya kaini wajan wasan yara sannan mukaje shpn munga mutane sa yawa , Hankali kwance nur ta fara bawd mumy lavarai masu bn dariya tin mumy na sharewa har ta fara darawa a take mumy taji son nur ya shiga zuciyarta dan jinta take kamar yar autar ta saar nur ce " Nur labarin nan ya isheni haka kije kiyi wanka kizo ki ci abinci yanxu auta zata dawo daga makaranta sai ku cigaba da bata labari toh mumy na, Karfe shida auta ta dawo daga makarantar islamiyya, sosai auta da nur suka saba suka zauna suna hirar su Da daddare bayan sallar isha'i mumy nur da auta suna zaune sun cika mumy da hira suna bata labarai sun sata a tsakiya suna ta shewa ko wannen su ya dora kansa akan cinyar mumy Dady da nura ne suka turo kofar tare da sallama sosai nura yaji dadin ganin nur da mumy suna hira, A'A mumy hira ake da yayan naki dady ya fda yana zama a kujera cikin girmamawa nur ta gaida dady ya amsa fuskar sa dauke da murmushi, Murmushi mumy tayi, nura ya kakeyi da surutun nur, dariya yayi mumy kema ta dame ki ke nan, Sun dade suna hira, "Nur Dan Allah ki tashi mu tafi dare fa yayi, ni wallahi anan zan kwana, abinda a gidan naka kullum auntyn nan tai ta zagina, nan kuma mumy ko hararata ba tayi, Ba yarda nura baiyi ba akan nur su tafi amma taki, mumy ce tace a kyaleta ta kwana ba dan ya so ba haka nura ya tafi rai a bace Washe gari nura bai zo gidan mumy ba sai kusan mangariba, lokacin su nur na falo suna hira ita da mumy da sallama ya shigo falon, nur na ganinsa ta tashi ta rungumeshi, Sannu da zuwa yaya yauwa, ya fda fuskarsa a hade, Mumy ina wuni, lpya lau, ina Aisha tana gaidaki nura ya fda yana hararar nur Sanda nura yacewa nur su tafi ba musu ta tashi domin mumy tace kar tayi masa musu Karfe tara na dare suka isa gida lokacin nur tayi bacci a mota a dakin ta ya kwantar da ita ya rufe mata ya nufi dakin Aisha By shamsiyyah salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:30 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 96_100 Nur wai bazaki fito mu tafi bane?"yi hakuri yayana ganinan zuwa daidai lokacin Aisha ta fito tana wani rangwada tana shishshigewa nura, Nur ta fito rataye da jakarta tace mutafi yi hakuri, lokacin Aisha ta sumbaci goshin Nura Nur ta kau da kai a xuciyarta tace yan iska kawai tayi gaba abunta. Bari kiga na tafi kar nayi latti, ya saketa yayi gaba, Aisha ta kwashe da dariyar mugunta shegiyawa wai adole kishi take ai yanxu xaki gane kuranki. Amota nur taki kula nura yayi juyin duniya amma fir taki kulasa, hakan yasa ya nemi guri gefen titi ya tsaya, sai lokacin ta dago kai ta kalleshi shima ita yake kallo tace"yayana lfy?"na tsaya ne in kin gama fushin sai mu tafi, murmushi nur tayi tace na dena d only bro, sosai yaji dadi sannan yaja suka tafi. Karfe biyu ya tafi skul dinsu, yana isa suna fitowa daga aji, ya dauketa suka tafi gida, kasancewar yau bayi da wani aiki yasa yana xuwa yaje ya watsa ruwa ya kwanta adakin nur. Karfe hudu ya farka yaga nur xaune gefensa tana assignment, ya mike ya shiga bandaki ya dauro alwala sannan ya yi sallar laasar. Yayana har ka tashi, "na tashi kanwata, dama inaso muyi magana dake, ta ajiye litattafan tace inajinka yayana, dama kanwata na samo miki malami dazai dinga koya miki karatun addini, agida sannan zan kaiki wata makaranta ta koyan girki, kwalliya da sauransu, cike da jin dadi tace" thankyou yayana Allah ya biyaka"amin yace shikam nur tana burgeshi saboda gata yarinya amma tasan abun daya dace . *bayan kwana biyu* Malam sadi shine xaiyiwa nur karatun addini agida misalin karfe hudu da rabi xai dinga zuwa yana koyar da ita na awa daya da rabi, sun fara da tauhida yadda zata san waye ubangijinta. Sosai nur take gane karatu domin daya gama mata ya mata tambayoyi ta amsa, yaji dadi sosai shima, haka kuwa yake xuwa kyllum biya mata karatun. Yayana sannu da dawowa"yawwa kanwata ta karbi jakarsa ta ajiye mai, taje ta hada mai ruwan wanka, baki kawai yasake yana kallon ikon Allah, ta fito ta sameshi xaune bakin gado, ta xauna ita ma, tace yayana na hadama ruwa kaje kayi wanka, toh yace ya mike ya nufi bandakin sai dayaje kofar bandakin sannan ya juyo yace ko zaki tayani ne?"ta girgiza kai alamar a'a, ya shifa yayi wankansa. Yau amfara koyawa nur girki bayan ankoyar da ita yadda xata kula da mijinnta, tana ta doki ta dawo dama yau girkin ta ne ta hadawa yayanta abinci. Driver na direta ta shiga gida da mugun gudu, bankada kofar falon tayi ta shiga bako sallama tsananin doki ta manta ma ana sallama, Jitayi an dauketa da mari, ke wai wace irin jakace kuma yaushe xakiyi hankali dabba kawai, ta juyo afusace tace ke!malama karki kara marina kuma karki kara cemun jaka if not i will deal wit u useless kawai tayi gaba abinta, baki Aisha ta bude tana kallon Nur harta isa dakinta, kaya ta canja tasa simple kaya sannan ta nufi kitchen. Jallof rice tayi gidan ya dume da kamshi, Aisha na daki ta dinga jiyo kamshi cike da mamaki ta fito kichen din ta nufa kai tsaye ganin Nur na hada juice yasa ta tabbatar ita tayi wannan girkin, Aisha tace ke uban waye yasaki girki budan bakin Nur tace ubanki, ta dauko hanu xata sake kai mata mari taji anrike hanun ta baya, taji ance in kika kurkura kika dakamun mata kin daki aurenki, ya saketa, oyoyo yayana nur ta fada tayi gunshi rumgumeshi tayi sannan ta riko hanunsa ta sumbata tacw"welcm cwt bro thankyou my sis, ta amshi jakar sukayi daki, suka bar Aisha tsaye ta xubawa sarautar Allah ido. Nura ya tafi masallaci sallar isha kafin ya dawo Nur tayi wanka ta feshe jikinta da turarw ta sanya riga da wando masu shegen kyau pink colour, ta warware gashinta ya watso abayanta ta fito falon lokacin Nura ya shigo da saama, ta karasa gunshi ta ce wlcm yayana, ya rikota suka nufi dinning yana bude flask din wani kamshine ya bigi hancinsa, ya dago yana mata kallon tuhuma, gira ta daga mai tace daga yau ka dena cin abincin restuarant, yace toh oya go nd call ur aunty, ta mike ta nufi dakin Aisha, bankada kofar tayi tace inkin ga dama kixo muci abinci, Aisha ta biyota amma ina ta tsere, aisha na xuwa tace Allah ya kiyaye naci abincin wannan jakar, yar kauye, lokacin Nur ta mike tace ke saurara maratarbiya na miki warning baki jiba ki daina cemun jaka, aisha tayi kan Nur tuni nura ya dakatar da ita. Sosai nura ya yaba girki kuma yayi hamdala da Allah yasa xamansa da Nur hadin Allah ne Muje xuwa anjima By Shamsiya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:30 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 101-105 Kwanci tashi ba wuya wajan Allah su Nur an gama pri sch ana shirin shiga jss 1 ba laifi ta fara girma amma har lokacin bataje panisau ba sbda ya fi so Nur taje a yadda ba iyayenta ba kowa sai yasan tayi hankali ta nutsu, Sai dai shi baya wata biyu bai je ba, "Yaya kaga saura izu goma na hade qurani na hadda ta kuma kaga nayi izu ashirin da biyar so nake ka hadan walima sosai idan na hade sittin dina na kuma haddace talatin, insha Allahu kanwata amma ba yanxu ba nafiso sai kin gama ss3 kije ma su umma amma in akai walima kinga dole sai an fdawa su, ni dai yaya ina so amin ko ba a fdawa su umma ba, kar ki damu kanwata yadda kikace haka zaayi ya fda yana jan kumatun ta, Cikin ikon Allah Nur aka shiga jss 1 sosai take maida hankali wajan karatun ta Mlm sadi ne ya bawa nura shawara akan ya sata islamiyyar da yake koyarwa sbda zata samu littatafai da yawa, nura ya gamsu da batun mlm sadi kuma yace zata fara zuwa ranar asabar amma da sharadin zai na mata a gida ma, mlm sadi ya yarda Nur ce cikin uniform dinta tana bakin gate tana jiran yayanta dan yau ya kara lokaci da yawa baixo ya dauketa ba, fuskarta a hade kamar bata taba dariya zama tayi ta dora kanta a kan kafarta sbda gajiyar da tayi, "Yan mata ya akayi ne naga kinyi shiru ke kadai ba azo daukan ki bane, wani matashin saurayi da bai wuce shekara 15 jikinsa sanye da uniform ya fda yana zama kusa da ita, dago kanta tayi cikin kotsawa wlh baa zo daukana bane shiyasa, duk maganar da suke cikin turanci suke yinta, kafin yay maga motar Nura tai parkn ganin Nur da wani zaune kuma yaga alama hira suke ransa yay mugun baci, ga kuma kishi da ya tokaresa, Ganin motar yayan nata yasa tayima saurayin sallama ta nufi motar " yaya barka da zuwa ya rana, yau bakazo da wuri ba, nur ta fda tana rufe murfin motar bayan ta zauna, Ko ta kanta baibi ba ya ja motar suka bar wajan Ganin yanayin yayan nata yasa ta kalleshi jiki a sanyaye " yaya laifi na maka kaki kulani, cikin bacin rai ya taka burki ya tsaya, " au sbda tsabagen rashin mutunci ma tambayata kike me kika mun bacin nazo na tadda ki da wani katan kuna hira, nura ya fda yana kallonta, Ba karamin razana nur tayi ba da ganin yanayin yayan nata dan tin da take dashi bata taba ganin sa a haka ba " yayana wallahi ban taba hira da shi........ Tsawar da ya daka mata ne ya sata hadiye zancenta, " wlh nur in baki min shiru ba sai na kwada miki mari bokon kin gamata daga yau tin da baza ki kare kanki ba, Kuka sosai nur takeyi a motar har suka je gda, tinda nur ta fara kuka yake jin kukan a ransa amma ya dake yay banza da ita kamar bai san tanayi ba, Nur na fita daga mota part dinta ta nufa ko jakarta bata dauka ba ta tafi tana kuka, lokaci Aisha na zaune a harabar gida tana waya kasa kasa ganin yanayin da taga nur yasata jin dadi, cikin faraa ta taso ta nufoshi, " honey sannu da zuwa, yauwa swt hrt ya gda,nura ya fda yana kakalo murmushi shi a dole bayaso ya gane Aisha ta gane sunyi fda, "Honey wallahi daman tin dazu nake jiranka gaba daya missing dinka nake, gidan yau naji ba dadi, Aisha ta fda tana shigewa jikinsa, " nima kan nayi msn naki da yawa swt hrt ya fda yana ruko hannunta suka shiga ciki, Aisha ce ta temaka masa yayi wanka, nan ta shiga janyo hankalin mijinta, cikin mintunan da basu fi ashirinba suka lula duniyar masoya, Gaba daya Aisha ta mantar dashi komai dan tn da ya auri Nur Aisha bata mallaka masa kanta gaba daya in kwa taga a matse yake toh sai ta gama ja masa rai ranar haka suka kasancr har goman dare suna farantawa junansu, a haka bacci yay gaba dashi Nur kuwa na shiga daki akan kujera ta kwanta tana rero kuka bayan anyi kiran sallar laasar tayi sallah ta juya ta shiga ba da sharar kuka a haka bacci yay gaba da ita By shamsiyyah salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:30 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 106_110 Washegari da asuba Nura ya farka ganinshi dakin Aisha baiji dadin hakan ba duk da ranar girkinta ne, ficewa yayi ta kwashe da dariyar mugunta, dakin Nur ya nufa tana xaune kan sallaya ya shigo da sallama, amma fuskarsa bako alamar annuri, ta dago suka hada ido ganin yanayinsa yasa ta saukar dakai, ina kwana yayana, lfy yace atakaice ya juya xai fita da sauri ta riko mai jallabiya pls im really sorry yayana i dont mean to hurt ur feelngs pls forgive me. Durkusawa yayi yana kallonta ta ce pks, ya dago habarta is ok kanwata komai ya wuce amma kinsan ke matar aure ce kuma bai dace ki dinga kula wasu mazan ba, ni ne mijinki ni kadaine xakiyi hira dani sai abba da daddy, kai ta daga mai alamar taji tace insha Allahu bazan sake ba, murmushi yayi yace toh maza tashi ki shirya da wuri kar mu makara. Dakinsa ya nufa acan yayi wanka ya shirya, yana fitowa yaga Aisha xaune afalo tana ta danna dannen waya, honey ina breakfast dina"swt hrt kasan dai ba girki nake ba don haka ban daura ba, juyawa yayi ba tare dayace komai ba ransa yana suya dakin Nur ya shiga, tana shafa mai yayi sallama, hijab dinta ta dauko tasa, sannan tace yayana har ka shirya gashi ban gama ba, "no kixo ki hadamun breakfast, " a'a auntyn fah?, kawai kije ki hadamun breakfast xatayi magana yasa hanu abakinsa alamar tayi shiru. Cikin mintuna da basufi arbain ba ta hada mai tea ta soya mai dankali da kwai, ta dauko tazo wucewa Aisha ta mike ta jawo mata gashin kanta ke! Ubanwa kikayiwa wannan abun, budan bakin Nur tace wa uwarki, taja tsaki tayi gaba abunta. Aisha tana zaune ranta ya gama baci, Nurane ya fito yana rike da jakar Nur, da hanxari ta mike ta isa gabansa ta fara zazzaga masa ruwan bala'i, ai ya kawo yarinya ta raina ta, Nur kam ta watsa mata harara, ta kamo hanun yayan nata tace my Dear lets go tym is going, cikin mamaki suka kalli nur ta daga ma yayan nata gira tace haba my Dear kaxo mu tafi mana ko so kake adakeni? Ashagwabe tayi maganar sosai yaji dadin hakan, nan ya manta da Aisha tsaye ya sumbaci goshin Nur yace muje ta juyo ta kalli Aisha kallin wulakanci sannan tace"thankyou my dear. Yanayin da nur ta fara nunawa mijinta ya fara dagawa Aisha hankali, ga uwa uba yarinyar ta fara gogewa sosai akan zaman aure sannan taga alamar yarinyar nan komai na jikinta sun bayyana, domin kirjinta ya ciko, komai dai masha Allah. Kwanci tashi asarar mai rai Kokarin Nur yasa ta tafi ss1 nan ne ta hadu da gogaggun kawaye wadanda suke yayan mutunci nan fa suka dinga sata a hanya yadda zata kula da mininta, kuma tana daukar abunda suke fada mata don ta kuduri niyyar cusawa Aisha bakin ciki. Yau girkin tane tun data dawo take ta faman aiki, hadaddan abinci ta shiryawa yayan nata da juice kalakala, sannan taje tayi wanka, ta turara dakinta da turaren wuta. Tana zaune bakin madubi tana kwalliya Nura ya shigo da sallama, ta mike tana taku dai dai ta isa gu sa, "wlcm my dear ta rumgumeshi, nan yaji wani abu ya tsirga mai har tsakiyar kansa, ta sakeshi taje ta karasa adonta, yana xaune ya xuba mata ido har ta kammala, ya fito mata da kayan da zata sa wani dankarararan leshine dan ubansu tana dariya tace thanks dear ya tayata sawa sannan taje ta hada mai ruwan wanka. Tare suka jero xuwa dinning lokacin Aisha tana zaune shaf yama manta da ita suka zauna suna shewa ya zuba musu abinci.nan Aisha ta taso tana huci. Toh ku biyoni don jin yadda xaa kaya nidai naja sis shamsiya da Abul. By Shamsiya salis & Haima(mmn Abul) [4/30, 5:30 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 111-115 " wuyan nur Aisha ta danka " wlh baki isa ba uban me kike takama dashi da zaki dinga min iskanci a cikin gidana, banza jahila yar kauye, Duka nur ta kaima Aisha lokacin da ta kwaci kanta, da ubanki nake takama, bnza tabba kawai, wlh baki isa kin min na kyale ki, ganin fada suke iya karfinsu ya sa yaja hannun nur ya kaita gefe, ku me yasa baku da hankali kwata kwata baza ku rike mutuncin ku ba ko so kuke ku doran hawan jini, nura ya fda ransa a bace, Ai tin da ka auro jahilar nan ka gama samun kwanciyar hankali a gidan ka, Aisha bn isa nace kiyi shiru kiyi ba, ai wallahi nura ba ka isa ka sa wannan kucakar yarinyar kuma jahila dabba wadda ita da kare basu da maraba a wajena, wlh ni ba jahila bace kuma jahilar da ki ke kira tana gda tsohuwar bnza mai zuwa gidan yarta tana lalata tarbiyar yarta, kuma.... Dukan da nura ya kaimata a baki ya sata yin shiru, " nur Aishan saarki ce ko mumyn saar kkce da zaki na zaginta, " ita baka ga abinda ta min ba sbda ita kana santa shine ita bazaka daketa ba sai ni ka daken, Nur ni zaki ma rashin kunya, Aishan ai ba saarki bace, Toh dan ta girmeni shine akace ta zagen ko ta dake ni, ai bbu adalci a cikin a..... Duka ya kara kaimata a baki cikin fushi nur tai bngaranta, "Aisha kinji kunya wlh banza a duniya ma akwai jahila kamar ke ki zauna kina fda da yar cikin ki wlh girma ya fdi, nura ya fda rai a bace, " dariya Aisha tayi shi yasa naga kai da kaja girman ka bata ma rashkn kunya, cikin bacin rai nura yay bangaran nur, Lkcn tana kwance akan gadon ta tana rera kuka, jikinsa a sanyaye ya karasa inda take dagota yayi ta kwace, " kanwata kiyi hakuri wallahi ba da niyya na miki ba, batan rai kikayi, yanxu nur ita bata barni na zauna lpya ba sannan kema bazaki barni na zauna lpya ba, gashi nan kinsa tana min gorin bakya min biyayya, ita bata ji magana ba kuma kema haka, kiyi hakuri idan na bata miki, Ya fda yana mikewa har yaje bakin kofa Aisha ta fara magana cikin dasashiyar murya, " yayana" a inda yake ya tsaya bai juyoba kuma bai tafi ba, " jiki a sanyaye ta taso tazo inda yake, " yayana kayi hakuri bazan karaba, ka yafemun bata maka da nayi, fuskarsa dauke da murmushi yace na yafe miki, muje my ci abinci, ba musu ta biyoshi suka ci abinci sannan suka kwanta Kwanci tashi ba wuya wajan Allah su Nur an shirin fara waec nan da wata data, sosai nur ta maida hankalinta wajan karatu, Har lokacin nura bai taba kusantar ta ba duk da fama da shawarta da yake, dan Nur Allah ya bata diri dan duk wani abu na cikar mace Nur na dashi, Yayi ma kansa alkawarin bazai taba kusantar ta ba har sai tayi candy abu daya da yake damunsa rashin fara aladar da batayi bane har yanxu, Kukan Nur ta nura ya jiyo ne ya katse masa tinani, cikin sauri ya nufi inda take, tqna durkushe a kasa tana murkutsutsu " nur mai ya sameki, baki da lpya, daga masa kai tayi alamar eh dagata yayi dan ya kaita asibiti, turus yayi ganin jini a kasa inda take, daukarta yayi ya kaita bandaki yace tai wanka, dakinsa ya nufa ya dakko pad, daman ya dade da siya sbda jiran zuwansa, da kansa ya sa mata pad din a pant dinta, sannan ya nufi toilet din ya kai mata lakacin ta gama wanka kan ta fito ya gyara wajan, Sanda ta fito ya sa mata doguwar riga mara nauyi ya rike hanunta suka nufi asibiti, magun guna aka hada mata sannan aka mata allura suka dawo gida Cikin dare ciwo ya kara addabar nur kwata kwata ta kasa sukuni ko kadan Nura na gefenta haka suka raba dare sai kusan asuba bacci mai nauyi ya dauke su Kwanci tashi ba wuya wajan Allah yaune su Nur suke zana jarabawarsu ta karshe a neco, daman sunyi jamb Alhamdulilah sakamakonsu ya fito da kyau har ya zarce yadda ake so Karfe 12:00 dai dai suka fito daga exam hall dinsu sosai suka rikita makarantar da hayaniya suna ta faman rubuce rubuce ana ta exchangn number, ita dai nur saidai ta rubuta a takadda sbda har lokacin nura bai sai mata waya ba, Wani kyakywan saurayi ya nufo inda ya tadda su tsaye, Yan mata sannunku, Hafsat kawar Nur tace yauwa sannu, nasan baku sanni ba sbda ni ba dan makarantar ku bane amma tare mukai neco daku, tin ran da na fara zuwa da naganki naji ina san kawarki ya fda yana nuna Nur, harara ta watsa masa, kaga dalla malam ni matar aure ce kayi hakuri ta fda tana mikewa hijab dinta ya janyo wanda yay dai dai ta tsayuwar motar nura a wajan Ku kasance damu danjin yadda za a kaya By Shamsiyya salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:30 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 116-120 Wawan mari Nur tayi ma saurayin da ya ruko mata hijab dinta " kai wani irin dan iskane mara mutunci wanda bai san darajar mace ba, na fda ma ina da aure shine zaka rukon hijab, Nur ta fda ranta a bace, Sosai nura yaji dadin yadda nur tayima saurayin ya tabbata duk inda nur take zata rike masa mutuncinsa, a hankali ya karaso inda take "Kut ni kika mara kinsan ko ni waye wallahi sai kinyi da kinsanin marina saurayin ya fda cikin borin kunya " dana sani uwarka zanyi shege mara mutunci, kuma sanin ko kai waye ba matsalata bace, domin baka da daraja da kima kamar ta miji na kuma insha Allahu kaima sai an ma matarka, banza jahili kawai, ta fda tana juyawa, ganin Nura a tsaye yasa hankalintq ya tashi dan bata san dame zai zo mata yau ba, " yayana ta fda cikin tashin hankali, har ta nufeshi sai kuma ta juya ta ruko hannun kawarta, " plsss hafsa ki fda masa yadda akayi wallahi yayana ban kulashi ba, shine yazo waje na dana ce masa ina da aure na tashi shine ya ruko min.... Hanunsa nura ya dora a baki alamar tai shiru, " naga komai kanwata kar ki damu ai na yarda dake, cikin jin dadi ta rungumeshi " na gode yayana " kar ki damu kanwata ya fda yana dagota daga jikin sa a mota ya sata sannan ya koma wajan saurayin, " zan maka uziri a yau sbda hukuncin da matata ta dauka akanka ya burgeni ko ba komai ta disgaka a gaban mutane, wannan kadai ya isheka tashin hankali, kuma kamar yadda tace insha Allahu sai an maatarka fiye da abinda ka mata, nura yay tsaki ya bar wajan Yau sati guda da gama makarantar Nur tana zaune a falonta tana kallo nura ya turo kofar tare da yin sallama, cikin faraa ta tashi taje ta tarosa tare da rungumeshi, sannu da zuwa yayana, " yauwa kanwata ya gida, wlh gashi Alhamdulilah, muje kayi wanka ta fda tana ruko hqnunsa, da kanta ta temakamashi yayi wanka sanda ya fito ya taddata kan gado tana jiransa, kusa da ita ya zauna tare da rungumota, Nur ina sanki sosai, nima haka yayana, kiss masu zafi ya shiga yi mata wanda nan take ya fara manta duniyar da yake ciki, ganin Nura na neman wuce gona da iri yasa nai sauri janyo hannun sister haima muka bar musu dakin, Kukan da naji Nur nayi ne kuma ana rarashinta yasa nai saurin karbar biron wajan sister haima na nufi inda nake jiyo kukan Nur ce kwance jikin nura tqna rero kuka kamar karamar yarinya, kiyi hakuri kanwata baxan karaba kinji ina sanki sosai na gode da yadda kika tsare mun budurcin ki, fatana Allah ya barmu tare, Washe gari da safe nur kwance kan doguwar kujera tana kallon hotuna a wayar nura ya fito daga daki " kanwata zan wuce wajan aiki ki shirya da laasar zan dawo na kaiki ku gaisa da mumy daga nan sai mu wuce muyi wa umma Abba da kakq siyayya jibi zamu tafi panisau Ihu nur ta Saki nagode yayana amma dan Allah bari na shirya ka saukeni yanxu gidan mumyn mafi shan hira da ita, " haba nur yanxu sai da na gama shirina kuma fa da auntyn ki zamu fita tin dazu ta shirya, " yayana kaya fa kawai zan canxa, toh sa kayanki ai akwai bata lokaci, Wayarsa ta mika masa fuakarta a hade ta koma ta kwanta a kujera Girgiza kansa yayi ya karaso inda take " sorry my dear tashi kije ki shirya amma karki bata lokaci kinji, Cikin murna tace " thank yuh ta fda tana shigewa daki, Aisha sosai ranta ya baci ganin tin dazu take jiransa yaki fitowa Ganin nur zata bata masa lokaci ya sa ya leka " kanwata ki sameni a wajan mota" "Toh yayana" "Swt hrt kiyi hakuri ki daina bata rai haka nan, " haba honey tin dazu fa nake jiranka, yi hakuri taso muta tafi ha fda yana ruko hanunta Tus yayi sbda abinda ya gani cikin mamaki ya karasa inda take "Kanwata me zan gani ba fa yau za mu tafi panisau din ba na ganki da akwati" eh na sani yaya amma ai zan canza kaya kaga kan laasar, sannan kuma in za mu fita da mangariba zan canxa dariya yayi ya karbi jakar yasa a baya Aisha kuwa ranta ba karamin baci yayi ba da taga da nur zasu tafi dariyar tayi sanda ta tuna zatai an fani da damar nan ta kunsawa nur bakin ciki fuskarta dauke da murmushi ta bude gidan gaba ta zauna, nur kuma ta zauna a baya ya ja motar yay waje By shamsiyyah salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:31 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 121_125 A gate din gidansu yaja ya tsaya , Nur ta bude kofa tayi waje, fitowa yayi ya dauka mata akwatin har ciki ya mikawa mai gadi, Aisha kuwa ta cika ta batse, Nur tana satar kallon Aisha sai da ta tabbatar su take kallo ta marairaice fuska"yayana wlh bana so ka tafi ka barni, nafiso ko yaushe na ganka kusa dani, nima haka kanwata amma kiyi hakuri zanje na kai Aisha gidansu xan dawo yau tare zamu wuni dake agidan mummy, sosai tani dadi ta rumgumeshi tace i luv u so much, "luv u too my dear ta silale tayi cikin gida, yana shiga mota Aisha taja wani tsaki har cikin ransa yaji tsakin amma bai tanka ta ba yaja suka tafi, itama akofar gida ya sauketa yayi gaba. Nur da sallama ta shiga falon ganin ba kowa yasa ta nufi dakin mummy, da sallama ta shiga aka amsa mata da gudu tayi kan mummy tana murna, mummy tace ke! Ni dallah karki karyani mana, mummy tana murmyshi tace sannu da zuwa ya'ta, lokacin daddy ya shigo, durkusawa nur tayi ta gaida shi cikin ladabi, ya amsa yana murmushi yace ina mijin naki?, sunkuyar dakai tayi tace ya kai Aunty Aisha gida xai dawo, toh ita shine bata shigo ta gaida mu ba, Ita dai nur bata ce komai ba ya mike yayi waje. Nur da mummy sun taba hira, sannan Nur ta nufi kitchen, nan ta fara shirin girkin abincin rana, mummy ta rasa ina Nur take, kamshin abincin dataji ne ya bata amsar inda take, kitchen din ta nufa a kofa suka hadu Nur dauke da kololin abinci biyu, murmushi mummy tayi tace sannu da aiki, a kunyace Nur ta ce kai umma meye abun sannu don na dafawa iyayena abinci, sosai umma taji dadin jin kalaman Nur yanxu ne tasan tayi dacen sirika, aranta ta ce har da ina kokarin korre wannan baiwar da Allah yamun, Nur ta wuceta taje ta jera komai a dinning. Ta gama Hada komai ta shiga wanka bayan ta fito dama azahar tayi ta dauro alwala tayi salla, tana idarwa ta shirya cikin wata atamfa, sosai dinkin ya amshi jikinta, ta feshe jikinta da turare sannan ta mike xata fito falo, taji an murda kofa, Nura tagani tsaye ya harde hanu yana kallonta sai murmushi yakeyi, yayi balain mata kyau, ta karasa tana mai sannu da dawowa, bude hanunshi yayi alamar taxo, noke kafada tayi tace yaya mummy da daddy fa suna nan, "toh meye ke ba matata bace, taki aikuwa ya karasa cikin dakin har inda take ya rumgumeta, badan taso ba, suna cikin wannan yanayin mummy ta iso ganin su yasa taja da baya ta koma, su kam sun lula don basu san ma ta xo ba. Karar wayar daddyce ta katse musu jin dadi, ganin sunan daddy yasa shi daga wayar da sauri, kuzo muci abinci, toh kawai yacw ya katse wayar, yaja hanun Nur suka nufi dinning. Nur ce tayi serving kowa, kamshi ya bude falon, daddy ya kalli mummy yace yau kam saboda sirikarki taxo shiyasa kika mana abinci mai dadi ko,?, ya fada yana kallonta, itama shi take kallo, " lailai sai dai muyi godiya wa Allah domin munyi dacen sirika tagari, a kunyace Nur ta sunkuyar dakai, sukayi adduar fara cin abinci sannan kowa ya fara ci, Nur takai loma uku xata kai na hudun kenan sai Amai, tuni Nura yayi toilet da ita, haka ta jigata dan sai data amayar da komai dataci, cikin rudani Daddy ya umarci Nura akan suje asibiti. Suna isa likita yasa ta kawo fitsari ya dau jininta gwajin farko sai ga ciki barovaro, sosai Nura yayi murna dajin wannan albisbir, kyautar dubu dari yabawa doctor, gidan su mummy suka wuce, kowa yaji dadi sosai, mummy tace lailai sai dai Nur ta dawo gidanta da zama ta reni jikanta, ta budawa idonta toka taki yarda haka dole suka yarda amma sai sunje panisau sun dawo. Toh ku biyomu don jin yadda xata kasance Daga alkalamin Shamsiya salis Da Haima(mmn Abul) [4/30, 5:31 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 126-130 Nura bai bar gidan ba sai kusan sha daya sai da mumy ta takura masa, da Aisha ta masa waya yqce ta tafi yana da uxiri, sanda ya dawo gida har tayi bacci, dakinsa ya nufa yayi wanka sannan yay alwala yay sallah ya godewa Allah da Allah ya bawa nur dinsa ciki fatansa Allah ya sauketa Lpya Washe gari nura bai tashi ba sai kusan sha biyu na rana, yana tashi yay wanka ya nufi dakin Aisha tana zaune a falo tana chrtn, Kusa da ita ya zauna swt hrt kin tashi lpya, lpya lau honey naga yau kasha bacci, bari kawai, jiya banyi bacci da wuriba ina aiki, Ina break fast dina, amaryar taka bata yi ma ba, amarya ai a gidan mumy ta kwana, ai sai ka bita can ka ci, " haba swt hrt me yasa kike haka, bai kamata ba fa ni mijinki ne, yanxu yaushe rabon da ki min girki, Ai ba kana da wayayiyar kauye ba sai kaje ta maka, swt hrt ki fita harka ta wallahi zan mareki ni bnsan iskanci, Ya fda rai a bace yay waje Nur na zaune a falo tin tara take jiran zuwansa amma shiru mumy na kule da ita amma ta kyaleta, Nura ne yay sallama tare da shigowa falon, mumy ce ta amsa masa sallamar kusa da nur ya zauna bayan ya gaida mumy " ina kwana, nur ta fda ciki ciki, " lpya lau, mumy me akama nur ne naga ranta a bace, nima ban sani ba ai kunfi kusa sai ka tambayeta, " mumy da abinci yinwa nake ji, wani irin yinwa ba daga gida kake ba, wlh mumy daga gida nake amma bata girka ba ya fda yana sosa keya, toh ai sai kaje kaci gashi can a dining, ba musu ya mike ya nufi dining mumy kuma tai daki, A hankali yake cin abincin yana satar kallonta amma kwata kwata bata kallonsa ta mai da kanta ga tv tana kallo, " nura ai ba inda zaka koh ga nur nan ka kula da ita zani anguwa yanxu amma da wuri Zan dawo, toh mumy Allah ya tsare Mumy na fita nura ya taso daga dining ya taho inda take haba zabina, me ya faru fishin me kike yi Aisha ta bato min rai nazo inda zan samu sauki, sai na tadda azabar da tafi wancan na gwanda Aisha tamin rashin kunya da ke ki fushi da ni, "Kanwata ki ce wani abu mana sai magana nake kin shareni, hararsa nur tayi tare da turo bakinta gaba " kanwata ni kike hara😳 nura ya fda yana zaro ido " eh din an harara Dana San bakai break fast ba wallahi da bayar da abincin zanyi 😚 shikenan tinda kin tsaneni, nura ya fda cikin shagwaba, sosai ya burge nur hakan yasata fara kyakyatwa, Gaskiya yayana kayi girma da shagwaba amma fa kayi kyau sosai, dariya yayi na gode kanwata, "Amma yayana kasan zanyi missing dinka shine ka ki zuwa da wuri, bari kawai kanwata kinsan Allah ina tashi wanka kawai nayi na taho, Har shabiyu fa bn tashi ba " ayya kasha bacci, daman kayana zanje na debo Wanda Zan tafi dasu, "Toh bari mumy ta dawo sai muje " ina zaku mumy ta fda tana shigowa ciki " yauwa mumy kayana zan debo, kwana nawa zata yi in ta je, mumy kwa Biyar nura ya fda yana kallonta " wallahi aa mumy sati hudu zanyi, 😳zaro ido nura yayi " gaskiya nur baki da hankali wlh,kawai sai na barki ki tafi kiyi wata guda a can " toh ai baiyi yawa ba shekarata nawa rabona da garin tinda ka dakko ni daga garin baka taba kaini ba sai dan nace zani yanzu kace baka san zance ba, " wlh nur kika batan rai sai na hanaki gaba daya naga in kina da ikon barin kanki, " bnda iko amma dai.... Mumy ce ta katseta ganin suna sanyin fda, " nura ban san musu kawai ka barta tayi wata dayan tinda sanda ka hana ta zuwa ta maka biyayya bai kamata yanxu ka hanata zuwa ba, Idan kinje ma kiyi shekara ki ga in zan damu, kisa driver ya kaita dakko kayanta, gobe in na sauke ki nur a panisau dan Allah kiyi zamanki kiga in zan nemeki, nura ya fda cikin bacin rai " wannan kuma matsalar kace ba tawa ba Ta fda tana shigewa daki, Sai da akai laasar mumy tasa driver ya kaita gidan ta, lkcn Aisha na zaune ita da kawayenta suna shewa, Hararsu tayi tai gaba, " Aisha wannan kuma wace, kar ki ce mana kishiyar ki ce, " ita ce mana, kai amma fa tana da kyau, mtswwww kinga bansan iskanci Nur na shiga daki ta fara hada kayanta sai da ta cika akwati biyu da kaya sannan ta kira driver yazo ya daukar mata Sosai Aisha da kawayenta suke mamakin ganin yadda nur ta lodi kaya, " Allah na godema da ka nunan wannan rana shegiya mayya ai daman mijina nawa ni kadai gasshi nan kin gama yayin ki an sallameki, Aisha ta fda lkcn da nur tazo kusa dasu Mtswww tsaki kawai nur tayi ta nufi mota Ku kasance damu danjn yadda zata kaya tsakanin nur da nura By Auntyn abul & Mmn abul [4/30, 5:31 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 131-135 Cikin mamaki nura da mumy ke kallon driver da yake ta faman shigo da kayan nur a akwati, " lalaima yarinyar nan watakan bata san gatse ba kenan" nur ya fda a ransa " Hadi me zan gani haka wadannan kayan fah, kan yay magana Nur ta shigo mumy nawa, Nur wannan kayan ai sunyi yawa " a'a mumy basuyi yawa ba, toh nur Allah ya tsare " Amin mum" Washe da asuba Nur bata koma bacci ba daman batai wani baccin kirki ba, Kara shirya kayanta tayi sannan ta fito ta Dora girki A bangaran Aisha kuwa kaguwa tayi nura ya dawo taji dalilin kwasar kayan, amma tin tana duba agogo har ta daina ganin bashi da niyyar dawowa a haka bacci ya kwasheta Tin da tai sallar asuba ta shiga kitchen ta hadawa nura abinci kala kala, bayan ta gama girki tayi gyaran daki sannan tai wanka, dakin nura ta wuce kai tsaye, da sallama ta shiga dakin, ya amsa mata ba yabo ba fallasa, swt hrt ina zuwa haka naga kana shiri da wuri, unguwa zani, ya fda a takaice, wayarsa ya dauka da mokulli yabi ta gefenta zai wuce, swt hrt bafa ka ci abinci ba kuma na gama, ya juyo a fusace zaiyi magana, sai kuma ya fasa, muje na ci dan sauri nake, murmushi tayi ta rike hannunsa har dining, bayan sun fara cin abinci, Aisha ta dago ta kalleshi, swt hrt wai ina Nur ne naga bata kwana a gidan kwana biyu kuma sai naga jiya tazo ta dibi kaya, Wani bakin ciki ne ya tokareshi shiyasa kenan yau har dayi masa girki ta zaci sakin nur din yayi kenan, nura ya fda a zuciyarsa, a fili kuwa yace ban sani ba nima jiyan ai da kin tsayar da ita kinji inda zata, ya fda rai a bace tare da daukan key dinsa yay waje daman ba jin dadin girkin yake ba, Duk suna zaune a falo suna jiransa dan har kayanta ta fito dasu, da sallama ya shigo mumy ta amsa masa, nur kuwa ko kallansa batayi ba bare yaci arzikin gaisuwa, mumy kan kyalesu tai dan ta san da kansu zasu shirya, Hadi ne ya zo ya debi kayan yasa su a mota sannan suka fice, Nur ki gaishe da umma kafin nazo ga kuma wannan kya basu ita da Abban naki, Mumy ta fda tana mika mata wata katuwar leda, toh mumy an gode ta karba tana sawa a motar, murfin motar baya ta bude zata shiga, Cikin bacin rai nura ya daka mata tsawa " uban waye drivern ki da zaki shiga baya, " haba nura baka ga yarinya bace, da auta suna nan ma tare zasu tafi toh sun min yajin aiki nima, saura kana mata tsawa a hanya ma " ke kuma ki fito ki koma gaba ban san rashin kunya, turo baki tayi sannan ta fito ta koma gaba yaja motar suka dau hanya Tin da suka tafi ba wanda yay wa wani magana, ganin ta gaji da yin shiru yasa ta dakko wayarta da mumy ta siya mata jiya ta fara kallo da ita, a haka har suka karasa garin panisau mai albarka, gari mai niima garin da kowa yake son sa, Yi hakuri sister Haima kar kiji ina koda garin mahaifata ce😜 Ihu nur ta Saki sanda ta ganta a kofa, wannan dalilin ne yasa nura sa burki bbu shiri " ke meyasa baki da hankali nur sbda munzo zakinayi ma mutane ihu, turo baki tayi bata kulashi ba ganin bata da niyyar yin magana tasa shi jan motarsa sukai ciki, " suna isa fada kowa ya bi su da kallo kuma ana yaba kyan yarinyar da ke gaban motar, a haka har suka shiga layin su, motar bata gama tsayawa ba nur ta fice da gudu " ummana ummana ummana, Kamar daga sama umma tajiyo muryar gudan jininta da sauri ta fito daga dakin dan ta tabbatar da ita dince ko gixon da ta sabayi mata nene Allah ina rokonka da sunanyenka tsarkakaku guda dari bbu daya Allah ya bawa abul kair lpya Allah ya albarkaci rayuwarsa, Allah yasa ni auntynsa, mamansa da kuma duk wani alummar musulmai suyi alfahari da shi amin summa amin Daga taskar Shamsiyya salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:31 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 136-140 Mutuwar tsaye umma tayi sanda taga yadda gudan jininta ta zama babba, Rungumar da nur tayi wa umma ne ya katse mata tinaninta, " ummana nayi misssin dinki alot, Murmshi umma tayi dan ba sanin mene mssn tayi ba, " nur kece kika girma haka, " ummana nice ina Abba, kan umma tai magana nura ya shigo rike da karamar akwatin nura yara biyu kuma matasa na rike da sauran kayan " yanxu nura da tare kuke kika kyaleshi da dibar kaya, sannu da zuwa nura umma ta fda fuskarta dauke da mirmushi kuma tana shimfida musu ta barma, Bayan sun gagaisa umma ta gabatar musu da abinci da ruwa suka ci sannan suka dora hira sosai umma taji dadin yadda yarta ta ta koma Bayan sallar laasar nur ta sake yin wanka ta shirya cikin wata dakakiyar doguwar riga ta shadda, tasa takalmi da jaka sai gyale kalar kayan, tsayawa fadar irin kyan da tayi bata lokaci, bayan ta gama shirinta ta fito ta tadda umma na shan inuwa, Ummana bari na dan zaga zan iya kaiwa dare idan yayana ya dawo kice mashi na fita zaga gari, " toh nur a dai kula, kai ummana yanzu fa na girma sosai, " ai naga alama kan, dariya nur tayi tana ficewa Ajiyar zuciya umma tace in banda *Hadin Allah* nur da ban san ya rayuwarta zata kasance ba, Allah ina godema, Allah kara hada kansu, " nur na fita makotansu ta zazagaya duk inda taje sai tayi bayani ake gane ta Wani gida ta shiga da ke gab da wakeken dutsen panisau yana kallon ramin da kuma masallaci a kofar gidan da sallama ta shiga, Wata mata ta amsa mata tare da mata shimfida, Bayan sun gaisa matar tace baiwar Allah ban gane ki ba fah, Murmushi nur tayi, " yanxu baba magajiya baki ganeni ba, daman zuwa nai ki kwatanta min gidan Asabe naje mu gaisa, cikin mamaki matar tace a ina kika santa, " baba nur ce fah dazu nazo, Sosai baba magajiya tai mamakinta, Sannan ta kwatanta mata ta tafi, Gidan dama ba boyayye bane a wajanta irin katan gidan nan ne da kowa da bangaransa, Da sallama ta shiga ta kwa ci saa duk suna tsakar gida, Wata kujera da ke gefe ta zauna tare da gaida su, Sannunki asabe wallahi baki da kirki da auren ki ya tashi ko ki aika mini in ma fishi kike da ni ni yanxu nazo neman yafiya, cikin rashin fahimta matan gidan da kuma asabe ke kallonsu " nifa baiwar Allah ban sanki ba, asabe ta fda cikin rashin fahimta " mutum sai bakin jinin jaraba a kasa masa talla amma baa siya wlh in nice mai kasa miki tallan nan na dena kasa miki" amma ai baki manta mai fda miki wannan maganganun ba koh" Nur ta fda tana kashe mata ido, " in kinga na manta da mai fdan wadan nan zancen tah tabbas zan mata da zan mutu asabe ta fda tana kallon nur " aikuwa rukayya (sunan asabe na gaskiya) kin manta kwa da zaki mutum dan kwa nur ce ni, ihu sosai asabe ta saki tana ruko nur yan gidan ma sakin baki sukai suna mamaki, dakin asabe suka nufa, sosai suka sha hira duk da mafi yawan maganar nur turanci ce yafiyar asabe ta nema sannan da zata tafi ta bata kyautar dubu goma, asabe sbda murna har kuka tayi, sukayi akan gobe da safe asabe zata xo gidan umma suje gidan ladidi sa sauran kawayensu, Tana barin gidan asabe ba inda ta wuce sai gidan kaka, Lkcin kaka na girkin abincin dare dan an kusa mangariba " kaka wai umma tace ki bata dadawar hamsin da goran ashirin, nur ta fda tana turo baki a gaban kaka Dariya kaka tayi " jairar banza iskancin da kika tina kenan, murmushi nur tayi tare da rungumo kaka ta baya, a nan suka zauna suka fara hirar yaushe gamo har akai ishai ta ci abinci taiyiwa kaka sallama Karon da nur taji tayi da mutum a sorone yasa kwala ihu Daga Shamsiyyqh & Haima ( mmn abul) [4/30, 5:31 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 141_145 Tsawar da taji an daka mata shi ya dawo da ita daga hayyacinta, ke! Bakya ganine kina buge mutane?, jin muryar Nura yasa ta danyi ajiyar zuciya, kokarin janye jikinta takeyi ya kankame ta ajikinsa, suna tsaye ahaka cikin soron, takun tafiya suka ji yayi saurin saketa. Ficewq tayi daga gidan, gidansu ta nufa, umma tana kwashe tuwo Nur ta shiga da sallama, ganin Nur yasa umma yin turus ke!,lfy kika dawo? Ina mijin naki?, turo baki Nur tayi tace yana gidan kaka, kan ta karasa magana tajiyo muryar abbanta, "maza ki kama hanya ki koma gun mijinki wannan ai sakarcin banxa ne, " haba abba nifa hutu nazo, hutun uwarki bace mun dagani cewar abban, da hanzari ta fice, tana tafiya tana hawaye. Sake karo tayi da mutum cikin hanzari ta dago jin kamshin turaren Nura ya tabbatar mata shine, toh ina zaije ta tambayi kanta, Kanwata ya ina kuma zaki?, " abbane yace sai dai naxo gunka mu kwana tare bayan nikuma hutu naxo, taso bashi dariya amma ya gimtse dariyar yace"kanwata toh meyasa bakice musu ni nace ki kwana can ba, na fada musu abba yace ban isa ba, wani dadi yaji rike hanunta yayi suka juya gidan kaka. Sai karfe goma Nur ta tashi daga inda suke hira ta nufi dakin kaka, ai kuwa kaka tayi maxa tace"maza fitomun zokibi mijinki dakin shi, turo baki tayi ta fara bubbuga kafa tana kunkuni ita ba inda xata, Nura kam ko ci kanki baice musu ba ya mike ma yayiwa kaka sai da safe ya tafi daki, kaka ma ta mike, tayi nata dakin, nur kuwa na tsaye abin duniya ya isheta, ta rssa nayi dankwalinta ta shimfida kan barandar inna ta kwanta, amma sam ta kasa bacci. Nura yana daki shiru shiru ba Nur ba alamunta, har bacci ya fara daukansa, mikewa yayi ya fito hango Nur yayi kwance akan baranda cikin hanzari ya karasa, Nur ya fada, bata tashi ba bare ta amsa, idonta arufe kamar me bacci, ya sake kiranta Nur, nan ma shiru sai daya sake kiranta akaro na uku sannan ta bude ido, ransa ya gama baci, cikin bacin rai yace" tashi mu tafi daki, ganin yanayinsa yasa ta mike ba musu, dakin ta shiga kan kujera ta xauna, anan ya taradda ita ya haye gado abinsa, bai kara bi ta kanta ba. Washegari tun kafin Nur ta tashi ya shirya yaje yayiwa su umma sallama ya bar garin, ransa duk a jagule. Nur lokacin data farka ta ganta kwance kan kujera, ta mike tayi salla sannan ta fita dakin kaka ta wuce taje ta gaidata, bata tambayeta Nura ba, itama kakan bata ce gashi ba haka tayi wanka ta nufi gidansu. Tun ransa nura yabar panisau bai kara waiwayar garin ba kimanin kwana ashirin da shida kenan, Nur kam duk tabi ta damu ta dena walwala kuma sam taki fadawa kowa halin datake ciki, haka abba yasa ta fara shirin komawa, tace ai sai yayanta yazo, nan abba ya rufe ta da fada akan maxa ta hada kayanta jibi xata bar gari. Hakan kuwa akayi ranar da xata tafi sai kuka takeyi, suna zaune da iyayen suna mata fada, driver yaxo daukarta, nan ta fito suka dau hanya. Direct gidan mummy aka wuce da ita, tarba kam tasha ta gun sirikanta. Muje zuwa kuyi hakuri ana zafi kuma bamu da wuta. By Shamsiyya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:32 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 146_150 Nur tana zaune falon mummy tana kallo Nura ya shigo da sallama, ta amsa mai juyawa yayi gun da take ya watsa mata harar yayi gaba abinsa, murmushi kawai tayi, dakin mummy ya nufa da sallama ya shiga, ina kwana mummy"lfy lau ya Aisha take, lfy lau tana gaisheki, mummykam tajine amma tasan sam Aisha bazata ce agaidata ba, nan suka tattauna abinda ya kawo shi sannan ya fito, daidai coridor suka hadu da Nur sannu kawai tace mai tayi dakin mummy, shiko ya kuma cika fam yayi waje. Tunda ga ranar Nur bata sake sa Nura a idonta ba, haka ko yaushe xaixo bata sani sai dai taji yaxo, sosai abun ke damunta amma bata da wata mafita data wuce hakuri. *bayan kwana biyar* Nur tana son tafiya taje ta zaga gari, dakin mummy taje ta zauna, tayi shiru mummy tace"lfy kuwa yar mummy kikayi shiru koda damuwane?, kai Nur ta dagawa Mummy, sannan tace mummy dama ina so nadan fita na zaga garine, murmushi mummy tayi tace yo banda abinki ai mijinki xaki tambaya, inya barki shi kenan, maza kirasa awaya. MiMikewa Nur tayi ta nufi dakinta, tagumi ta zuba, ta rasa ya zatayi tasan da kyar yayanta zai barta fitan nan, mika hanu tayi ta dauko wayarta akan bedsite, dialing number Nura tayi cikin sa'a kuwa ya shiga sai dai ba'a daga ba, ta kira kysan sau uku ba a dauka ba mayar da wayar tayi, can kusan minti talatin ta ji wayar na ruri, hanu takai ta dauko wayar, karawa tayi akunne tare dayin sallama. Hello yayana antashi lfy, lfy lau ya kuke yasu mummy"kowa lfy, yayana dan Allah inaso ne in dan fita xaga gari shine mummy tace na fada maka, shiru yayi yana wani nazari, har Nur tace hello yayana ko baka jina ne, gyaran murya yayi yace ina jinki, ba yau ba sai wani lokaci kawai ya katse wayar, bin wayar Nur tayi da kallo tana mamakin Yayan nata, toh meta mishi haka da zafi daxai sa ya tsane ta haka, haka ta wuni adaki jiki duk ba kwari, taki fadawa mummy gaskiya yadda sukayi. *3 weeks later* Nur ce durkushe sai sheka amai rake, cikin hanxari mummy ta taimaka mata ta gyarata suka nufi asibiti, a mota ma sai aman takeyi, waya mummy ta dauka ta bugawa Nura, a rude yace gani nan xuwa. Minti kusan talatin da isar su har anbasu gado Nura ya iso, gani mummy na safa da marwa yasa jikinsa yayi sanyi, ganin Nura yasa tayi gunsa da sauri, lfy mummy? Ya tambaya kwantae da hankalinka Nura xata warware laulayine, suna tsaye sai ga dr ya bukaci ganawa da mijin Nur cikin hanxari Nura ya bishi office. Gaskiya tana tsananin bukatar kulawa, kuma ya kamata ta rage yawan damuwa don karya haifar mata da ciwon hawan jini domin yanxy ma jininta ya fara hawa kasan mai ciki, dafe kai Nura yayi yana sauraron likitan nan, godiya ya mai sannan ya fita. Dakin da Nur take ya nufa, tana kwance tana bacci mummy na zaune kusa da gadon da Nur take, sosai tabashi tausayi guri ya nema ya zauna yana ta karanto addou i gareta. Ku kasance tare damu anjima . Allah ubangiji ka karawa sis na lfy, shamsiya abokiyar aikina(antyn abul), amin ya Allah. By Shamsiya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:32 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 146_150 Nur tana zaune falon mummy tana kallo Nura ya shigo da sallama, ta amsa mai juyawa yayi gun da take ya watsa mata harar yayi gaba abinsa, murmushi kawai tayi, dakin mummy ya nufa da sallama ya shiga, ina kwana mummy"lfy lau ya Aisha take, lfy lau tana gaisheki, mummykam tajine amma tasan sam Aisha bazata ce agaidata ba, nan suka tattauna abinda ya kawo shi sannan ya fito, daidai coridor suka hadu da Nur sannu kawai tace mai tayi dakin mummy, shiko ya kuma cika fam yayi waje. Tunda ga ranar Nur bata sake sa Nura a idonta ba, haka ko yaushe xaixo bata sani sai dai taji yaxo, sosai abun ke damunta amma bata da wata mafita data wuce hakuri. *bayan kwana biyar* Nur tana son tafiya taje ta zaga gari, dakin mummy taje ta zauna, tayi shiru mummy tace"lfy kuwa yar mummy kikayi shiru koda damuwane?, kai Nur ta dagawa Mummy, sannan tace mummy dama ina so nadan fita na zaga garine, murmushi mummy tayi tace yo banda abinki ai mijinki xaki tambaya, inya barki shi kenan, maza kirasa awaya. MiMikewa Nur tayi ta nufi dakinta, tagumi ta zuba, ta rasa ya zatayi tasan da kyar yayanta zai barta fitan nan, mika hanu tayi ta dauko wayarta akan bedsite, dialing number Nura tayi cikin sa'a kuwa ya shiga sai dai ba'a daga ba, ta kira kysan sau uku ba a dauka ba mayar da wayar tayi, can kusan minti talatin ta ji wayar na ruri, hanu takai ta dauko wayar, karawa tayi akunne tare dayin sallama. Hello yayana antashi lfy, lfy lau ya kuke yasu mummy"kowa lfy, yayana dan Allah inaso ne in dan fita xaga gari shine mummy tace na fada maka, shiru yayi yana wani nazari, har Nur tace hello yayana ko baka jina ne, gyaran murya yayi yace ina jinki, ba yau ba sai wani lokaci kawai ya katse wayar, bin wayar Nur tayi da kallo tana mamakin Yayan nata, toh meta mishi haka da zafi daxai sa ya tsane ta haka, haka ta wuni adaki jiki duk ba kwari, taki fadawa mummy gaskiya yadda sukayi. *3 weeks later* Nur ce durkushe sai sheka amai rake, cikin hanxari mummy ta taimaka mata ta gyarata suka nufi asibiti, a mota ma sai aman takeyi, waya mummy ta dauka ta bugawa Nura, a rude yace gani nan xuwa. Minti kusan talatin da isar su har anbasu gado Nura ya iso, gani mummy na safa da marwa yasa jikinsa yayi sanyi, ganin Nura yasa tayi gunsa da sauri, lfy mummy? Ya tambaya kwantae da hankalinka Nura xata warware laulayine, suna tsaye sai ga dr ya bukaci ganawa da mijin Nur cikin hanxari Nura ya bishi office. Gaskiya tana tsananin bukatar kulawa, kuma ya kamata ta rage yawan damuwa don karya haifar mata da ciwon hawan jini domin yanxy ma jininta ya fara hawa kasan mai ciki, dafe kai Nura yayi yana sauraron likitan nan, godiya ya mai sannan ya fita. Dakin da Nur take ya nufa, tana kwance tana bacci mummy na zaune kusa da gadon da Nur take, sosai tabashi tausayi guri ya nema ya zauna yana ta karanto addou i gareta. Ku kasance tare damu anjima . Allah ubangiji ka karawa sis na lfy, shamsiya abokiyar aikina(antyn abul), amin ya Allah. By Shamsiya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:32 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 155-160 Hannun nur nai yay motsi, cikin Sauri ya kai dubansa zuwa kallonta, A hankali ta fara bude idonta a kan fuskar nura ta sauke su, murmushi nura ya sakar mata, dauke fuskarta tai daga kallonsa, " sannu nur" mumy ta fda tana karasowa gadonta, mumy DA sauki nur ta fda fuskarta dauke da murmushi, Mumy ce ta taimakata taje toilet tai brush sannan ta dawo ta hada mata tea mai kauri bayan tasha ta musu sallama akan zata je gda ta dawo anjima Mumy na fita nura yay saurin zama gefenta akan gadon, kanwata ya jikin, nur ta dauke kanta daga inda yake, a hankali ya dora hanunsa akan nata, kanwata kimin magana mana ko naji sauki a raina, ba yadda nura baiyi da nur akan tai magana ba amma tai bnza dashi kamar bada ita yake ba, Jiki a sanyaye ya koma ya zauna akan kujerar dake gefen gadon a haka suka zauna bbu mai cewa wani a abu har mumy ta dawo Nura bai bar asibitin ba sai kusan goma na dare amma har lokacin bai samu kalma ko daya a bakin nur ba duk jikinsa a sanyaye ya tafi Washe gari karfe takwas nura ya nufi asibiti ko break fast baiyi ba, a hankali ya tura kofar dakin nur bata gadon sai mumy dake zaune gefen gadon " mumy ina kwana, " lpya lau, " ya mai jikin, jiki Alhamdulilah yayi sauki, yauwa daman ina san zuwa gida yanxu in nur ta fito kace na tafi, plssss ka kula da ita dan zan dan jima, " toh mumy Allah ya tsare, Amin mumy ta fda tana ficewa, A hankali ta turo kofar bandakin ta fito ganin nura a tsaye yasata hade ranta, har ta karaso gadon ta zauna, ko kallonsa ba tayi ba ta jawo mai tana shafa " kanwata kin tashi lpya, ya jikin naki, ko motsa baki batai ba bare ya sa ran zatayi magana tana gama shafawa ta kwanta akan gado tare da lumshe idonta, Tabbas ta san yayan nata ba santa yake ba kawai tausayi take bashi, dan tausayin tane yasa ya dakkota daga garinsu ya kawota nan, inkwa haka ne tabbas zuciyarta bata mata adalci ba da ta raya mata nura na santa duk a cikin zuciya nur ke tunani a hankali hawaye suka fara biyo idonta suna fita " kanwata me aka miki kike kuka dan Allah kiyi hakuri koh jikin naki ne, Gyada kanta tayi alamar a'a " kanwata dan Allah kiyi hakuri ki daina azabtar dani da yin shirunki, ki yafe mun laifin da na miki, tabbas nasan bn kyauta ba amma kiyi hakuri Allah yana tare da masu hakuri, Nur ya fda yana rike da hanunta, Ganin bazata kulashi ba yasa dole ya hakura ya kyaleta Kwanan nur biyu a asibiti aka sallameta amma har lkcin nura bai samu sauki wajan nur ba sosai yaji ba dadi daman haka masoyi yake ji in abar kaunarsa ya juya mashi baya, tabbas baiyima nur adalci ba " nura wai tinanin me kakeyi ne ka shiga motar mu tafi gda mana, mumy ta fda tana kallon nura Murmushi yay yace toh mumy sannan ya shiga ya jasu suka tafi gda Yau kwanan nur biyu daga sallamowa daga asibiti nura kullum nan gdan yake wuni amma ko kallo bai ishi nur ba Da sallama ya turo kofar ya shigo gidan, mumy ce a falon cikin shirin fita unguwa, " mumy ina kwana, lpya lau daman tin dazu nake jiranka zan fita ne kuma sai dare zan dawo dan Allah ka kula da ita, mumy ta fda tana ficewa Tana zaune akan gado tana dadadn na wayarta daga ita sai wata doguwar riga blue, sosai riga ke nuna yanayin dirintq, A hankali nura ya turo kofar ya shigo da sallama jin muryar nura yasata kin dagowa, ta amsa masa sallamar ciki ciki A hankali ya karaso inda take tare da zama a gefenta, " kanwata ya jikin naki, nura ya fda fuskarsa dauke da murmushi, " ai kasan bn warke ba da zaka tambayan ya jikin, nur ta fda tana murguda baki 😳 zaro ido nura yayi, " ni kike harara kanwata harda murguda baki, " eh din an murguda " haba kanwata me yasa kika tsane ni haka kinsan irin kunci da matsin da zan shiga in kina min hakan, ko so kike ki doran hawan jini, nur ya karashe maganar kamar zaiyi kuka "Ni da ka shareni tsawan lkci bance ka tsaneni ba sai kai, ba ka damu da halin da nake ciki ba baka damu da lpyata ko ta jaririn dake cikina ba ko baka sona ai naci albarkacin danka dake cikina amma kwata kwata ka juyan baya...... Kukan da yaci karfinta ne yasata kin karasa maganar Sosai jikin nura yakara sanyi janyota yayi jikinsa " kanwata kiyi hakuri wallahi batan rai kikayi shi yasa amma kinsan ina sanki kuma ko da yqushe da sanki nake kwana nake tashi kullum sanki kara shiga zuciyata yake kiyi hakuri kinji, Nura ya karashe maganar kamar zaiyi kuka, Na hakura yayana, kaima ka yafe mun nima na yafe miki kanwata, nura ya fda yana manna mata kiss a kumatunta *ngde sosai da adduanki sisterna, Allah ya raya mana abul bisa turbar musulunci amin summa amin* Daga alkalamin Shamsiyya salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:32 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 161-165 Nura ne ya taimaka mata sukayi girkin rana sunayi suna zabga soyayarsu, a haka ranar suka wuni da yamma suna zaune a dakin nur akan gado, " kanwata, nura ya fda yana kallonta, wlh ina bukatarki fah yanxu, dariya tayi, yayana ba gani ba, ganin nur bata gane mai yake nufi ba yasa shi matsawa kusa da ita ya fara kissn dinta ko ta ina, nan da nan suka fita hayyacinsu, ganin nura na neman wuce gona da iri yasa na janyo musu kofa nai waje, Kwanci tashi ba wuya wajan Allah nur an samu addmssn a b.u.k sun bata medcne, sosai ta maida hankalinta ga karatunta ba ta wasa kullum drivern mumy ke kaita ya dakkota a haka semester su ya fara ja Kwanci tashi ba wuya wajan Allah cikin nur ya fito sosai kuma ya shiga watan haihuwa ko yau ko gobe, nura kullum yana makale da nur kamar zaa kwace masa ita, tin cikin nur na da wata shida akayi bikin kannan nura auta da yayarta,babar aka kaita kaduna sai auta kuma da ta auri dan kanin mumy aka kaita katsina Aisha kuwa gaba daya ta mnta da wata nur dan ko zance nur basa yi a gdan da ita ce ke kokarin fda ma nura ina nur, ganin kamar ba yason zancenta yasa ta daina mashi Yau kwanan su nur biyu da gama jarabawar second semestern su sun tafi hutu wanda suna komawa zasu shiga level 2 sosai nur cikin yasa girma amma yayi mata kyau ta kara cika indai mutum ya ganta sai ta burgeshi Nur ce kwance a saman cinyar nura,mumy na gefensu suna kallon wani film a m.b.c drma, sosai nur ke jin dadin shirin, " mumy wai yaushe nur zata koma gda na ne, nura ya fda yana shafa kan nur " iyeeeee masu gda toh sai tayi arbain, da ko dan da kukasamu yayi wayau, " kai mumy dan Allah, kinsan yadda nake kewa.........karar da nur ta saki ne yasashi kin karasa maganar da yakeyi, " nura me ya sameki haihuwar ce, mumy ta fda a rude, ganin halin da yarta take ciki, daki ta nufa ta dakko key nura ya sata a kafada suka nufi asibiti, Cikin gagawa suka karbeta kasancewar asibitin na kudine, Mumy da nura sai zagaye suke suna jiran fitowarta Cikin mintunan da ba su wuce talatin ba nur ta zan kado kyawawan yayanta maza guda biyu Wata nurse ta fita fuskarta dauke da murmushi ta sami su mumy Congratulatn, an samu twince maza gaba daya, murna sosai mumy da nur sukai rafar dubu dubu nur ya bawa nurse din guda biyu, sosai tai murna Bayan angama gyarata ita da jariran aka sallamesu kasancewar lpyarta kalau " hello Alhaji nur ta haihu, daga daya ban garan aka ce " haba me aka samu, " yan biyu ne duka mata, sosai dady yay murna yace yqnxu zai kamo hanyar kano Suna isa gda mumy ta hada ma nur ruwan wanka sannan akayi mata, nura kwa na makale da twince dinsa Da kyar nura ya bada twince aka musu wanka, abba yayiwa waya da kaka ya fda musu nan da nan kaka ta fita tana fdawa makota, duk wanda yaji sai yayi mata murna, Yau kwanan nur biyu da haihuwa har lkcn nura bai fdawa Aisha ba, kaka ce tai sallama tare da turo kofar Aisha na zaune tana kallo, Ciki ciki ta amsa mata sallamar, ina nuran yake, ya nazo ganin mai jego naga gida ba kowa, Duuuum gaban Aisha ya fdi, wace kuma me jego, Aisha ta fda rai a face, Ke bansan bar badanci kina nufin kice kuna zaune gda daya da nur baki san ta haihu ba, kaka ta fda rai a bace Cikin tashin hankali Aisha ta mike dan kwata kwata ta manta da wata nur, wace nur din ce ta haihu Aisha ta fda, Kan kaka tai magana nura ya fito daga daki A'A kaka sai yau zaki zo ai angwayan naki sunyi fishi dake ace sai da suka kwana 2 kika kazo, bari kawai wannan salamiyar matar taka batasan nur ta haihuba suna gda daya " kaka ai nur tin da ta sami ciki mumy da dady suka kwace min ita, ba irin fishin da bnyi ba amma suka hanani ita, tana gdan mumy mu tafi, nura ya fda ba tare da ya kalli Aisha ba Mutuwar tsaye Aisha tayi tabbas zuciyarta ta yaudareta da ta fda mata nura ya saki nur gashi har ta haihu kuma in ta fahimci zanjen yan biyu ta haifa kuma maza, Kamar mahaukaciya Aisha ta shiga daki ta dau key din mota tai gidan mumyn ta Ku kasance da mu anjima dan jin yadda zaa kaya tsakanin Aisha da nur By Shamsiyyah salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:32 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 166_170 Bankada kofar dakin tayi ta shiga bako sallama mummy! Mummy!! Mummy tana ta kwalawavmummyn kira cikin hanxari mummyn Aisha ta fito ta tarbi yar tata, lfy dai Aisha, ina fa lfy mummy Nur tana gidan mymmynsu Nura ashe bai saketa ba har ta haihu yan biyu duka maza, sallami Mummy ta shuga yi, ke da wasa kike ko da gaske? Haba mummy da gaske nake nima bai fadan ba yanxu kaka tazo daga kauye gunta nakejun lbrn. Zaunar da yar tata tayi kan kujera tace tirka shi toh au bamuci ta zama ba dole mu mike mu samu mafita, Aisha ta dybi mumynta tace mumy na shiga uku ki taima keni pls, kwantar da hankalinku yata xan share hawayanki gidan Nur tamkar Nur ta barshi ne, mikewa tayi taje daki ta dauko gyalenta ta dawo tashi muje. Gurin wani shahararren boka suka je nan suka fara xayyana masa dalilin zuwansu nan boka ya tuntsire da dariya, ya dubesu yace angama amma akwai sharadi ita yartaki sai taxo na sadu da ita na kwana bakwai wa'uya zubilla cikin hanxari Aisha tace na aminve indai bukata ta xata biya na rayu da Nura ni kadai, dariyar mugunta boka ya dinga yi, nan ya umarci Aisha data shiga dakin dake yamma dasu, haka uwar tana kallo amma ta kasa komai saboda son xuciya waiyaxubillah. Haka ta kasance tsakanin boka da aisha har tsawon kwana bakwai, nura sam bai ma san tana fita ba tunda ya tare gidan mumy, anyi suna naganu na fada domin yara suncu sunan kakaninsu daddy da abban nur amma ana kiransu da *Aslam* da *Ashraf*, sosai yara da uwarsu sunga gata domin sun san su yan dangine, daddy ya musu kyautar filaye da kudi miliyan daidai a cikin acc dinsu, shagali kam anyi, ranar suna gida ya cika ya batse yan panisau ma ba'a barsu a baya ba domin sunxo kuma sunyi rawar gani. *2 week later* Nur da yaranta suna cikin kawar mummy da dady da kuma uban gayya domin ya daina komawa gida ma, suma iyayen ganin irin rashin arzikin Aisha tasa sukayi burus da ita, haka suka kasance suna tarairayar surukarsu ta mutunci da jikokinsu. Wata ranar talata Nura ya fito sanye cikin suirt baki sunyi bala'in masa kyau yana ta kamshi, Nur ta dubeshi tana murmushi tace yayana sai ina kayi kyau fa sosai, ya janyo ta jikinsa yace gun auntynki xani, tuni Nur ta bata fuska tana kokarin xamewa, haba kanwata me nayi kuma kodan nace xani gun auntyki toh kwantar da hankalinki na fasa, Tayi murmushi tace 'a a yayana kaje kar Allah ya kamaka da laifin rashin adalci, ya sumbaci goshinta yace kin amunce, tace eh yayana ya jen ya sumbaci yaransa da suke bacci ya fita. Tunda Nura ya fita yau kusan kwana biyar bashi ba labarinsa wayoyinsa duka akashe, har su mummy hankalinsu ya matukar tashi, Nur kam duk ta wani susuce daddy na zaune rike da ashraf mummy tana daki, Nur ta fito ta gaida daddy tace daddy ansamu labarinsa kuwa, 'aa kawai yace daki nur ta koma cikin hanxari ta dauko mayafinta ta nufi kofar fita, Nur ina xaki daddy ya tambaya"gidanmu xanje na duba ko yana can tunda ranar yace gun Aunty aisha xashi, bata jira mai xaice ba tayi waje. Tana shiga gidan taga motarsa da sauri ta karasa bude kofar falon tayi ba tare da sallama ba, amma abinda tagani ya matukar bata mamaki, ta kumayi dana sanin zuwanta, Nura ta gani da Aisha suna tsakiya da shaaninsu na ma'aurata taja ta jingina da jikin bango saboda jirin dake dibarta innalillahi kawai take ambata. Aisha tagani akanta tana mata dariyar mugunta, malama lfy zaki shigo mun gida bako saklama?, " cikin bacin rai Nur ta dau hanu ta wanke aisha da mari, zata kara mata itama taji an mareta, ganin Nura ne yasa ta budewa idonta toka ta fara zaxzagamai bala'i, ke wacw irun jaka ce karya, kin biyoni nan in miki meye?toh kafin na bude idona ki bace mun dagani cike da mamaki Nur ta ke kwllon Nura, haka taja jiki asabule ta juuya. Muje zuwa xakujimu myna nan tarw daku By Shamsiya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:35 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 166_170 Bankada kofar dakin tayi ta shiga bako sallama mummy! Mummy!! Mummy tana ta kwalawavmummyn kira cikin hanxari mummyn Aisha ta fito ta tarbi yar tata, lfy dai Aisha, ina fa lfy mummy Nur tana gidan mymmynsu Nura ashe bai saketa ba har ta haihu yan biyu duka maza, sallami Mummy ta shuga yi, ke da wasa kike ko da gaske? Haba mummy da gaske nake nima bai fadan ba yanxu kaka tazo daga kauye gunta nakejun lbrn. Zaunar da yar tata tayi kan kujera tace tirka shi toh au bamuci ta zama ba dole mu mike mu samu mafita, Aisha ta dybi mumynta tace mumy na shiga uku ki taima keni pls, kwantar da hankalinku yata xan share hawayanki gidan Nur tamkar Nur ta barshi ne, mikewa tayi taje daki ta dauko gyalenta ta dawo tashi muje. Gurin wani shahararren boka suka je nan suka fara xayyana masa dalilin zuwansu nan boka ya tuntsire da dariya, ya dubesu yace angama amma akwai sharadi ita yartaki sai taxo na sadu da ita na kwana bakwai wa'uya zubilla cikin hanxari Aisha tace na aminve indai bukata ta xata biya na rayu da Nura ni kadai, dariyar mugunta boka ya dinga yi, nan ya umarci Aisha data shiga dakin dake yamma dasu, haka uwar tana kallo amma ta kasa komai saboda son xuciya waiyaxubillah. Haka ta kasance tsakanin boka da aisha har tsawon kwana bakwai, nura sam bai ma san tana fita ba tunda ya tare gidan mumy, anyi suna naganu na fada domin yara suncu sunan kakaninsu daddy da abban nur amma ana kiransu da *Aslam* da *Ashraf*, sosai yara da uwarsu sunga gata domin sun san su yan dangine, daddy ya musu kyautar filaye da kudi miliyan daidai a cikin acc dinsu, shagali kam anyi, ranar suna gida ya cika ya batse yan panisau ma ba'a barsu a baya ba domin sunxo kuma sunyi rawar gani. *2 week later* Nur da yaranta suna cikin kawar mummy da dady da kuma uban gayya domin ya daina komawa gida ma, suma iyayen ganin irin rashin arzikin Aisha tasa sukayi burus da ita, haka suka kasance suna tarairayar surukarsu ta mutunci da jikokinsu. Wata ranar talata Nura ya fito sanye cikin suirt baki sunyi bala'in masa kyau yana ta kamshi, Nur ta dubeshi tana murmushi tace yayana sai ina kayi kyau fa sosai, ya janyo ta jikinsa yace gun auntynki xani, tuni Nur ta bata fuska tana kokarin xamewa, haba kanwata me nayi kuma kodan nace xani gun auntyki toh kwantar da hankalinki na fasa, Tayi murmushi tace 'a a yayana kaje kar Allah ya kamaka da laifin rashin adalci, ya sumbaci goshinta yace kin amunce, tace eh yayana ya jen ya sumbaci yaransa da suke bacci ya fita. Tunda Nura ya fita yau kusan kwana biyar bashi ba labarinsa wayoyinsa duka akashe, har su mummy hankalinsu ya matukar tashi, Nur kam duk ta wani susuce daddy na zaune rike da ashraf mummy tana daki, Nur ta fito ta gaida daddy tace daddy ansamu labarinsa kuwa, 'aa kawai yace daki nur ta koma cikin hanxari ta dauko mayafinta ta nufi kofar fita, Nur ina xaki daddy ya tambaya"gidanmu xanje na duba ko yana can tunda ranar yace gun Aunty aisha xashi, bata jira mai xaice ba tayi waje. Tana shiga gidan taga motarsa da sauri ta karasa bude kofar falon tayi ba tare da sallama ba, amma abinda tagani ya matukar bata mamaki, ta kumayi dana sanin zuwanta, Nura ta gani da Aisha suna tsakiya da shaaninsu na ma'aurata taja ta jingina da jikin bango saboda jirin dake dibarta innalillahi kawai take ambata. Aisha tagani akanta tana mata dariyar mugunta, malama lfy zaki shigo mun gida bako saklama?, " cikin bacin rai Nur ta dau hanu ta wanke aisha da mari, zata kara mata itama taji an mareta, ganin Nura ne yasa ta budewa idonta toka ta fara zaxzagamai bala'i, ke wacw irun jaka ce karya, kin biyoni nan in miki meye?toh kafin na bude idona ki bace mun dagani cike da mamaki Nur ta ke kwllon Nura, haka taja jiki asabule ta juuya. Muje zuwa xakujimu myna nan tarw daku By Shamsiya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:35 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 171-175 Cikin tashin hankali nur ta fita batasan inda take sa kafarta ba da taimakon Allah ta karasa gda, Yanayin da su dady suka ganta ba karamin daga musu hankali yayi ba, cikin tashin hankali mumy ta rukota nur me ya faru, da kyar nur ta basu lbri tana kuka, Inalilahi waina ilaihir rajiun, abinda mumy da dady ke yi kenan a bakinsu har suka samu nutsuwa, tabbas ko shakka bbu akwai abinda ke damun dan su amma ba yadda za ai suce ga takamai man abinda ya sameshi, da kyar mumy ta rarashi nur tayi shiru Abu kamar wasa nura yau kwanan sa goma rabansa da gidan mumy, kuma ya kashe wayoyin sa gaba daya, Nur kuwa duk ta rame dan gaba daya ta fita hayyacinta, ko abinci bata ci sosai, " hajiya ki shirya ke da nur din muje gdan sa mu ga mu kuma da me zai kar be mu, ba musu suka shirya suka tafi, Da sallama suka shiga falon, nura da Aisha na zaune ana ta faman shan soyayya Mtswwwwww aikin banza kawai baza a taba barin mutum ya sake da iyalansa ba banda abin kunya ina na taba jin uban miji yazo gdan dansa Aisha ta fda cikin bacin rai, " yanxu nura kana kallon abinda matarka kema mahaifinka kayi mata shiru, mumy ta fda cikin tashin hankali, " toh mumy me Zan mata Ku fa kuka zo inda take ai gaskiya ta fda " na Shiga uku na haifi da wata ta dinga juya minshi wallahi Aisha baki isaba Allah ya fiki, mumy ta fda tana kuka Dady kan waje yayi dan tabbas yanxu ya tabbatar asiri ke dawainiya da dan nasa kuma insha Allahu zai yi iya kokarinsa dan nemawa dan nasa lpya wajan Allah " kinga malama ki fice min daga gida sai ki tafi can ki karata da kukan ki, kar ki dagan hankali, Aisha ta fda tana nuna mumy da yatsa, nur wadda tin da sukazo bata ce komai ba ta matso kusa da mumy tare da rike hanunta, dan su fita " banxaye kawai, kuma wallahi kuka kara shigo min gida sai kunyi da kun sanin zuwa gda na, ganin Aisha na zaginsu yasa nur juyowa cikin bacin rai " ke dan ubanki ki gyara zancenki mu din ba saaninki bane bnza jahila kawai ni tinda nake ma na taba ganin jahilin mutum kamar ke, nur ta fda rai a bace Cikin bacin rqi Aisha ta dago hannu zata mareta, nur ta rike hanun ta wanka mata kyawaean mari guda biyu, Ganin nur ta mari Aisha yasa nura ya maso kusa da ita yana huci kamar namijin zaki, ya daga hanun zai mareta ta kauce " zan maka uxiri daya ba a hayyacin ka kake ba amma wallahi da sai na gwabza muku rashin mutunci da ga kai har matar taka, nur ta fda cikin masifa, hanun mumy taja sukai waje Tin daga ranar gaba daya suka dukufa yiwa nura addua, sannan kusa sa ana mashi, sanda nur tai arba'in taje panisau tayi sati daya sannan ta dawo gda " sosai ta maida hankalinta ga karatunta dan sun koma twince kwa anyi wayau sosai, kamaninsu sak da mahaifin su, Tin da boka ya sadu da Aisha shaidan ya kwawata mata boka gani take duk duniya yafi kowa sarrafa mace, hakan yasa wata rana taje ta sameshi " hajiya kina da wata bukatarne dan nasan waccan bukatar ta biya, " eh boka bukatata ta biya amma ina so na zamar maka tamkar mata dan sosai naji dadin muamala da kai, " kar ki damu zan fi kowa san hakan dan ke din ta musammance nima kaina bntaba haduwa da wata mace da naji dadin harka da ita ba kamarke, tin daga ranar boka ya zama abokin alfashan Aisha Kwanci tashi ba wuya wajan Allah yau shekarar twince daya da haihuwa har lokacin nura bai waigesu ba, sosai sukai wayau ga baki suna tafiya ga kuma hakora, yaran abin shaawa duk wanda ya gansu sai sun bashi shaawa Da daddare suna falo suna hira dady ya kalli mumy yace " na karbo rubutun wajan malam na kadage a jaba yace indai na bashi rubutun ya sha sau uku da safe da rana da daddare ba zaiyi kwana ukuba asirin bai karye ba amma fa sai mun dage da addua a daran yau, Nur kema ki mashi, yaushe zaku gama exam din, saura kwana uku insha Allahu daddy Inyeee kice yar gatan mumy an kusa shiga level 3, insha Allahu dady, Allah yasa gaba daya suka amsa da amin sannan sukaje sukai nufin kwanciya dan karfe daya zasu tashi suyi sallah dan nemawa nura sauki wajan Allah Allah ka yaye mana duk wata damuwa dake damun mu, ina miko gaisuwa ga son dina sister haima a masa kisss hudu a kumatu By shamsiyya salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:35 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) 31-35 Yau sati biyu nura bai je panisau sbda kar Aisha tai zargin wani abun yasa bays zuwa, yana kwance akan doguwar kujera idonsa a lumshe kamar mai bacci amma kuma ba bacci yake ba, tinanin nur kawai yake, kullum da ita yake kwana kuma da ita yake tashi bashi da wani tinani in ba nata ba, " honey, honey, Aisha ta fada tana tabashi, kamar bazai bude idonsa ba kuma sai ya bude a hankali, sweat heart ya akayi, ina bacci kina tashina koh ya fda cikin shagwaba, " kayi hakuri honey ko zamuje kaje kaga likitane dan naga kwanan kamar baka da lafiya, " sweat heart lpya ta kalau, nura ya fada yana yana mikewa daga kan kujerar, " yauwa honey daman hajiya ce tamin waya wai zamu tafi abuja zamuyi sati daya, maganar ba karamin batawa nura rai tayi ba abinda ya tsana kenan na halin mumyn su Aisha kawai saidai taima yayanta waya suxo suyi tafiya, Aisha ce ta katse masa tinaninsa, honey yanaji kayi shiru ba komai amma bn yarda da tafiyar nan ba amma fah in na isa, ya fda yana shigewa daki, Da daddare nura na kwance a daki, shawara ta fado masa akan ya bar Aisha ta tafi shi kuma yay anfani da wannan damar yaje ya kara sabawa da nur tare da iyayenta, murmushin jin dadi yayi tare da mikewa yay falo, ganin tana zaune tana sharar hawaye yasa ya zauna kusa da ita sweat heart me aka miki kike kuka, haba honey kasan dai mumy kuma idan ka hanani zuwa Allah zata iya cewa na taho, ni kuma bazan so na tafi ba tare da ixininka ba, ajiyar zuciya ya sauke, ya isa sweat heart kije ki hada kayanki ku tafi amma fah nima bazan iya zama gidan nan baki nan gidan kaka Zan tafi na gwadayin sati koh zan iya, toh honey a gaida kakan Tin safe nura ya sauke Aisha gidansu, ya kama hanyar panisau, cikin mintinan da ba su wuce 40 ba nura ya isa garin panisau da sallama ya isa gidan kaka bata nan, ganin bata nan ya taxi fada ko zai hadu da zabin ransa, haka ya gama zagayansa a fada amma bata nan *kofa* yaje ganin yana ta zagaye bbu ita bbu dalilinta, yasa ya tafi gidan kaka jikinsa a sabule, Sanda yaje gidan kaka bata dawo ba, kusan mintinsa biyar ya gaji ya tashi da nufin yaje ya tambayi gidan su nur, har yazo zaure ya hadu da kaka tana shigowa, a' a nura kaine a gidan, " eh kaka nine amma kuma kin fiye yawo, waya fadama yawo nakeyi, lkcn ne suka karasa cikin daki, " kaka ina kikaje na kusa awa a garin nan ba kya nan, bari kawai nura wallahi nur ce ...... Kaka mai ya sameta nura ya tambaya cikin tashin hankali, wallahi yau kuaan satin ta daya bata fita toh yau jikin nata yayi tsanani sosai yanxu ma wani magani zanje karbo mata a gidan wani wanxami...... Kaka wani irin wanzami kuma baku kaita asibiti ba, aa ba a kaita ba a gida ake mata magani, Kaka tashi ki rakani gidan muje naga jikinta, Toh amma ka jirani tukunna bari na dawo ba yadda nura baiyi yabi kaka ba amma taki Sanda ta isa gidan wanxamin ta karbo mata magani sannan ta wuce gidan su nur dan kwata kwata hankalinta baya jikinta tana shan tinanin matsanancin halin da ta bar nur a ciki Ganin kusan minti 30 da tafiyar kaka kuma bata dawo ba yasa hankalinsa yaki kwanciya ya fito dan yay tambaya ko za a kaishi gidan su nur din By Shamsiyya salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:35 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 41_45 *1 *week* *later* Nura yana ta shirin komawa kano, zuwa wannan lokaci ya saba da Nur sosai, yana tsaye jikin motarsa Nur ta fito daga gida, tayi haske ta rame sosai ahankali take tafiyar kamar bazata taka kasa ba, da sallama ta isa gurin motar, "yayana kardai har ka shirya? Ta tambaya tana rausayar dakai, sosai ta burge shi domin tana da sexy eyes, ya bude baki yace" kanwata karki damu xan dinga xuwa kowani karshen sati ina dubaki, kai kawai ta daga mai sannan sukayi sallama ya tafi. Tunda Nura ya bar garin Nur ta sake dawowa gidan jiya, kazanta sai abinda ya karu domin tama daina wanka, wata ranar laraba Nur ta dawo daga tallan gyada, tana dire tiren ta shige bayan gida, tana fitowa ba wanke hanu ta dauko abinci ta fara ci. Ke baki da hankaline zakici abinci da hanunki baki wanke ba kin fito bayi umma ke magana, Nur ta turo baki tace"haba umma wani wanke hanu xanyi bayan bada hanun zanci ba, a zuciye umma ta biyota aikuwa maza Nur ta mike tayi haryar fita, sai dataga umma ta koma sannan taxo tadau abincin tayi xaure acan ta karasa ci. Yau jumaa yaune Nura xaixo amma aranar zai koma kasancewar Aisha ba lafiya tunda ta dawo daga tafiya, yanata shiri Aisha dake kwance kan gado tayi wuf ta mike tace, Honey ina xuwa haka? bayan kasan bani da lfy, ya dubeta sannan ya dauke kai batare dayace mata komai ba yace panisau zani.ta murtuke fuska wlh sai dai muje tare, da sauri ya juyo yace ina?" Tace gun kakar yace ina ai yau xandawo dan haka kawai ki zauna, tace gaskiya bazan xauna ba.ficewa yayi zuwa dakinsa ya barta tsaye bakin gado. Nura yana tsaye afalo yana tunanin yadda zaiyi da Aisha can dai dabara ta fado mai ya nufi dakin nata, a kan bedsite yasameta ta zuba uban tagumi yacire hannun ta dago ta kallesa sannan yace ki shirya muje, tsabar murna bata san sanda ta rungumeshi ba, ya rada mata akunne amma fa sai sunday zamu dawo, ta daga mai kai sannan ta zare jikinta ta fada toilet. Basu fi mintina talatin ba suka isa panisau, isar su keda wuya ko gidan kaka basu isa ba, Nur ya hango suna gada, ganin tare suke da Aisha karta xargi wani abu yasa ya canja hanya, ashe Nur ta hango motarsa, taga kuma ya juya ta kumbura suntum tiran tallan ta dauka tayi gida. Kudin kawai ta mikawa ummanta ta wuce daki, batayiwa kowa magana ba, gadon ummanta ta hau ta kwanta sai bacci. Misalin karfe hudu da rabi na yamma Nura yaceawa kaka xashi gidansu Nur, ya fito lokacin Aisha tana tsakar gida yace mata xaije gidan abokinsa tace adawo lfy, ya fice da sallama ya shiga gidansu Nur, ummace kadai azaune tana tankade garin tuwo, kujera yar tsuguno ya dauko ya zauna, ya gaishe da umma cike da ladabi, baba bayanannane, wlh ya fita amma ya kusa dawowa. Umma taje ta kawo mai ruwa yasha yana ajiye kwanan shan yajiyo sallamar baba, ya amsa sanman ya karbi ledar ya kai kusa da umma, sosai suka gaisa da baba, "ina Nur ne ko taje miki aikane?baba ya tambaya nan umma ta fadamai yadda akayi, dakin umman ya nufa yana shiga ya ganta zaune bakin gado, karasawa yayi ya zauna yace yar baba lfy?tace abba sannu da dawowa ba komai, toh taso muje ga yayanki can yaxo ta nuke kafada abba baxani ba ai tun xuwansa na hango motarsa daya ganni sai ya juya da motarsa shine yanxu xaixo.dariya tabawa baban nata dakyar yasamu ta fito. Muje xuwa in munyi caji domin wayata ba caji yanxu By shamsiya salis & Haima(mmn abul) [4/30, 5:35 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 181-185 " mumy naga kinyi murmushi, " toh nura me kake so na maka, " mumy kina ganin nur zata gafarta min abinda na mata, me zai hana, kaje ka gwada ka gani mana, kamar jira yake ya mike yay dakinta, Jin alamar ruwa a bandaki ya tabbatar masa da bata fito daga wanka ba " a bakin gadon ya zauna yana jiran fitowarta, baifi minti goma da zama ba nur ta fito daure da towel iya gwiwarta, ganin nura a dakin yasata tai kicin kicin kamar bata taba dariya ba, Ko kallonsa bata kara yi ba tai gaban mudubi dan ta shirya, a hankali ya taso yazo inda take gaban sa na dukan uku uku " kanwata" nura ya fda lkcn da yazo gab da ita, ko dagowa batayi ba bare yasa ran zata amsa " tabbas na kasance mai laifi a wajanki, amma bazan gaza wajan baki hakuri ba, kiyi hakuri ki yafemun,kanwata wallahi bnda bakin baki hakuri dan tabbas na cutar dake keda yayana, idan baki yafen ba bazan taba samun nutsuwa,ki taimakawa rayu....... Harar da nur ta watsa mashi ya sashi kin karasa maganar da zaiyi, " kaga malam ka tashi ka fita zansa kaya hanxu ai bani na biyoka ba bare ka kirani da karya, nur ta fda tana nuna mashi kofa alamar yay waje, jikinsa a sabule yqy waje Mumy bata falon hakqn yasa shi kwanciya akqn doguwar kujerq yana sharar kwallah Mumy ce ta fito rike da hannun twince zasu fita unguwa, " mumy yanxu wai zaku tafi nur ta fda tana fitowa daga daki, " eh dota so nake mu dawo da wuri, Mummy unguwa zasu, nura ya fda yana tashi daga kwanciyar yake, karar kofar da yadda aka turo kofar yasa mumy kin bada amsa gaba daya suka mai da duban su ga Wadda ke shigowa " sbda tsabar ka mai dani yar iska ina tambayarka ina zaka shine zaka share ni koh, najika shiru baka dawo ba driver yace nan ka taho toh da izinin wa ka fito, Aisha ta fda tana huci fuskarta a murtuke, shidai nura mamaki ya hanashi cewa komai daman haka take mashi kamarshi Aisha ta zauna tana juyawa lalai zai koya mata hankali zabin da take ta zabgawa na rashin mutunci ne ya katse mashi tunaninsa, " ke dallah malama ki fice mana daga gda kafin ranki ya baci banza jaka dabba, banda ke jahilace kyazo ki sami saar uwarki kice zakina fda mata magana, ai koh bata haifeki ba kya mutunta ta dan dan da ta haifo kika aureshi, nur ta fda cikin matsifa " ni zaki fdawa magana mara dadi Aisha ta fda zata mareta, gam nura ya rike mata hannu, kyawawan mari yayi mata guda hudu a fuskarta, ke dan iskanci nur din zaki mara, sbda baki da mutunci uwata zaki nama rashin kunya, toh kije na sake ki saki biyu dan uwarki, kuma wallahi idan kika kuskura na dawo na sami ko tsinke naki a cikin gdana sai ranki yayi mumunan baci kuma kin rasa komai, dan dai ba a so ai saki uku a take da ba abinda zai hanani yimiki ukun kije ki auri fasikin bokan ki banza karya me bin maza, Aisha da tai mutuwar tsaye tin da ya saketa ta fara kuka, " mumy dan Allah ki bashi hakuri wallahi Allah ina sanshi sosai, Mtswwwwwww, tsaki mumy tayi taja twince dinta tai waje, kuka sosai Aisha takeyi a gaban nura, ita kwa nur na zaune Akan kujera tana chrtn " nur Dan Allah ki bashi hakuri, Aisha ta fda tana rike kafar nur, bugemata hannu tayi, dallah malama daina tabani da kazamtacen hanunki Ganin nura bashi da niyyar hakura yasa ta ficewa tana rusa kuka kamar mahaukaciya " kanwata kuna da tea a kitchen yinwa nake ji,zaka iya zuwa ka duba nikan bn sani ba nur ta fda batare da ta kalleshi ba jiki a sanyaye ya hado tea dan kadan yasha Daga taskar yan mutan Kano da jos [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 186-190 Yau kwanan nura uku da dawowa gda amma har lkcn nur bata kula sosai ya shiga damuwar haka, Da daddare nur da mumy na hira, nur tace, mumy ina san zuwa panisau gobe, je ki fdawa mijinki shi ke da ikon barinki ba ni ba, " mumy dan Allah ki barni ba sai na tambayeshi ba sbda naga da kina barina, nur ta fda cikin shagwaba, " lalai kan baki shirya zuwa panisau ba da kin shirya zuwa da kinje kin tambaya, ba yadda ta iya dole ta nufi dakinshi tana turo baki, Yana kwance akan gadonsa ya lumshe idonsa kamar me bacci, a hankali ta turo kofar tare da shigowa, da sallama ta shiga tare da zama a gefen gadon, " yayana, nu ta fda tana kallonsa, sosai ya bata tausayi Dan kana ganinsa zaka San yana cikin damuwa sbda yadda ya rame, A hankali ya bude runanun idonsa da sukayi ja sbda kuka har wani kumbura sukai, ga wani azababab ciwon kai da yake damunsa, " kanwata" ya fda da dashashiyar muryarsa, " mumy tace nazo na tambayeka zani panisau gobe, shiru kawai yayi mata ya bita da kallo, " yayana magana fah nake ma, " nur kije Allah ya kaimu goben, " Ameen" nur fa fda tana mikewa, Hanunta ya ruko cak ta tsaya amma bata juyo ba a hankali ya taso da kyar ganin jiri na dibarsa zai fdi yasa nur zaunar dashi, itama ta zauna, " nur ki duba girman Allah ki yafe mun, ki tina Allah ma muna masa laifi in munemi yafiya ya yafe mna bare kuma a tsakanin mu, kin dai san haka kawai bazan wulakanta ki ba aikin asiri, kuma kinsan asiri bbu wanda yafi karfin ya kama, toh ni meye laifina abinda na aikatashi ba a cikin hayyaci na ba, nur ki tina ku kuka dage da addua da karbar mun magani har na samu sauki, na sami sauki yanxu maimakon ki yafen muka rayuwarmu kamar da sai kuma ki juyan baya, da me zanji, bakin cikin da Aisha ta sani a ciki ko kuma azabar da kike min wadda zuciyata baza ta iya dauka ba,😭😭 nur ya karashe maganar cikin kuka Nur wadda tinda nura ya fara magana jikinta yay sanyi a hankli ta matsa kusa dashi tana share masa hawaye, " yayana kayi hakuri ka yafe mun bazan karaba" ta fda cikin shagwaba, na yafe miki Nima ki yafen na yafema, ta fda tana rungumeshi, Lumshe idonsa yayi, a hankali ta fara kisssing din sa, a take ya fara maida mata martani nan da nan suka bar hayyacinsu, ni dai auntyn abul dauko shi nayi nai waje na rufo musu kofa A dakin nura ta kwana sai da asuba ta koma daki ko wannen su fuskarsa dauke da murmushi, Wanka tayi sannan ta fara gyaran daki kamar yadda ta saba karfe bakwai ta gama komai ta ciga kitchen dan dora girki, Jitai an rike mata kugu da sauri ta juyo sbda tsoro, ido daya ya manne mata, murmushi tayi masa " ina kwana yayana" " lpya lau kanwata, shi ya taimaka mata sukayi girki sunayi suna shan soyayyarsu, Karfe tara dai dai suka gama shirya komai a dining, Nur ce ta taimaka mashi yayi wanka, sannan itama tayi wanka, A tare sukai break fast, bayan sun gama break fast nura yaje aka rage mashi suma, sosai nura yay kyau, Karfe hudu suka fara shirin tafiya, doguwar riga pink ta saka tai roln da blue din gyale sai blue din jaka da takalmi, wayyo zokuga yadda nur tayi kyau kamar a saceta, sanda ta fito nura na mota na jiranta, mumy tayi ma sallama ta ruko hannun twince suka fito, tinda nur ta fito nura ya kafeta da idanunsa had suka karaso ajiyar zuciya ya sauke sanda ta hura masa iska a idonsa Tina nin me kake yayana," ba komai. Kanwata kawai kinyi min kyaune nagode ta fda tana shiga motar yaja suka taxi By shamsiyyah & Haima (mmn abul) [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 191-195 Sanda su nura suka isa panisau gdan su umma suka fara sauka sosai umma da Abba suka ji dadin ganin su kuma ko da yaushe suna wa Allah godia da wannan hadin tabbas wannan shi ake kira *HADIN ALLAH* Basu bar gdan umma ba sai laasar a gdan kaka suka kwana, kwanansu biyu suka koma gda, *********************************** Tinda Aysher ta fita daga gdan mumy a hargitse, gudu take sosai a titi ita kanta bata San inda take saka kafarta ba da temakon Allah ta karasa gda, kuka kan ta shashi kamar ranta zai fita, Sai da Aysher ta kusan sati tana jinya har ta hakura ta fauwalawa Allah komai tai ta faman istigifari Kwanci tashi ba wuya wajan Allah su haneefah ana level 4 saura shekara daya ta gare mata ta gama b.u.k twince kuma na wajan mumy tin da aka yaye su basu komo ba, har lkcn nur bata kara samun wani cikin ba, soyayya suke mai tsafta tsakaninsu " yayana wai me na maka ne tin dazu fa nake kiranka amma kaki ko dago kai ka kalleni sai faman danna laptop kake, Aisha ta fda tana tsugunnawa gaban nura, Dago kansa yay ya kalleta, sannan ya cigaba da danna laptop dinsa, cikin fushi nur ta dauke laptop din ta dora a gado, " wai nur me yasa zaki dame ni ne aiki fa nakeyi, nura ya fda fuska a tamke, " wallahi yaya bazan bar ka ba sai ka fdan me nayi maka, haka kawai sai ka hau fishi da ni, nur ta fda tana mikewa Janyota nura yayi ta fdo Kansa so kike kiji me kika min, nura ya fda yana shafata, daga masa kai tayi alamar eh " suna nake so ki canza min bana son yayana din nan, amma kinki chanja min, nura ya fda a shagwabe, Hmmmmm murmushi nur tayi kar ka damu yayana daga yau ka zama prince, 😳 zaro ido nura yayi, " da gaske kike princess, daga mashi kai tayi, sosai yaji dadin sunan, nan danan ya rungumeta sosai a jikinsa ya fara kissing dinta ta ko ina,hannunsa ya zura cikin rigarta ya fara yawo dasu a ciki, ganin suna neman fita a hayyacinsu yasa na fita na janyo musu kofar "A gurguje ta shiga wanka sbda lattin da tayi yau a makaranta gashi malamin da suke dashi bashi da kirki, A falo ta tadda nura yana break fast, prince ina kwana, lpya lau princess, wannan saurin fa na meye, wlh prince na makara ne bnsan nayi latti shi yasa, toh muje na sauke ki sbda naga yadda kika makara din nan zaki iya tukin ganganci, nura ya fda yana mikewa, Sosai yake gudu da ita akan titi har suka karasa cikin gate din makarantar motar doctor salim na tsayawa ta su nura na tsayawa, Cikin hanzari nur ta bude murfin motar zata fita ya ruko hanunta, haba princess bbu ko sallama naga bai shiga ajin ba, prince ga motarsa nan fah ta fda tana ficewa, Mamaki dauke a fuskar doctor salim yake kallon nur da ta fito daga motar abokinsa, cikin girmamawa ta gaidashi, ya amsa har lokacin fuskarsa dauke da mamaki Kwankwasa masa windown da akayi ne ya sashi dago kanshi cikin mamaki ya fito daga motar salim, daman kana duniyar, dariya salim yayi toh ba gashiba ka ganni, ai anan nake aiki, salim ya fda, daman nur kanwar ka ce, dariya nura yayi a'a mata tace, sosai suka sha hira, yan ajin kuwa kowa sai yaba kyan nura suke suna dama ya sosu, sosai nur ta kulu ko me yasa ya fitoma, Fatima plsss zo muje mu gaida doctor salim ko Allah zaisa abokin nasa yace yana sanmu, amma Maryam kar ya dizga mu fah insha Allahu bazai disgamu ba suka fada suna ficewa Ran nur ba karamin baci yayi ba sanda su fatima suka fita Malam ina kwana, su fatima suka gaida doc salim cikin sakin fuska, lpya ya fada a takaice, Nura suka gaishar ya amsa musu cikin sakin fuska, ya karatu, Alhamdulilah, malam daman tambayarka zamuyi zamu karbo abu kar ka shiga ka hanamu shiga, toh kawai ya ce musu, Gefen su can kadan suka zauna suna jiran nura, Sai da suka kusa minti sha biyar sannan nura ya tafi saidashi sukai har lkcin idon nur na kansu, Ba yadda basuyi ba ya basu number amma yaki, ya ce musu yana da aure dole suka hakura suka kyaleshi ya tafi By Auntyn abul & Mmn abul [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 196-200 Suna shigowa aji ran nur ya kara baci, kusa da ita suka zauna, Mtswwwww aikin banza mutum duk inda kuka ga namiji sai kun ce kuna sanshi, wallahi kunyi asara, nur ta fda cikin bacin rai, Kiji mata ina ruwanki mu mukaga muna so, idan ma bakin ciki kike ya kashe ki kinga mutum ba irin mijinki ba, Banza nur ta musu tq cigaba da saurarar karatunsa, Karfe hudu dai dai suka gama lecture, su maryam na fitowa motar nura na tsayuwa, cikin sauri suka karaso wajansa a zatansu wajansu ya zo, Sannu da zuwa, suka fda a tare, yauwa ya fda fuska a hade, kunga dan Allah ku fita harkata kan na gwabza muku rashin mutunci, salon matata ta ganni da ku ku samin zargi, 😳 zaro ido sukayi mata kuma, eh ko ban isa nayi matar Bane, ka isa mana Allah ya baka hakuri suka fda suna barin wajen, kusa da shi suka zauna suna kallonsa, ganin ya fara murmushi yana kallon wani guri yasa su saurin kallon wajan Wayyo zo kuga yadda su fatima suka rude kaddai nur itace matar nura, indai kwa itace sun gama jin kunya, A hankli take tafiya fuskarta a tamke, tinda nura yaga ta hade rai ya sa shi jin gabansa na faduwa, baya san fushin nur dinsa ko kadan, Da sauri ya karaso inda take littatafan hanunta ya karba, princess ya karatun, naga kamar yau kunsha wuya sosai, hararar da ta watsa mashi ya sashi yin shiru, shi ya bude mata gaba ta shiga ya saka littafan a baya sannan ya shiga ya ja suka tafi Maryam da fatima sosai suka ji kunya, kuma tin daga ranar suka dau alkawarin dena kula duk wanda suka gani in ba shi ya kula su ba Da daddare nur tana zaune tana shan ice- cream nura ya shigo tare da sallama, ciki ciki ta amsa, kusa da ita ya zauna, " kanwata ki gayan laifin da nayi plsss kai ki azabtar da ni da share ni, bbu abinda ka min, ta fda a takaice, " wlh akwai amma ni bn san mene ba, " kaje ka tambayi yan matan naka mana Lumshe ido nura yayi sai a lokacin ya samu nutsuwa, Princess wlh ba yan matana bane nan ya kwashe komai ya gaya mata, turo baki tayi gaba, Toh kuma mene ko baki gamsu ba, na gamsu mana amma ni ka daina kaini makaranta daga yau ni zan na zuwa da kaina " yadda kika ce haka zaa yi ranki ya dade, yadda yayi ya burgeta sosai hakan yasata yin murmushi, nan suka cigaba da hirarsu har lkcn bacci yayi suka tafi suka kwanta, Kwanci tashi ba wuya wajan Allah su nur a na semester karshe sosai ta maida hankalinta ga karatun ta bata wasa, ko abinci bata ci sosai, ta maida hankalinta ga boko, nura kansa baya samun kyakyawar kulawa Kamar kullum nur na zaune a kan sallaya tana tq faman karatu nura ya turo kofar tare da sallama, ba tare da ta dago ba ta amsa sallamar, Yan boko karatun ne, eh yayana, gaskiya na kagu ki gama dan nasamu cikakiyar kulawa kamar da, kar ka damu prince ai na kusa gqmawa, sun dan taba hira kadan sannan ya fice dan ta samu damar karatun ta Kwanaki haka suka dinga shudewa, twince sun girma sosai dan sun fara makaranta ************************************** Aisha ba irin naci da batayiwa nura akan ya maida ta ba amma yaki, haka suka hakura ta fammalawa Allah komai sosai ta ke istigifari ta kuma koma makarantar islamiyyya, A haka har wani ya ganta shima ba wani babba bane amma yana da yara biyu matarsa ta mutu wajan haihuwa, Da kyar Aisha ta yarda ta aureshi, sosai take bawa yaran kulawa, kuma suma suka dauketa tamkar ita ta haifesu, nasir mijin Aisha na santa kuma yana bata kulawa soaai, da kyar ta yakashe son nura ta fara yiwa nasir shi *Allah sarki duniya makaranta Aisha dai anyi ilimi a gidan duniya* Kwanci tashi ba wuya wajan Allah su nur an kammala jarabawa kuma cikin ikon Allah tana daga cikin wanda suka fito da first klax an bata koyarwa anan jamiar bayero, murna wajan nur ba a cewa komai Ranar da ta karbo takaddunta da daddare nura na kallo ta shigo falon a kasa ta zauna kusa da kafafunsa " yayana na gode hakika bani da bakin godia a gareka dole na godewa Allah da ya hadani da kai badan taiman Allah sannan da taimakonka ba da banxo matsayin da nake ba, ta karashe maganar cikin kuka Dagota tayi ya rungumeta,kanwata karki min godia, ngde da like bani cikakiyar kulawa fatana a koda yaushe ki cigaba da sona har karshen rayuwar mu Insha Allahu yayana ni takace har karshen rayuwata Kisss ya manna mata sannan suka cigaba da kallonsu cikin so da kaunar junansu By auntyn abul & Mmn abul [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 201-205 " prince Dan Allah ka kaini gdan mumy gobe na yini, sbda nayi missing din mumy na, Nur ta fda tana shafa sumar kan nura da yake kwance a cinyarta A'A gobe fa lahadi kin San bbu fita ina gda na fiso na kasance dake, kina bani kyakyawar kulawa, Murmushi nur tayi, yadda kace haka zaa yi my prince, yauwa my princess shi yasa kullum nake kara sanki fiye da tinani na, dariya nur tayi nima haka my prince Zazzabi mai zafi nur ta tashi ga wani tashin zuciya da take fama dashi, da kyar tai sallar asuba ta kwanta ta janyo bargo tare da rufe jikinta Ganin nur bata fito ba gashi har tara tayi yasa nura shiga dakin, yadda ya ganta lulube cikin bargo ya sashi saurin karasowa inda take Princess me ya sameki ya fda yana zama kusa da ita, yaye bargon yayi ya dagota yadda ya ji jikinta yayi ya sa shi saurin kwantar da ita ya debo ruwa mai sanyi ya fara gasa mata jikinta bayan ya gama ya maida ya dawo ya shiga cikin bargon sannan ya rungumota ya rufesu, cikin minti goma bacci mai nauyi ya dauke su Basu suka farka ba sai kusa biyu da rabi, 😳zaro ido nura yayi sanda ya Dora idonsa kan agogo yaga biyu da rabi, cikin sauri ya nufi dakinsa yay alwala yay sallah, nur ma sallar tayi sannan ta fito falo, take aware yaje yayo musu, sannan ya dawo Princess taho muci abinci, toh my prince, amma kuma Allah yasa na iya ci sbda tashin zuciyar dana ke ji, " zaki iya insha Allahu princess ya fda yana juye abincin a plate, loma daya taji zuciyarta ta fara tashi ta nufi toilet da gudu Bayan ta gama aman nura yace su tafi asibiti da kyar nur ta yarda suka tafi asibitin, Gwajin farko aka tqbbatar musu da shigar ciki na wata biyu, wayyo zokuga murna wajan nura kamar wannan haihuwan nur na farko Kyauta ta musamman yay ma likitan sannan ya ruko hannun nur suka fito, duk inda suka gifta sai an kallesu, sosai suke burge mutanan da kansa ya bude mata mota ta shiga sannan yaja suka tafi " yayana daman gdan mum ka wuce da mu wlh, banza yay mata Kamar bai ji ba " yayana da kaifa nake kamin shiru, Kallonta yay tare da harararta, Dariya ma ya bata amma ta dake " toh kuma me nayi na harara, " au tambaya ma kike koh, ina tin jiya nace ba zancen zuwa gdan mumy koh kin manta ne" A'A yaya ban manta ba amma kuma ai kaga jiya bamuyi zaton da ciki a jiki na ba, amma yanxu akwai ciki a jikina kaga dole na tafi can nai goyan ciki na har na hai........ Yadda nura ya taka motar a titi tai kara ya sata yin shiru tana kallonsa cikin tsoro Cikin Bacin rai ya juyo ya kalleta, " gdan mumyn zaki goyan ciki, toh wlh ban yarda ba, wancan karanma dan ba yarda zanyi ne shi yasa, amma wannan karan baki isa ba, ai ba haihuwar farko bace Turo baki nur tqyi ta juya kanta tana kallon titi " au tsabagen rashin mutunci ina miki magana shine zaki dauke kanki, wato ga dan iska koh, shi kadai ya dinga sababin sa amma koh tanka mashi batayi ba, shirun da nur tayi mashi ba karamin bata mashi rai tayi ba, cikin bacin rai ya ja motar ya nufi gda, Tin da nura ya sauke nur ya fice bai dawo ba sai bayan sallar isha'i Tana zaune a falo tana kallon t v wanda hankalinta ba a kan kallon yake ba, da sallama ya shigo fuskar nan tashi a tamke, " au sbda sabar rashin mutunci yarinyar nan bata san ma ta min laifi ba shine take zaune harda dayin kallo nta, nura ya fda a zuciyarsa, Harara ya makamata yay hanyar dakinsa, yana shiga ya fda toilet, Nura na shiga daki, nur ta yanke shawar binsa dan bazata iya jure fushin mijinta ba akanta Yana daure da towel sai kuma karami da yake goge gashin kansa, ya fito Ganin wadda ke zaune a gefen gadon ya sashi kara bata rai ya nufi madubi tare da zama akan stl A hankali ta karaso inda yake, " prince kawo na gogema jikin naka, sosai nura yaji dadi a ransa, a fili kuma yace bashi zan iya, ba yadda batayi da shiba amma ya hanata dole ta tsaya tana kallonsa, a haka har ya gama komai ya mike da nufi zuwa yasa kaya " haba yayana, nayi ma laifi, kuma nazo baka hakuri shine zaka share ni, nur tq fda tana shan gabansa Banza yay mata yabi ta gefen tq zai wuce jikinsa ta fda tana kuka Ganin yaki magana yasata dago kanta, ta fara kai mashi duka a kirji cikin wasa " wlh sai ka yafen, ni ba da wasa nakema ba shine zaka fara fushi dani, yadda tai maganar ba karamin burgeta yayi ba Rike hanunta yayi, toh my princess ki yi hakuri ki daina duka na mana, so kike ki samin ciwon kirji, Toh bakai ka fara fushi dani ba, to ai na hakura, nura ya fda yana juyo da ita, a hankali ya fara shafa ta, itama tana fara maida masa martani, kafafunan su suka gagara daukarsu, hakan yasa suka fada kan gado, ni dai ganin bazan iya kallo ba yasa nace sister haima taho mu bar musu dakin, daga zuwa kallon sulhu By Shamsiyyah salis Nd Haima (mmn abul) [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 206-210 *bayan sati guda* "Nur wallahi idan baki sauri ba zan tafi na barki baki ganin yamma nayi, kuma kin addabeni muje zaki ga gari, "Yayana gani nan kayafa nake karasa sawa shiyasa, nur ta fda tana fitowa rike da jaka a hanunta Harara nura ya wulla mata, ba tare da yace mata komai ba ya nufi hanyar fita, itama bayansa ta bi suka fice, Wani katon shopn mall suka tsaya, a tare suka jero har suka shiga cikin wajen, siyayya sukayi sosai na kayan abinci da ciye ciye, sannan ta koma kan turaruruka da man shafawa kala kala, Bayan sun gama siyayya sun fito, har sun kusa mota nur taji ana kiran sunan ta, 😳 zaro ido nur tayi sanda ta juya ta ga mai kiranta " aunty Aisha kece, nur ta fda fuskarta dauke da murmushi, " nice nur daman kina nan, Aisha ta fda tana kallonta, "Wallahi aunty ina nan kin ganni, kwata kwata kin buya, ko a gr ba a jinki, ina su mumy, wlh kowa lpya, ina twince, Twince na wajan mumy, kinyi aure ne kohu dawo biko, nur ta fda tana kallon nura da ya jingina jikin mota bbu alamar faraa a fuskarsa Dariya Aisha tayi, a'a ni kan nayi aure, ai mijinki da ke kadai ya dace, kamar yadda nima na samu nawa mijin da yafi can canta ga rayuwata, " kai aunty na mijina fah gwarxon namiji ne, nima nawan haka gama shi nan ku gaisa, Aisha ta fda tana nuna mijinta, Cikin faraa ya karaso suka gaisa, nura ma zuwa yay suka gaisa, sannan kowa ya nufi motarsa bayan sunyi canjin number Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, cikin jin dadi, sosai nur take alfahari da mijinta, kwata kwata bayasan bacin ranta, a haka suke rainon cikin nur har Allah ya sa cikin ya shiga watan haihuwa Nur ce kwance kan doguwar kujera kanta na kan cinyar nura, "Princess nifa naga yau din nan kin tashi duk wani iri koh dai haihuwa ce, nura ya fda yana zura hanunsa cikin rigar nur yana shafa kirjinta, dan indai suna tare baya iya cikaken minti biyar ba tare da ya shafa kirjinta ba, "Haba prince dan Allah ka kyaleni da ciwona da ya tameni, sai faman shafa ni kake, nur ta fda tana cire hanun nura daga rigarta, "Allah ya huci zuciyarki bazan kara taba ki ba bare kimin gori, nura ya fda yana janye kan nur daga cinyarsa ya canza kujera Minti goma da faruwar hakan bbu wani kalma da ya kara shiga tsakanin su Ganin yadda mararta ta kulle yasata saurin sakkowa daga kujerar, juyi sosai nur takeyi a falo, amma nura yaki kulata Wayyo Allah na prince ka taimakamin kar na mut.......... Yadda mararta ya murda yasata kin karasa maganar, Cikin tashin hankali nura ya taso ya dauketa ya sata a mota sukai asibiti Cikin ikon Allah su nur na zuwa asibiti ta zankado kyakyawar yarta kyakyawa, Su mumy nura ya kirawo ya fda musu, kasancewar nur bata sha wuyaba yasa aka sallameta suka koma gda Tinda suka dawo gda gdan ya fara cika da jamaa, ba yadda nura yaso haka ya hakura ya fice sbda yawan jamaa kwanan nur biyu da haihuwa, kaka tazo, zo kuga murna wajan kaka kamar me Suna zaune a falo nur da kaka suna kallo, da daddare, sai kuma auta da tazo itama, nura ya turo kofar tare da yin sallama, suka amsa mashi, Kusa da kaka ya zauna yana rungumota jikinsa, kakata ya gajiya, ba gajiya, hpe dai kina kulamin da baby na, bn sani ba dan rainin wayyo tashi ka bn waje, Allah ya huci zuciyarki kaka, nur ya kalla, harara ta galla mashi sannan ta dauke kanta, murmushi kawai yqyi, nur dinshi akwai rigima jibi yadda take fushi dashi tin ranar da ta haihu, da a ce ba kowa gdan da tini ya shawo kan matarsa, ya fda a zuciyarsa, ganin bata da niyyar tanka mashi yayi dakinsa Yana kwance akan gado auta tayi sallama tare da turo kofar ya amsa mata fuska a sake, yaya ga abincinka inji mumy twince, tnxs idan kinje kice ina kiranta, ina yaran naki, suna gdan mumy ta fda tana ficewa Nur yaya na kiranki, toh kawai tace ta mike ta nufi dakinta tai kwanciyarta dan bata san musu kaka ta tilasta ta sai taje tana shiga daki ta kwanta bacci yay gaba da ita Nura kwa na can yana ta faman jira ganin bata da niyyar zuwa yasa shi fitowa ya nufi dakinta Daga taskar Shamsiyyah salis Nd Haima ( mmn abul) [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 171-175 Cikin tashin hankali nur ta fita batasan inda take sa kafarta ba da taimakon Allah ta karasa gda, Yanayin da su dady suka ganta ba karamin daga musu hankali yayi ba, cikin tashin hankali mumy ta rukota nur me ya faru, da kyar nur ta basu lbri tana kuka, Inalilahi waina ilaihir rajiun, abinda mumy da dady ke yi kenan a bakinsu har suka samu nutsuwa, tabbas ko shakka bbu akwai abinda ke damun dan su amma ba yadda za ai suce ga takamai man abinda ya sameshi, da kyar mumy ta rarashi nur tayi shiru Abu kamar wasa nura yau kwanan sa goma rabansa da gidan mumy, kuma ya kashe wayoyin sa gaba daya, Nur kuwa duk ta rame dan gaba daya ta fita hayyacinta, ko abinci bata ci sosai, " hajiya ki shirya ke da nur din muje gdan sa mu ga mu kuma da me zai kar be mu, ba musu suka shirya suka tafi, Da sallama suka shiga falon, nura da Aisha na zaune ana ta faman shan soyayya Mtswwwwww aikin banza kawai baza a taba barin mutum ya sake da iyalansa ba banda abin kunya ina na taba jin uban miji yazo gdan dansa Aisha ta fda cikin bacin rai, " yanxu nura kana kallon abinda matarka kema mahaifinka kayi mata shiru, mumy ta fda cikin tashin hankali, " toh mumy me Zan mata Ku fa kuka zo inda take ai gaskiya ta fda " na Shiga uku na haifi da wata ta dinga juya minshi wallahi Aisha baki isaba Allah ya fiki, mumy ta fda tana kuka Dady kan waje yayi dan tabbas yanxu ya tabbatar asiri ke dawainiya da dan nasa kuma insha Allahu zai yi iya kokarinsa dan nemawa dan nasa lpya wajan Allah " kinga malama ki fice min daga gida sai ki tafi can ki karata da kukan ki, kar ki dagan hankali, Aisha ta fda tana nuna mumy da yatsa, nur wadda tin da sukazo bata ce komai ba ta matso kusa da mumy tare da rike hanunta, dan su fita " banxaye kawai, kuma wallahi kuka kara shigo min gida sai kunyi da kun sanin zuwa gda na, ganin Aisha na zaginsu yasa nur juyowa cikin bacin rai " ke dan ubanki ki gyara zancenki mu din ba saaninki bane bnza jahila kawai ni tinda nake ma na taba ganin jahilin mutum kamar ke, nur ta fda rai a bace Cikin bacin rqi Aisha ta dago hannu zata mareta, nur ta rike hanun ta wanka mata kyawaean mari guda biyu, Ganin nur ta mari Aisha yasa nura ya maso kusa da ita yana huci kamar namijin zaki, ya daga hanun zai mareta ta kauce " zan maka uxiri daya ba a hayyacin ka kake ba amma wallahi da sai na gwabza muku rashin mutunci da ga kai har matar taka, nur ta fda cikin masifa, hanun mumy taja sukai waje Tin daga ranar gaba daya suka dukufa yiwa nura addua, sannan kusa sa ana mashi, sanda nur tai arba'in taje panisau tayi sati daya sannan ta dawo gda " sosai ta maida hankalinta ga karatunta dan sun koma twince kwa anyi wayau sosai, kamaninsu sak da mahaifin su, Tin da boka ya sadu da Aisha shaidan ya kwawata mata boka gani take duk duniya yafi kowa sarrafa mace, hakan yasa wata rana taje ta sameshi " hajiya kina da wata bukatarne dan nasan waccan bukatar ta biya, " eh boka bukatata ta biya amma ina so na zamar maka tamkar mata dan sosai naji dadin muamala da kai, " kar ki damu zan fi kowa san hakan dan ke din ta musammance nima kaina bntaba haduwa da wata mace da naji dadin harka da ita ba kamarke, tin daga ranar boka ya zama abokin alfashan Aisha Kwanci tashi ba wuya wajan Allah yau shekarar twince daya da haihuwa har lokacin nura bai waigesu ba, sosai sukai wayau ga baki suna tafiya ga kuma hakora, yaran abin shaawa duk wanda ya gansu sai sun bashi shaawa Da daddare suna falo suna hira dady ya kalli mumy yace " na karbo rubutun wajan malam na kadage a jaba yace indai na bashi rubutun ya sha sau uku da safe da rana da daddare ba zaiyi kwana ukuba asirin bai karye ba amma fa sai mun dage da addua a daran yau, Nur kema ki mashi, yaushe zaku gama exam din, saura kwana uku insha Allahu daddy Inyeee kice yar gatan mumy an kusa shiga level 3, insha Allahu dady, Allah yasa gaba daya suka amsa da amin sannan sukaje sukai nufin kwanciya dan karfe daya zasu tashi suyi sallah dan nemawa nura sauki wajan Allah Allah ka yaye mana duk wata damuwa dake damun mu, ina miko gaisuwa ga son dina sister haima a masa kisss hudu a kumatu By shamsiyya salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 176-180 Karfe daya dai dai gdan duk suka mike, dady ne yay musu limanci, su kansu basu san adadin sallar da sukai ba sosai sukai wa nura addua, tinda su dady suka fara addua nura ya mike kansa ya fara juya masa kamar zai cire yana son tina abu amma kwata kwata ya kasa tina komai Tin karfe bakwai Aysher ta tafi wajan mutuminta, nura yana zaune ya rasa me yake mashi dadi, tabbas akwai abinda yake son ya tina amma ya kasa, Daddy ne yay sallama tare da shigowa dakin, nura na ganinsa ya mike, dady sannu da zuwa zauna, ba musu ya zauna, nura ina matar taka, bnsan inda taje ba dady, amma na ganka shiru ko ba ka da lpya ne, wallahi dady tin jiya da daddare na rasa meke damuna Dan kwata kwata gani nake kamar akwai abinda ke damuna, kar ka damu nura, ga wannan kasha ba musu yasha sosai dady yaji dadi dan yasan tabbas adduarsu ta karbu, " nura so nake ka rakani office Dan ina da aiki da yawa, toh dady muje, damanna gaji da zaman waje daya, ya fda yqna mikewa, rqnar bashi ya koma gda ba sai kusan sallar isha'i dady ne ya sauke shi a gda, sannan ya koma, sanda ya koma har lokacin Aysher bata dawo ba Yau su nur a ka gama exam din second semestern su na level 2 sosai take jin ta cikin nishadi, ana fitowa daga exam ta kamo hanyar gda daman dady yasa driver ya koya mata mota yanxu da motar ta take fita, Nura na tashi daga bacci yqji Kansa na masa ciwo, twince dinsa ne suka fado masa Take ya tino maganarsu ta karshe da nur dinsa, a hankali ya tuno ranar da tazo ya wulakanta ta, da kuma ranar da su dady suka zo Aisha tawulakanta su sosai ran nura ya baci, wash zafafan hawayene suka zubo mashi na Bacin rai tabbas sai ya koyawa Aisha hankali, cikin bacin rai ya nufi dakin Aisha, " hello honey wallahi ina da bukatarka yau din nan kar kace min a'a, so nake ma ka kara mallake min nura dan kwanan na kasa gane gansa, Amma da farko aikin yayi kyau dan ko leke har yau bema iyayensa ba bare kuma tsinanun yayqnsa da bakauyiyar matarsa Mutuwar tsaye nura yayi ya fara karanto addu'oi a hankali, har ya samu nutsuwa cikin tashin hankali nura ya shigo falon ganinsa yasa ta bata rai ko kallonta bai yi na ya dau key dinsa yay waje, tana kiransa amma ko kallonta baiyi ba Cikin tashin hankali ya tura kofar dakin, dady da mumy na zaune sai twince da suke wasa a falo, Cikin farin ciki mumy da dady suka mike, nura, suka fda a tare, A hankali nura ya sulale a kasa, dan Allah ku ya femun wallahi sharrin Aisha ne yanxu ma naji tana waya da bokanta abokin fasikancinta, nan nura ya kwashe komai ya fda musu, sosai sukai mamakin halin Aisha sannan suka ce sun yafe mashi da da mahaifi sai Allah nan da nan suka fara tarairayarsa, Mumy ina twince dina, gasu can mumy ta fda tana nuna masa su 😳 zaro ido yayi yana mamakin girmansu Dakkosu yayi yna musu wasa nan da nan ya shiga ransu, Suna hira su dukansu nur ta turo kofar ta shigo tare da sallama, Mumy ta amsa mata, yar gatan mmumy kin dawo eh mumyna ta fda tana zama kusa da mumy sai a lokacin nur ta kula da nura da ya kafe ta da ido kallo daya ta mashi ta dauke idonta, ba laifi ya rame yayi baki ga uwar suma da ya tara da yawa kuma ga dukkan alamu bata samun kulawa kamar da " mumy bari na shigq na dan watsa ruwa dan na gaji sosai, Toh yar gatan mumy ajiyar zuciya nura ya sauke sanda nur ta bace da ganinsa, Mumy nur kan ta kara kyau sosai dariya mumy tayi kawai By Shamsiyyah salis & Haima (mmn abul) [4/30, 5:36 PM] Shsy Sls Excl: 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧 🌧 HADIN ALLAH 🌧 🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧 🌧🌧🌧🌧🌧🌧🌧 Written by Shamsiya Salis & Haima(mmn Abul) Dedicated To Shamsiya Salis(Auntyn Abul) Halimahaimausman.wordpress.com 211_215 *last page* *wannan fajin naki ne aunty na Ayusha Iliasu musa bn manta ki ba a ko wane lkci kina raina, fatana a koda yaushe Allah sa ki gama makaranta lpya ki kuma fito mana da sakamako mai kyau ur shamsiyya still luv yuh😘😘😘* Ba karamin mamaki yay ba sanda ya ganta a kwance a tsakiyar gado sai faman suburbudar baccin ta take hankali kwance, cikin bacin rai na nufi wajan auta, " dan wulakanci auta da nace ki cema nur tazo shine kika ki gayamata, nur ya fda sanda ya isa wajan su kaka Cikin tashin hanki auta ta fara magana " wallahi yaya na fda mata ina dawowa kuma ga kaka nan ka tambayetq bai ko kara kallonsu ba ya nufi dakinsa cikin bacin rai, ranar bacci barawone ya sace shi Tin daga ranar nura in ya fita tin safe baya dawowa sai dare, sosai nur ta shiga tashin hankali ganin yadda ya canza, Ranar suna yarinya taci sunnan mahaifiyar nur khadija ana ce mata islam, anci an sha kamar me yan panisau ma an mata kara anzazzo daman mutan panisau ba da ga nan akwai kara Kwana 2 da suna gida ya watse bbu kowa daga me jego yarta, da daddare tana kwance a falo bayan ta kwantar da Islam a daki, Nura ya turo kofar tare dayin salama, fuskarta dauke da faraa ta taso tare da karbar brief case dinsa bayan ta amsa mashi sallama Yayana sannu da zuwa, "Yauwa " nura ya fda a takaice, hanyar dakinsa ya nufa, jiki ba kwari tabi bayansa, bayan ya fito daga kwanka ya shirya cikin wata farar jalabiyya sannan ya hau gado yay kwanciyarsa tare da lumshe idonsa A hankali nur ta matsa kusa dashi tare da hayewa kan gadon, kusa dashi ta kwanta tare da dora kanta a kirjinsa, ajiyar zuciya nura ya sauke sosai yaji dadi, domin yayi missing dinta alot, A hankali ta zura hanunta cikin jalabiyarsa tana shafa jikinsa, hanunta ya rike, tare da bude idonsa Wanda har sun fara canza kala, plssssss bnso ki kyale ni bacci nakeji, ni kuma inaso bazan iya jure fishinka ba yayana nasan ni namaka laifi, amma nazo Neman yafiya sai faman shareni kakeyi, Nur ta fda kamar zatayi kuka, ba irin magiyar da batai mashi ba amma yay mata banza, ganin bashi da niyyar kulata yasa dole ta daga shi ta zura kafarta kasa zata sauka, hanunta ya ruko cikin kulawa, na hakura kanwata amma Dan Allah ki fdan me yasa kika tsaneni, Yayana ban tsaneka ba ina sanka, kuma insha Allahu daga yau bazan kara bata maka ba, promise nura ya fda cikin jin dadi, daga mashi kai tayi alamar eh, janyota yayi ta fdo jikinsa nan suka fara sunbatar juna, ni dai ja da baya nayi, nace a dai kula kar a wuce gona da iri sbda madam tana jinin haihuwa😜 *bayan shekara biyu* Soyayya ake mai tsafta tsakanin nur da nura kwata kwata basa so Suyi nisa da juna, ko asibiti wajan aiki nur ta tafi suna makale da juna a waya, sosai yqn biyu sukai wayau kamar yadda kanwarsu ma tayi wayau Nur da nura an zama iyaye, basa cikaken wata guda basu je panisau ba, Yau ta kama lahadi nur da nura da kuma yayansu da mumy ta kawosu suyi week end na zaune a falo suna hira, nura ya kalli nur yace princess kullum kara godewa Allah nake da Allah ya mallakamin ke a matsayin mata ta, dariya nur tayi nima haka my prince gani nake duk duniya ba wanda ya kaini saar miji a duniya, Yauwa princess na mnta bn fda miki ba aure zan kara, toh yayana Allah yasa ka samo wadda zamu hada kanmu mu zauna lpya ba tare da mun daga mashi hankali ba,😳 zaro ido nura yayi yanaga baki tsorataba, Sbda me zan tsorata dan zaka kara aure ba a auren ka auroni, ta fda tana daga mashi gira, dukan wasa ya kaimata, Allah ya shirya ki princess sbda kinsan bazan iya kara aureba shine harda saurin yadda koh, dariya nur tqyi toh kma kara kaga inzandqmu, dariya gaba daya sukai sannan yq rungumota yq mannq mata kiss ita ta mashi suka kara rungume juna su da yaransu cikin so da kaunar junansu Alhamdulilah anan muka kawo karshen wannan littafi namu mai suna asama. Jinjinar ban girma Gareki yar uwata kuma abokiyar aikina hakika bani da bakin godiya domin kin kasance abar alfaharina, fatana Allah ya karawa rayuwarki albarka yasa ki gama da duniya lfy,ya albarkaci zuri'arki yabaki miji na gari. Auntyn Abul SHAMSIYYA SALIS BAN MANTA DAKU BA masoya aduk inda kuke da duk mai kaunar wannan littafin mai suna HADIN ALLAH. KUNA RAINA HAIMA NOVELS WORLD OF HAUSA NOVELS CANDY NOVELS KASAITATTUN MATA PHARTY BB NOVELS KAMOSA SPECIAL GALS O11 NOVALL LODGE JINIE DAYA NOVELS MUSAN JUNA OHW DA SAURAN MASOYANMU SAI MUN HADU ASABON NOVEL DINMU MAI SUNA BURIN IYAYE YANA NAN TAFE. ABULKHAIR Allah ya rayamun kai ya albarkaci rayuwarka ya baka ilimi mai amfani yas kaxama mahaddacin qur'ani tare da saurn yayan musulmi baki daya Daga taskar Shamsiya slis And Haima(mmn Abul)

Share this


Author: verified_user

0 Comments: